< 2 Tarihi 24 >

1 Yowash yana da shekara goma sha bakwai sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarauta a Urushalima shekara arba’in. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ce; ita daga Beyersheba.
Joas était âgé de sept ans quand il commença à régner, et il régna quarante ans à Jérusalem. Sa mère avait nom Tsibia, [et] elle était de Béer-sebah.
2 Yowash ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji duka shekarun Yehohiyada firist.
Or Joas fit ce qui est droit devant l'Eternel, durant tout le temps de Jéhojadah le Sacrificateur.
3 Yehohiyada ya zaɓi mata biyu dominsa, yana kuma da’ya’ya maza da’ya’ya mata.
Et Jéhojadah lui donna deux femmes, desquelles il eut des fils et des filles.
4 Wani lokaci daga baya Yowash ya yanke shawara yă gyara haikalin Ubangiji.
Après cela Joas prit à cœur de renouveler la maison de l'Eternel.
5 Ya tara firistoci da Lawiyawa wuri ɗaya ya ce musu, “Ku je garuruwan Yahuda ku karɓa kuɗin da ya kamata a biya shekara-shekara daga dukan Isra’ila, don gyaran haikalin Allahnku. Ku yi haka yanzu.” Amma Lawiyawa ba su yi haka nan da nan ba.
Et il assembla les Sacrificateurs et les Lévites, et leur dit: Allez par les villes de Juda, et amassez de l'argent de tout Israël, pour réparer la maison de votre Dieu, d'année en année, et hâtez cette affaire; mais les Lévites ne la hâtèrent point.
6 Saboda haka sarki ya kira Yehohiyada babban firist ya ce masa, “Me ya sa ba ka bukaci Lawiyawa su kawo harajin da Musa bawan Ubangiji ya ce a biya daga Yahuda da Urushalima da kuma taron Isra’ila domin Tentin Sujada Shaida ba?”
Et le Roi appela Jéhojadah le principal [Sacrificateur], et lui dit: Pourquoi n'as-tu pas fait en sorte que les Lévites apportassent de Juda, et de Jérusalem, et de tout Israël, le tribut ordonné par Moïse serviteur de l'Eternel, pour le Tabernacle du Témoignage?
7 Yanzu’ya’ya muguwar macen nan Ataliya maza sun fasa zuwa cikin haikalin Allah, suka kuma yi amfani da kayayyaki masu tsarki ma wa Ba’al.
Car la méchante Hathalie [et] ses enfants avaient dépouillé la maison de Dieu, et ils avaient même approprié aux Bahalins toutes les choses consacrées à la maison de l'Eternel.
8 Bisa ga umarnin sarki, aka yi akwati aka sa a waje, a mashigin haikalin Ubangiji.
C'est pourquoi le Roi commanda qu'on fit un coffre, et qu'on le mît à la porte de la maison de l'Eternel en dehors.
9 Aka yi umarni a Yahuda da Urushalima cewa ya kamata suka kawo wa Ubangiji harajin da Musa bawan Allah ya bukaci daga Isra’ila a hamada.
Puis on publia dans Juda et dans Jérusalem, qu'on apportât à l'Eternel l'impôt que Moïse serviteur de Dieu avait mis dans le désert sur Israël.
10 Dukan hafsoshi da dukan mutane suka kawo nasu kuɗin da aka sa musu da farin ciki, suna zuba su cikin akwatin sai da ya cika.
Et tous les principaux et tout le peuple s'en réjouirent; et ils apportèrent [l'argent], et le jetèrent dans le coffre, jusqu'à ce qu'on eût achevé [de réparer le Temple].
11 Duk sa’ad da Lawiyawa suka fito da akwatin zuwa ga hafsoshin sarki, suka kuma ga cewa akwatin yana da kuɗi mai yawa, sai magatakardan fada da hafsan babban firist su zo su juya kuɗin daga akwatin su mai da shi wurinsa. Sun riƙa yin haka kullum suka tara kuɗi mai yawa.
Or quand les Lévites emportaient le coffre suivant l'ordre du Roi, ce qu'on faisait dès qu'on voyait qu'il y avait beaucoup d'argent; le Secrétaire du Roi, et le Commis du principal Sacrificateur venaient, et vidaient le coffre, puis ils le reportaient, et le remettaient en sa place Ils faisaient ainsi tous les jours; et on amassa quantité d'argent.
12 Sarki da Yehohiyada suka ba da shi ga mutanen da suka yi aikin da ake bukata don haikalin Ubangiji. Suka ɗauki masu gini da kafintoci don su gyara haikalin Ubangiji, da kuma ma’aikatan ƙarafa da tagulla don su gyara haikalin.
Et le Roi et Jéhojadah le distribuaient à ceux qui avaient la charge de l'ouvrage du service de la maison de l'Eternel, lesquels louaient des tailleurs de pierres et des charpentiers pour refaire la maison de l'Eternel, et des ouvriers travaillant en fer et en airain pour réparer la maison de l'Eternel.
13 Mutanen da suke lura da aikin natsattsu ne, kuma gyare-gyaren suka ci gaba a ƙarƙashinsu. Suka sāke gina haikalin Allah bisa ga ainihin fasalinsa suka ƙara masa ƙarfi.
Ceux donc qui avaient la charge de l'ouvrage travaillèrent, et il fut entièrement achevé par leur moyen, de sorte qu'ils rétablirent la maison de Dieu en son état, et l'affermirent.
14 Da suka gama, suka kawo sauran kuɗin wa sarki da Yehohiyada, da su ne kuwa aka yi kayayyaki domin hidima da kuma domin hadayun ƙonawa, haka kuma kwanoni da sauran kayayyakin zinariya da azurfa. Muddin Yehohiyada yana raye, aka riƙa kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
Et dès qu'ils eurent achevé, ils apportèrent devant le Roi et devant Jéhojadah le reste de l'argent, dont il fit faire des ustensiles pour la maison de l'Eternel; [savoir] des ustensiles pour le service et pour les oblations, et des tasses et d'autres ustensiles d'or et d'argent; et ils offrirent continuellement des holocaustes dans la maison de l'Eternel, durant tout le temps de Jéhojadah.
15 Yanzu Yehohiyada ya tsufa kuma cike da shekaru, ya kuwa mutu yana da shekara ɗari da talatin.
Or Jéhojadah étant devenu vieux et rassasié de jours, mourut. Il était âgé de cent trente ans quand il mourut.
16 Aka binne shi tare da sarakuna a cikin Birnin Dawuda, saboda kirkin da ya yi a Isra’ila wa Allah da haikalinsa.
Et on l'ensevelit en la Cité de David avec les Rois, parce qu'il avait fait du bien en Israël, envers Dieu, et envers sa maison.
17 Bayan mutuwar Yehohiyada, hafsoshin Yahuda suka zo suka yi mubaya’a wa sarki, ya kuma saurare su.
Mais après que Jéhojadah fut mort, les principaux de Juda vinrent, et se prosternèrent devant le Roi; [et] alors le Roi les écouta.
18 Suka yashe haikalin Ubangiji Allah na kakanninsu, suka bauta wa ginshiƙan Ashera da kuma gumaka. Saboda laifinsu, fushin Allah ya sauko a kan Yahuda da Urushalima.
Et ils abandonnèrent la maison de l'Eternel le Dieu de leurs pères, et [s'attachèrent] au service des bocages, et des faux dieux; c'est pourquoi la colère de [l'Eternel s'alluma] contre Juda et contre Jérusalem, parce qu'ils s'étaient rendus coupables en cela.
19 Ko da yake Ubangiji ya aiki annabawa zuwa wurin mutane don su dawo da su gare shi, kuma ko da yake sun ba da shaida a kansu, ba su saurara ba.
Et quoiqu'il leur envoyât des Prophètes pour les faire retourner à l'Eternel, et que [ces Prophètes] les [en] sommassent, toutefois ils ne voulurent point écouter.
20 Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Zakariya ɗan Yehohiyada firist. Ya tsaya a gaban mutane ya ce, “Ga abin da Allah ya ce, ‘Me ya sa ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji ba? Ba za ku yi nasara ba. Domin kun yashe Ubangiji, shi ma ya yashe ku.’”
Et même l'Esprit de Dieu revêtit Zacharie fils de Jéhojadah le Sacrificateur, de sorte qu'il se tint debout au dessus du peuple, et leur dit: Dieu a dit ainsi: Pourquoi transgressez-vous les commandements de l'Eternel? Car vous ne prospérerez point; [et] parce que vous avez abandonné l'Eternel, il vous abandonnera aussi.
21 Amma suka yi masa maƙarƙashiya, kuma ta wurin umarnin sarki suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu a filin haikalin Ubangiji.
Et ils se liguèrent contre lui, et l'assommèrent de pierres, par le commandement du Roi, au parvis de la maison de l'Eternel;
22 Sarki Yowash bai tuna da alherin da Yehohiyada mahaifin Zakariya ya nuna masa ba, sai ya kashe ɗansa, wanda ya ce yayinda yake mutuwa, “Bari Ubangiji yă dubi wannan yă kuma sāka maka.”
De sorte que le Roi Joas ne se souvint point de la gratuité dont Jéhojadah, père de Zacharie, avait usé envers lui; mais il tua son fils, qui en mourant dit: Que l'Eternel le voie, et le redemande!
23 Da shekara ta kewaye, mayaƙan Aram suka yi gāba da Yowash suka kai hari wa Yahuda da Urushalima suka kuma kashe dukan shugabannin mutane, suka aika da dukan ganima zuwa ga sarkinsu a Damaskus.
Et il arriva qu'au bout d'un an l'armée de Syrie monta contre lui, et vint en Juda et à Jérusalem, et [les Syriens] détruisirent d'entre le peuple tous les principaux du peuple, et envoyèrent au Roi à Damas tout leur butin.
24 Ko da yake mayaƙan Arameyawa sun zo da mutane kaɗan kawai, Ubangiji ya sa suka ci nasara a kan sojojin Yahuda mafi yawa, don mutanen Yahuda sun rabu da Ubangiji Allah na kakanninsu, aka kuma hukunta Yowash.
Et quoique l'armée venue de Syrie fût peu nombreuse, l'Eternel livra pourtant entre leurs mains une très-grosse armée, parce qu'ils avaient abandonné l'Eternel Dieu de leurs pères. Ainsi [les Syriens] mirent Joas pour un exemple de jugement.
25 Sa’ad da Arameyawa suka janye, suka bar Yowash da mummunan rauni. Hafsoshinsa suka haɗa baki a kansa saboda kisan ɗan Yehohiyada firist da ya yi, suka kashe shi a kan gadonsa. Ta haka ya mutu aka kuma binne shi makabartan sarakuna.
Et quand ils se furent retirés d'avec lui, parce qu'ils l'avaient laissé dans de grandes langueurs, ses serviteurs conjurèrent contre lui, à cause du meurtre des fils de Jéhojadah le Sacrificateur, et le tuèrent sur son lit; et ainsi il mourut, et on l'ensevelit en la Cité de David, mais on ne l'ensevelit point aux sépulcres des Rois.
26 Waɗanda suka haɗa bakin kuwa su ne Zabad ɗan Shimeyat wata mutuniyar Ammon da Yehozabad ɗan Shimrit wata mutuniyar Mowab.
Et ce sont ici ceux qui conjurèrent contre lui, Zabad, fils de Simhat femme Hammonite, et Jéhozabad fils de Simrith femme Moabite.
27 Labarin’ya’yansa maza, annabce-annabce masu yawa game da shi, da tarihin gyaran haikalin Allah suna a rubuce a rubuce-rubuce a littafin sarakuna. Amaziya ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Or quant à ses enfants, et à la grande levée de deniers qui avait été faite pour lui, et au rétablissement de la maison de Dieu, voilà, ces choses sont écrites dans les Mémoires du Livre des Rois; et Amatsia son fils régna en sa place.

< 2 Tarihi 24 >