< 2 Tarihi 36 >

1 Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a Urushalima yă gāji mahaifinsa.
Alors le peuple du pays prit Jéhoachaz fils de Josias, et on l'établit Roi à Jérusalem en la place de son père.
2 Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku.
Jéhoachaz était âgé de vingt et trois ans quand il commença à régner, et il régna trois mois à Jérusalem.
3 Sarkin Masar ya tumɓuke shi a Urushalima, ya tilasta Yahuda su biya haraji talenti ɗari na azurfa da kuma talentin zinariya.
Et le Roi d'Egypte le déposa à Jérusalem, et condamna le pays à une amende de cent talents d'argent, et d'un talent d'or.
4 Sarkin Masar ya naɗa Eliyakim, ɗan’uwan Yehoyahaz, sarki a bisa Yahuda da kuma Urushalima, ya kuma canja sunan Eliyakim zuwa Yehohiyakim. Amma Neko ya ɗauki Yehoyahaz ɗan’uwan Eliyakim ya kai Masar.
Et le Roi d'Egypte établit pour Roi sur Juda et sur Jérusalem Eliakim frère de [Joachaz], et lui changea son nom, [l'appelant] Jéhojakim; puis Nécò prit Jéhoachaz, frère de Jéhojakim, et l'emmena en Egypte.
5 Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa.
Jéhojakim était âgé de vingt-cinq ans quand il commença à régner, et il régna onze ans à Jérusalem, et fit ce qui déplaît à l'Eternel son Dieu.
6 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya hauro ya kara da shi. Ya kama shi, ya daure da sarƙoƙin tagulla, ya kuma kai shi Babilon.
Nébucadnetsar Roi de Babylone monta contre lui, et le lia de doubles chaînes d'airain pour le mener à Babylone.
7 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kuma kwaso kayayyaki daga haikalin Ubangiji ya sa su a haikalinsa a can.
Nébucadnetsar emporta aussi à Babylone des vaisseaux de la maison de l'Eternel, et les mit dans son Temple à Babylone.
8 Sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim, ayyukan banƙyamar da ya aikata da dukan abubuwan da aka same shi da su, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda. Sai Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Or le reste des faits de Jéhojakim, et ses abominations, lesquelles il fit, et ce qui fut trouvé en lui, voilà ces choses sont écrites au Livre des Rois d'Israël et de Juda, et Jéhojachin son fils régna en sa place.
9 Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku da kwana goma. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji.
Jéhojachin était âgé de huit ans quand il commença à régner, et il régna trois mois et dix jours à Jérusalem, et il fit ce qui déplaît à l'Eternel.
10 Da bazara, Sarki Nebukadnezzar ya aika a kawo Yehohiyacin, aka kuma kawo shi Babilon, tare da kayayyaki masu daraja daga haikalin Ubangiji, sai Sarki Nebukadnezzar ya naɗa kawunsa Zedekiya, sarki a bisa Yahuda da Urushalima.
Et l'année suivante le Roi Nébucadnetsar envoya, et le fit emmener à Babylone avec les vaisseaux précieux de la maison de l'Eternel, et établit pour Roi sur Juda et sur Jérusalem Sédécias son frère.
11 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya.
Sédécias était âgé de vingt et un ans quand il commença à régner, et il régna onze ans à Jérusalem.
12 Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa kuma bai ƙasƙantar da kansa a gaban Irmiya annabi, wanda ya yi magana kalmar Ubangiji ba.
Il fit ce qui déplaît à l'Eternel son Dieu, et ne s'humilia point pour [tout ce que lui disait] Jérémie le Prophète, qui lui parlait de la part de l'Eternel.
13 Ya tayar wa Sarki Nebukadnezzar, wanda ya sa ya yi rantsuwa da sunan Allah. Ya zama mai kunnen ƙashi da kuma taurin zuciya, bai kuwa juye ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ba.
Et même il se rebella contre le Roi Nébucadnetsar, qui l'avait fait jurer par [le Nom de] Dieu; et il roidit son cou, et obstina son cœur pour ne retourner point à l'Eternel le Dieu d'Israël.
14 Bugu da ƙari, dukan shugabannin firistoci da mutane suka ƙara zama marasa aminci, suna bin dukan abubuwan banƙyama na al’ummai, suka ƙazantar da haikalin Ubangiji, wanda ya tsarkake a Urushalima.
Pareillement tous les principaux des Sacrificateurs, et le peuple, continuèrent de plus en plus à pécher grièvement, selon toutes les abominations des nations; et souillèrent la maison que l'Eternel avait sanctifiée dans Jérusalem.
15 Sai Ubangiji Allah na kakanninsu, ya yi ta aika da magana gare su ta wurin’yan saƙonsa sau da sau, domin ya ji tausayi mutanensa da mazauninsa.
Or l'Eternel le Dieu de leurs pères les avait sommés par ses messagers, qu'il avait envoyés en toute diligence, parce qu'il était touché de compassion envers son peuple, et envers sa demeure.
16 Amma suka yi wa’yan saƙon Allah ba’a, suka rena maganarsa, suka yi wa annabawansa dariyar reni, har sai da fushin Ubangiji ya tasar a kan mutanensa babu makawa.
Mais ils se moquaient des messagers de Dieu, ils méprisaient ses paroles, et ils traitaient ses Prophètes de Séducteurs, jusqu'à ce que la fureur de l'Eternel s'alluma tellement contre son peuple, qu'il n'y eut plus de remède.
17 Ya bashe su ga sarkin Babiloniyawa wanda ya karkashe samarinsu da takobi a wuri mai tsarki, bai yi juyayin saurayi, ko budurwa, ko tsoho, ko gajiyayye ba. Allah ya bashe su duka ga Nebukadnezzar.
C'est pourquoi il fit venir contre eux le Roi des Caldéens, qui tua leurs jeunes gens avec l'épée dans la maison de leur Sanctuaire, et il ne fut point touché de compassion envers les jeunes hommes, ni envers les filles, ni envers les vieillards et décrépits; il les livra tous entre ses mains.
18 Nebukadnezzar ya kwashe dukan kayayyaki daga haikalin Allah, babba da ƙarami, da ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin sarki da na fadawansa zuwa Babilon.
Et il fit apporter à Babylone tous les vaisseaux de la maison de Dieu, grands et petits, et les trésors de la maison de l'Eternel, et les trésors du Roi, et ceux de ses principaux [officiers].
19 Suka cinna wa haikalin Allah wuta, suka rurrushe katangar Urushalima; suka ƙone dukan fada, suka kuma lalace kome mai amfani da yake can.
On brûla aussi la maison de Dieu, on démolit les murailles de Jérusalem; et on mit en feu tous ses palais, et on ruina tout ce qu'il y avait d'exquis.
20 Waɗanda ba a kashe ba kuwa Nebukadnezzar ya kwashe su, ya kai Babilon, suka zama bayinsa da na’ya’yansa maza har zuwa kahuwar mulkin Farisa.
Puis [le roi de Babylone] transporta à Babylone tous ceux qui étaient échappés de l'épée; et ils lui furent esclaves, à lui et à ses fils, jusqu' au temps de la Monarchie des Perses.
21 Ƙasar ta more hutun Asabbacinta; a dukan lokacin zamanta kango ta huta, har sai da shekaru saba’in nan suka cika bisa ga maganar Ubangiji da Irmiya ya faɗi.
Afin que la parole de l'Eternel, prononcée par Jérémie, fût accomplie, jusqu'à ce que la terre eût pris plaisir à ses Sabbats et durant tous les jours qu'elle demeura désolée, elle se reposa, pour accomplir les soixante-dix années.
22 Don a cika maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya, a shekara farko ta Sairus sarkin Farisa, sai Ubangiji ya motsa zuciyar Sairus na Farisa don yă yi shela a dukan masarautarsa, ya kuma sa shi a rubuce cewa,
Or la première année de Cyrus Roi de Perse, afin que la parole de l'Eternel prononcée par Jérémie fût accomplie, l'Eternel excita l'esprit de Cyrus Roi de Perse, qui fit publier dans tout son Royaume, et même par Lettres, en disant:
23 “Ga abin da Sairus sarkin Farisa ya ce, “‘Ubangiji Allah na sama, ya ba ni dukan mulkokin duniya, ya kuma naɗa ni in gina masa haikali a Urushalima a Yahuda. Duk wani na mutanensa a cikinku, bari yă haura yă tafi, bari kuma Ubangiji Allahnsa yă kasance tare da shi.’”
Ainsi a dit Cyrus, Roi de Perse: L'Eternel, le Dieu des cieux, m'a donné tous les Royaumes de la terre, lui-même m'a ordonné de lui bâtir une maison à Jérusalem, en Judée. Qui est-ce d'entre vous de tout son peuple [qui s'y veuille employer?] L'Eternel son Dieu soit avec lui, et qu'il monte.

< 2 Tarihi 36 >