< 2 Korintiyawa 3 >

1 Yabon kanmu ne kuma muka fara yi? Ko kuwa muna bukatar wasiƙun yabo ne zuwa gare ku, ko daga gare ku, kamar yadda waɗansu suke yi?
(Are we beginning to commend ourselves again? Do we need, as some do, letters of recommendation to you, or commendation from you?
2 Ai, ku kanku ku ne wasiƙarmu, wadda aka rubuta a zukatanku, domin kowa yă santa, yă kuma karanta ta.
You are our letter, inscribed on our hearts, known and read by all men;
3 Kun nuna cewa ku wasiƙa ce daga Kiristi, sakamakon hidimarmu, ba wadda aka rubuta da inki ba, sai dai da Ruhun Allah mai rai. Ba kuma a kan allunan dutse ba, sai dai a kan allunan zukatan mutane.
you are manifestly a letter of Christ, mediated by us, written not with ink but by the Spirit of the living God, not on stone tablets but on ‘tablets’ that are hearts of flesh.)
4 Amincewa kamar wannan shi ne namu ta wurin Kiristi a gaban Allah.
Now we have such confidence before God because of the Christ;
5 Ba mu da wani abin da za mu nuna cewa da iyawarmu ne muke aikin nan. Iyawarmu daga wurin Allah ne.
not that we are competent of ourselves to reckon anything as being from ourselves, but our competence is from God—
6 Shi ya sa muka gwaninta a matsayinmu na masu hidimar sabon alkawari ba ta rubutacciyar Dokar ba, amma ta Ruhu; don Dokar, kisa take yi, Ruhu kuwa yana ba da rai.
indeed, He has made us competent as ministers of a new covenant; not of letter but of Spirit, because the letter kills, while the Spirit gives life.
7 To, in hidimar da ta kawo mutuwa, wadda an rubuta a kan allon dutse, ta zo da ɗaukaka har Isra’ilawa suka kāsa duban fuskar Musa saboda tsananin haskenta, ko da yake mai shuɗewa ce,
Now if the ministry of death, engraved in letters on stones, came with glory—so that the children of Israel could not gaze at the face of Moses because of the glory of his countenance (that was fading)—
8 ashe, hidimar Ruhu ba za tă fi wannan ɗaukaka ba?
how can the ministry of the Spirit not be more glorious?
9 In hidimar da take jawo wa mutane hukunci tana da ɗaukaka haka, to, lalle, hidimar da take kawo adalci za tă fi ta ɗaukaka nesa!
For if the ministry of condemnation had glory, how much more glorious is the ministry of righteousness!
10 Gama abin da dā take da ɗaukaka, ba ta da ɗaukaka a yanzu, in aka kwatantata da mafificiyar ɗaukaka ta yanzu.
Because what had glory could actually be said to be without glory, compared to the surpassing glory—
11 In kuma aba mai shuɗewa ta zo da ɗaukaka, ashe, abin da yake dawwammame, lalle ne yă kasance da ɗaukakar da ta fi haka nesa!
if what is being set aside had glory, that which is continuing is much more glorious.
12 Da yake muna da bege irin wannan, to, muna da ƙarfin zuciya sosai ke nan.
Therefore, since we have such a hope, we use great boldness of speech—
13 Mu ba kamar Musa ba ne, wanda ya rufe fuskarsa da lulluɓi, don kada Isra’ilawa su ga ƙarewar ɗaukakan nan mai shuɗewa.
not like Moses, who put a veil over his own face, so that the children of Israel would not observe the end of what was fading.
14 Amma aka sa hankulansu suka dushe, gama har yă zuwa yau akwai lulluɓin nan a duk sa’ad da ake karatun tsohon alkawari. Ba a kawar da shi ba, sai a cikin Kiristi ne kaɗai ake kawar da shi.
But, it was their minds that were closed, because to this day that very veil remains in place when the Old Testament is read, since only in Christ is it taken away.
15 Har yă zuwa yau, duk sa’ad da ake karatun littattafan Musa, lulluɓin nan yakan rufe zukatansu.
Yes, even to this day, when Moses is read a veil lies on their heart.
16 Amma duk sa’ad da wani ya juyo ga Ubangiji, akan kawar da lulluɓin.
However, whenever anyone turns to the Lord the veil is removed.
17 Ubangiji fa, shi ne Ruhu, kuma duk inda Ruhun Ubangiji yake, a nan’yanci yake.
Now the Spirit is the Lord, and where the Lord's Spirit is there is freedom.
18 Mu da ba mu da lulluɓi a fuskokinmu duk muna nuna ɗaukakar Ubangiji, ana sauya mu mu ɗauki kamanninsa cikin ɗaukaka mai hauhawa. Ubangiji wanda yake ruhu kuwa shi ne mai zartar da haka.
So we all, contemplating as in a mirror the glory of the Lord with unveiled face, are being transformed into the same image from glory to glory, precisely from Lord Spirit.

< 2 Korintiyawa 3 >