< 2 Bitrus 1 >
1 Siman Bitrus, bawa da kuma manzon Yesu Kiristi, Zuwa ga waɗanda ta wurin adalcin Allahnmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi sun sami bangaskiya mai daraja irin tamu.
Simon Petrus, Jesu Christi tjenare och Apostel; dem som med oss lika dyrbara tro fått hafva i rättfärdighetena, som vår Gud gifver, och Frälsaren Jesus Christus.
2 Alheri da salama su zama naku a yalwace ta wurin sanin Allah da Yesu Ubangijinmu.
Nåd och frid föröke sig i eder, genom Guds och vårs Herras Jesu Christi kunskap.
3 Ikonsa na Allahntaka ya ba mu kome da muke bukata don rayuwa da kuma tsoron Allah ta wurin sanin wanda ya kira mu ta wurin ɗaukakarsa da nagartarsa.
Efter det allahanda af hans Gudoms kraft, hvad som till lif och Gudaktighet tjenar, oss skänkt är, genom hans kunskap, som oss hafver kallat genom ( sina ) härlighet och dygd;
4 Ta wurin waɗannan ya ba mu alkawaransa masu girma da kuma masu daraja, domin ta wurinsu ku iya yin tarayya cikin Allahntakarsa, ku kuma kuɓuta daga lalatar da take cikin duniya wadda mugayen sha’awace-sha’awace suke jawowa.
Genom hvilka oss de dyra och aldrastörsta löfte gifna äro; nämliga, att I derigenom mågen blifva delaktige af Guds natur, om I flyn verldenes förgängeliga lusta;
5 Saboda haka, ku yi iyakar ƙoƙari ku ƙara wa bangaskiyarku nagarta; ga nagarta kuwa, ku ƙara mata sani;
Så lägger eder nu derom alla vinning, att I uti edra tro låten finnas dygd, och i dygdene beskedelighet;
6 ga sani kuma ku ƙara masa kamunkai; ga kamunkai kuma ku ƙara da daurewa; ga daurewa kuwa ku ƙara da tsoron Allah;
I beskedelighetene måttelighet, i måttelighetene tålamod, i tålamodet Gudaktighet;
7 ga tsoron Allah kuma ku ƙara da nuna alheri ga’yan’uwa; ga nuna alheri ga’yan’uwa kuma ku ƙara da ƙauna.
I Gudaktighetene broderlig kärlek, i broderlig kärlek allmännelig kärlek.
8 Domin in kuna ƙaruwa a waɗannan halaye, za su kāre ku daga rashin tasiri da rayuwa na rashin amfani cikin saninku na Ubangijinmu Yesu Kiristi.
Ty när dessa stycker äro rikeliga när eder, så låta de eder icke finnas fåfänga eller utan frukt, i vårs Herras Jesu Christi kunskap.
9 Amma in wani ba shi da su, ba shi da hangen nesa ke nan kuma makaho ne, ya kuma manta cewa an tsarkake shi daga zunubansa na dā.
Men hvilken denna icke hafver, han är blind, och ser intet, och hafver förgätit, att han var ren gjord af de synder, som han förra hade.
10 Saboda haka’yan’uwana, ku ƙara aniya wajen tabbatar da kiranku da zaɓenku da aka yi. Gama in kuka yi waɗannan abubuwa, ba za ku taɓa fāɗuwa ba,
Derföre, käre bröder, lägger eder heldre vinning om att I gören edor kallelse och utkorelse fast; ty om I det gören, så fallen I icke någon tid.
11 za ku sami kyakkyawar marabta cikin madawwamin mulkin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. (aiōnios )
Ty i så måtto blifver eder rikeliga gifven ingången i vårs Herras och Frälsares Jesu Christi eviga rike. (aiōnios )
12 Saboda haka kullum zan tuna muku da waɗannan, ko da yake kun sansu kun kuma kahu ƙwarai cikin gaskiyar da kuke da ita yanzu.
Derföre vill jag icke hafva fördrag att förmana eder alltid härom, ändock I det veten, och ären stadfäste i denna närvarande sanning.
13 A ganina ya dace in tunashe ku muddin ina raye cikin tentin wannan jiki,
Ty jag menar det vara tillbörligit, så länge jag är i denna hyddo, att uppväcka och förmana eder.
14 domin na sani na kusa in ajiye shi a gefe, yadda Ubangijinmu Yesu Kiristi ya nuna mini a sarari.
Ty jag vet att jag skall snarliga aflägga denna mina hyddo, såsom ock vår Herre Jesus Christus hafver mig kungjort.
15 Zan kuwa yi iyakacin ƙoƙari in ga cewa bayan rabuwata kullum za ku iya tuna da waɗannan abubuwa.
Men jag vill vinnlägga mig att I, efter min död, skolen behålla detta i åminnelse.
16 Ba mu bi tatsuniyoyin da aka ƙaga da wayo sa’ad da muka gaya muku game da ikon Ubangijinmu Yesu Kiristi da zuwansa ba, sai dai mu shaidu ne na ɗaukakarsa mai girma da muka gani da ido.
Ty vi hafve icke efterföljt några kloka fabler, då vi kungjordom eder vårs Herras Jesu Christi kraft och tillkommelse; utan vi hafve sjelfve sett hans härlighet.
17 Gama ya sami girma da ɗaukaka daga Allah Uba sa’ad da murya ta zo masa daga Mafificiyar Ɗaukaka cewa, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; da shi nake jin daɗi ƙwarai.”
Då han fick af Gud Fader äro och pris, genom ena röst, som till honom skedde af den stora härligheten, så lydandes: Denne är min älskelige Son, i hvilkom jag hafver ett godt behag.
18 Mu kanmu mun ji wannan muryar da ta zo daga sama sa’ad da muke tare da shi a kan dutse mai tsarki.
Och denna röst hörde vi komma af himmelen, då vi vorom med honom på det helga berget.
19 Muna kuwa da maganar annabawa da aka ƙara tabbatar mana, zai fi kyau in kuka lura da ita, kamar hasken da yake haskakawa a wuri mai duhu, har yă zuwa wayewar gari da kuma haskakawar tauraron asubahi a zukatanku.
Vi hafvom ett fast prophetiskt ord; och I gören väl att I akten derpå, lika som på ett ljus, som skin uti ett mörkt rum, så länge det dagas, och morgonstjernan uppgår i edor hjerta.
20 Gaba da kome dai, dole ku gane cewa babu annabcin Nassin da ya fito daga fassarar annabi da kansa.
Och det skolen I först veta, att ingen Prophetia i Skriftene sker af egen utläggning.
21 Gama annabci bai taɓa samo tushensa daga nufin mutum ba, sai dai mutane sun yi magana daga Allah yayinda Ruhu Mai Tsarki ya bishe su.
Ty ingen Prophetia är ännu framkommen af menniskovilja; utan de helga Guds menniskor hafva talat, rörde af dem Helga Anda.