< 2 Korintiyawa 11 >
1 Ina fata za ku yi haƙuri da’yar wautata. Amma, ai, kun riga kun yi haƙuri.
I would that ye could bear with me a little, that I might talk foolishly: and indeed, bear ye with me.
2 Ina kishinku da kishi irin na Allah. Na yi muku alkawarin aure ga miji ɗaya, Kiristi, domin in miƙa ku a gare shi kamar budurwa zalla.
For I am jealous over you, with a godly jealousy: for I have espoused you to a husband as a chaste virgin, whom I would present to the Messiah.
3 Sai dai ina tsoro kada yă zama, kamar yadda maciji ya yaudari Hawwa’u da makircinsa, ku ma a bauɗar da hankalinku daga sahihiyar biyayya amintacciya ga Kiristi.
But I fear, lest, as the serpent beguiled Eve by his craftiness, so your minds should be corrupted from simplicity towards the Messiah.
4 Gama in wani ya zo wurinku yana wa’azin wani Yesu dabam da wanda muka yi wa’azinsa, ko kuma in kun karɓi wani ruhu dabam da wanda kuka karɓa, ko wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, ya nuna kun yarda da su ke nan cikin sauƙinkai.
For if he that cometh to you, had proclaimed to you another Jesus, whom we have not proclaimed; or if ye had received another Spirit, which ye have not received; or another gospel, which ye have not accepted; ye might well have given assent.
5 Amma a ganina waɗancan da kuke ce da su “manyan manzanni” ba su fi ni da wani abu ba.
For, I suppose, I came not short of those legates who most excel.
6 Mai yiwuwa ni ba horarre ba ne a magana, amma ina da sani. Mun kuwa bayyana muku wannan a sarari, ta kowace hanya.
For, though I be rude in speech, yet not in knowledge; but in all things we have been manifest among you.
7 Laifi ke nan ne na yi da na ƙasƙantar da kaina, don a ɗaga ku zuwa babban matsayi ta wurin yin muku wa’azin bisharar Allah kyauta?
Did I indeed commit an offence, by humbling myself that ye might be exalted? and by proclaiming the gospel of God to you gratis?
8 Na yi wa waɗansu ikkilisiyoyi ƙwace ta wurin karɓar taimako daga wurinsu, domin in yi muku hidima.
And I robbed other churches, and I took pay of them for ministering to you.
9 Sa’ad da nake tare da ku kuma nake zaman rashi, ban nawaita wa kowa ba, gama’yan’uwan da suka zo daga Makidoniya sun biya bukata. Na kiyaye kaina daga nawaita muku ta kowace hanya, zan kuma ci gaba da yin haka.
And when I came among you and was needy, I was burdensome to none of you; for the brethren who came from Macedonia, supplied my wants: and in all things I kept myself, and I will keep myself, from being burdensome to you.
10 Ba shakka, kamar yadda gaskiyar Kiristi take a cikina, babu wani a yankunan Akayya da zai iya hana yin taƙaman nan tawa.
As the truth of the Messiah is in me, this glorying shall not be made vain as to me in the regions of Achaia.
11 Don me? Don ba na ƙaunar ku ne? Allah dai ya sani ina ƙaunarku!
Why? Because I do not love you? God knoweth.
12 Zan kuma ci gaba da yin abin da nake yi, domin in toshe kafar mutanen nan da suke fariya, suna nema mu daidaita da su.
But what I do, that also I will do; that I may cut off occasion, from them who seek occasion: so that in the thing wherein they glory, they may be found even as we.
13 Gama irin waɗannan mutane manzannin ƙarya ne, ma’aikata ne masu ruɗi, sun ɓad da kamanni kamar su manzannin Kiristi ne.
For they are false legates, crafty workers, and feign themselves to be legates of the Messiah.
14 Ba abin mamaki ba ne, gama Shaiɗan kansa ma yana ɓad da kamanni kamar shi mala’ikan haske ne.
And in this there is nothing strange. For if Satan feigneth himself an angel of light,
15 Don haka, ba abin mamaki ba ne, in bayin Shaiɗan sun ɓad da kamanni kamar su bayin adalci ne. A ƙarshe, za a sāka musu gwargwadon ayyukansu.
it is no great thing if his ministers feign themselves ministers of righteousness; whose end shall be according to their works.
16 Ina sāke faɗa, kada wani yă ɗauka ni wawa ne. Amma in kun ɗauke ni haka, to, sai ku karɓe ni kamar yadda kuke karɓan wawa, domin in ɗan in yi taƙama.
Again I say, let no one think of me, as being a fool: or if otherwise, receive me as a fool, that I may glory a little.
17 A wannan taƙamata ba na magana yadda Ubangiji zai yi ba ne, sai dai magana ce irin ta wawa.
What I am now saying, I say not in our Lord, but as in folly, in this matter of glorying.
18 Da yake mutane da yawa suna taƙama irin ta duniya, ni ma haka zan yi.
Because many glory after the flesh, I also will glory.
19 Ku kam kuna da wayo sosai, har kuna jimre wa wawaye da murna!
For ye hear with indulgence them who lack reason, seeing ye are wise.
20 Gaskiyar ita ce, kuna haƙuri da duk wanda ya sa ku bauta ko ya cuce ku ko ya more ku ko ya nuna muku isa ko kuma ya mare ku a fuska.
And ye give ear to him, who putteth you in bondage; and to him, who devoureth you; and to him, who taketh from you; and to him, who exalteth himself over you; and to him, who smiteth you in the face.
21 Ina jin kunya in ce mun nuna kāsawa da ba mu yi waɗannan abubuwan ba! Abin da wani yake da ƙarfin hali yin taƙama a kai, shi ne ni ma nake ƙarfin hali yin taƙama a kai. Ina magana kamar wawa ne.
I speak as if under contempt: I speak as if we were impotent, through deficiency of understanding; that in whatever thing any one is presuming, I also am presuming.
22 In su Ibraniyawa ne, ni ma haka. In su Isra’ilawa ne, ni ma haka. In su zuriyar Ibrahim ne, ni ma haka.
If they are Hebrews, so I also: or if they are Israelites, I also. If they are the seed of Abraham, I also.
23 In su bayin Kiristi ne, ni na fi su ma, ina magana kamar ruɗaɗɗe ne fa! Ai, na fi su shan fama ƙwarai da gaske, da shan dauri, na sha dūka marar iyaka, na sha hatsarin mutuwa iri-iri.
If they are ministers of the Messiah, (in defect of understanding, I say it, ) I am superior to them: in toils more than they, in stripes more than they, in bonds more than they, in deaths many times.
24 Sau biyar Yahudawa suka yi mini bulala arba’in ɗaya babu.
By the Jews, five times was I scourged, each time with forty stripes save one.
25 Sau uku aka bulale ni da bulalar ƙarfe, sau ɗaya aka jajjefe ni da duwatsu, sau uku jirgin ruwa ya ragargaje ina ciki, na kwana na kuma yini ruwan teku yana tafiya da ni.
Three times was I beaten with rods: at one time I was stoned: three times I was in shipwreck, by day and by night; I have been in the sea, without a ship.
26 Na yi tafiye-tafiye da yawa, na sha hatsari a koguna, na sha hatsarin’yan fashi, na sha hatsari a hannun kabilarmu, na sha hatsari a hannun al’ummai, na sha hatsari a birane, na sha hatsari a jeji, na sha hatsari a teku, na kuma sha hatsarin’yan’uwa na ƙarya.
In journeyings many, in peril by rivers, in peril by robbers, in peril from my kindred, in peril from Gentiles: I have been in peril in cities; I have been in peril in the desert, in peril in the sea, in peril from false brethren.
27 Na yi fama, na shan wuya, ga kuma rashin barci sau da yawa. Na san abin da ake nufin da jin yunwa da ƙishirwa, sau da yawa kuwa na kasance da rashin abinci, na sha sanyi da zaman tsirara.
In toil and weariness, in much watching, in hunger and thirst, in much fasting, in cold and nakedness:
28 Ban da waɗannan abubuwa, kowace rana ina ɗauke da nauyin kula da dukan ikkilisiyoyi.
besides many other things, and the thronging around me every day, and my anxiety for all the churches.
29 Wane ne ya rasa ƙarfi, da ban ji shi a jikina ba? Wane ne ya fāɗi cikin zunubi, da ban ji zafin wannan ba?
Who becometh weak, and I become not weak? Who is stumbled, and I burn not?
30 In ma lalle ne in yi taƙama, to, sai in yi taƙama da abubuwan da suka nuna rashin ƙarfina.
If I must glory, I will glory in my infirmities.
31 Allah Uban Ubangiji Yesu Kiristi, wanda yabo ta tabbata a gare shi har abada, ya san cewa ba ƙarya nake yi ba. (aiōn )
God, the Father of our Lord Jesus the Messiah, blessed for ever and ever, he knoweth that I lie not. (aiōn )
32 A Damaskus, gwamnan da yake ƙarƙashin Sarki Aretas, ya sa tsare ƙofofin birnin Damaskus, don yă kama ni.
At Damascus, the commander of the army of Aretas the king, guarded the city of the Damascenes, to seize me.
33 Amma aka saukar da ni cikin kwando ta tagar katanga, na kuɓuce masa.
And from a window, in a basket, they let me down from the wall, and I escaped from his hands.