< 2 Tarihi 29 >

1 Hezekiya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Abiya,’yar Zakariya.
Hezekiah was 25 years old when he became the king [of Judah]. He ruled from Jerusalem for 29 years. His mother was Abijah, the daughter of [a man whose name was] Zechariah.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda kakansa Dawuda ya yi.
Hezekiah did things that Yahweh considered to be right, like his ancestor King David had done.
3 A wata na farkon a farkon shekarar mulkinsa, ya buɗe ƙofofin haikalin Ubangiji ya gyara su.
During March of the first year that Hezekiah was ruling Judah, he unlocked the doors of the temple, and his workers repaired them.
4 Ya kawo firistoci da Lawiyawa, ya tattara su a filin da yake a gefen gabas
Then he gathered the priests and other descendants of Levi in the area on the east side of the temple,
5 ya kuma ce musu, “Ku saurare ni, Lawiyawa! Ku tsarkake kanku yanzu, ku kuma tsarkake haikalin Ubangiji Allah na kakanninku. Ku fid da ƙazanta daga wuri mai tsarki.
and he said to them, “You descendants of Levi, listen to me! Consecrate yourselves. And then consecrate the temple of Yahweh, the God whom our ancestors [worshiped/belonged to]. Remove from the temple all the things that are not pleasing to God.
6 Kakanninku ba su yi aminci ba; suka aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnmu, suka kuma yashe shi. Suka juya fuskokinsu daga mazaunin Ubangiji suka kuma juya masa baya.
Our ancestors disobeyed God; they did many things that he considered to be evil, things that were not pleasing to him. They abandoned this place where Yahweh lives, and they have turned away from him.
7 Suka kulle ƙofofin shirayi, suka kuma kashe fitilu. Ba su ƙone turare ko su miƙa hadayun ƙonawa a wuri mai tsarki ga Allah na Isra’ila ba.
They locked the doors of the temple and extinguished the lamps. They did not burn any incense, and they did not offer any sacrifices that were to be completely burned [on the altar].
8 Saboda haka, fushin Ubangiji ya fāɗo a kan Yahuda da Urushalima; ya mai da su abin tsoro da abin banrazana da kuma abin ba’a, kamar yadda kuke gani da idanunku.
Therefore, Yahweh has become very angry with us people of Jerusalem and [other places in] Judah, and he has caused other people to become frightened and horrified [when they hear what Yahweh did to punish us]. And they ridicule us. You know this very well.
9 Abin da ya sa ke nan kakanninmu suka fāɗi ta takobi, kuma shi ya sa aka kai’ya’yanmu maza da’ya’yanmu mata da matanmu bauta.
That is why our fathers have been killed in battles, and our sons and daughters and our wives have been captured and taken [to other countries].
10 Yanzu ina niyya in yi alkawari da Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin fushinsa yă kauce daga gare mu.
But now I intend to make an agreement with Yahweh, our God, in order that he will no longer be angry with us.
11 ’Ya’yana maza, kada ku yi sakaci yanzu, gama Ubangiji ya zaɓe ku don ku tsaya a gabansa ku kuma yi masa hidima, don ku yi hidima a gabansa ku kuma ƙone turare.”
[You who are like] my sons, do not waste any time. [Do immediately what Yahweh wants you to do.] Yahweh has chosen you to stand in his presence and offer sacrifices and burn incense.”
12 Sai waɗannan Lawiyawa suka shiga aiki, daga Kohatawa Mahat ɗan Amasai da Yowel ɗan Azariya. Daga Kabilar Merari, Kish ɗan Abdi da Azariya ɗan Yahallelel. Daga Gershonawa, Yowa ɗan Zimma da Eden ɗan Yowa.
Then these descendants of Levi started to work [in the temple]: From the descendants of Kohath there were Mahath the son of Amasai, and Joel the son of Azariah. From the descendants of Merari there were Kish the son of Abdi, and Azariah the son of Jehallelel. From the descendants of Gershon there were Joah the son of Zimmah, and Eden the son of Joah.
13 Daga zuriyar Elizafan, Shimri da Yehiyel. Daga zuriyar Asaf, Zakariya da Mattaniya.
From the descendants of Elizaphan there were Shimri and Jeiel. From the descendants of Asaph there were Zechariah and Mattaniah.
14 Daga iyalin Heman, Yehiyel da Shimeyi. Daga zuriyar Yedutun, Shemahiya da Uzziyel.
From the descendants of Heman there were Jehiel and Shimei. From the descendants of Jeduthun there were Shemaiah and Uzziel.
15 Da suka tattara’yan’uwansu suka kuma tsarkake kansu, sai suka shiga ciki suka tsarkake haikalin Ubangiji, kamar yadda sarki ya umarta, suna bin maganar Ubangiji.
When those men had gathered their fellow descendants of Levi and had consecrated themselves, they entered the temple in order to consecrate it. That was what the king had commanded them to do, and they were also obeying what Yahweh had commanded.
16 Firistoci suka shiga cikin wuri mai tsarki na Ubangiji suka tsarkake shi. Suka fitar da dukan abin da yake marar tsabta da suka samu a haikalin Ubangiji zuwa filin haikalin Ubangiji. Lawiyawa suka ɗauke su suka kai su Kwarin Kidron.
The priests entered the temple to consecrate it. They brought out into the courtyard of the temple everything that they had found in the temple that was not pleasing to Yahweh. Then the descendants of Levi took those things down to the Kidron Valley [and burned them there].
17 Suka fara tsarkakewar a rana ta farko na farkon wata, a rana ta takwas na watan kuwa suka kai shirayin Ubangiji. Karin kwana takwas kuma suka tsarkake haikalin Ubangiji kansa, suka gama a rana ta goma sha shida na farkon wata.
The priests and other descendants of Levi started this work on the first day of March and finished purifying the courtyard [of the temple] on the eighth day of that month, and they finished purifying the temple one week later.
18 Sa’an nan suka tafi wurin Sarki Hezekiya suka faɗa masa, “Mun tsarkake haikalin Ubangiji gaba ɗaya, bagaden ƙone hadaya tare da dukan kayayyakinsa, da tebur don shirya tsarkaken burodi, tare da dukan kayayyakinsa.
Then they went to King Hezekiah and reported, “We have purified all parts of the temple, and the altar where sacrifices are completely burned, and all the items used at the altar, the table on which the priests place the sacred bread, and the things [used at that table].
19 Mun shirya muka kuma tsarkake dukan kayayyakin da Sarki Ahaz ya cire cikin rashin amincinsa yayinda yake sarki. Yanzu suna a gaban bagaden Ubangiji.”
While Ahaz was our king, he disobeyed what Yahweh had commanded, and he removed from the temple many things [that should be there], but now we have brought them back and placed them in front of the sacred altar.”
20 Da sassafe kashegari Sarki Hezekiya ya tattara manyan birni wuri ɗaya, suka haura zuwa haikalin Ubangiji.
Early the next morning, King Hezekiah gathered together the city officials, and they went to the [courtyard of the] temple.
21 Suka kawo bijimai bakwai, raguna bakwai, bunsurai bakwai da kuma awaki mata bakwai a matsayin hadaya don zunubi domin masarauta, domin wuri mai tsarki da kuma domin Yahuda. Sarki ya umarce firistoci, zuriyar Haruna, su miƙa waɗannan a bagaden Ubangiji.
They took with them seven bulls, seven rams, seven male lambs, and seven male goats to be an offering in order that Yahweh would forgive the sins of all the people in the kingdom of Judah, and in order to purify the temple. The king commanded that the priests, who were descendants of Aaron, should offer those animals to be sacrificed to Yahweh on the altar.
22 Saboda haka suka yayyanka bijiman, firistoci suka karɓi jinin suka yayyafa a kan bagade. Suka kuma yanka ragunan suka yayyafa jinin a bagaden. Haka kuma suka yanka’yan ragunan suka yayyafa jinin a bagaden.
So first the priests slaughtered those bulls, and took their blood and sprinkled it on the altar. Then they slaughtered the rams and sprinkled their blood on the altar. Then they slaughtered the lambs and sprinkled their blood on the altar.
23 Aka kawo awaki domin hadaya don zunubi a gaban sarki da taron, suka kuwa ɗibiya hannuwansu a kansu.
The goats that were slaughtered to be an offering in order that Yahweh would forgive the sins of the people were brought to the king and the others who were there. Then the king and those who were present laid their hands on those goats.
24 Sa’an nan firistoci suka yayyanka awakin suka miƙa jininsu a bagade domin hadaya don zunubi don kafara saboda dukan Isra’ila, domin sarki ya umarta a yi hadaya ta ƙonawa da hadaya don zunubi domin dukan Isra’ila.
Then the priests slaughtered those goats and splashed their blood on the altar in order that Yahweh would forgive the sins that all the Israeli people had committed. The priests did that because the king had commanded that offerings that would be completely burned [on the altar] and other sacrifices should be made for all the people of Israel.
25 Sarki Hezekiya ya ajiye Lawiyawa a cikin haikalin Ubangiji tare da ganguna, garayu da molaye, yadda Dawuda da Gad mai duba na sarki da kuma annabi Natan suka tsara. Ubangiji ne ya umarta wannan ta wurin annabawansa.
The king then told the descendants of Levi to stand in the temple with their cymbals and harps and lyres, obeying what David and his prophets Gad and Nathan had commanded. Those were things that Yahweh had told his prophets that the descendants of Levi should do.
26 Saboda haka Lawiyawa suka tsaya a shirye tare da kayan kiɗin Dawuda, firistoci kuma tare da ƙahoninsu.
So the descendants of Levi [went and] stood in the temple, ready to play the musical instruments that King David had given to them. And the priests were ready to blow their trumpets.
27 Hezekiya ya ba da umarni a miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagade. Yayinda aka fara miƙawa, ana rerawa ga Ubangiji, tare da bushe-bushe da kiɗe-kiɗen kayan waƙa na Dawuda sarkin Isra’ila.
Then Hezekiah told some of the priests to burn the animals that would be sacrificed on the altar. When they started to burn the animals, the people started to sing to [praise] Yahweh, while the other descendants of Levi were playing their instruments.
28 Dukan taron suka durƙusa suka yi sujada, yayinda mawaƙa suke rerawa, ana kuma busa ƙahoni, dukan wannan ya ci gaba sai da aka gama miƙa hadaya ta ƙonawa.
All the people who were there bowed to worship Yahweh, while the singers sang and the trumpeters blew their trumpets. They continued to do this until they had finished slaughtering all the animals that would be completely burned.
29 Sa’ad da aka gama miƙawa, sai sarki da mutanen da suke tare da shi suka durƙusa suka yi sujada.
When they finished making those offerings, the king and all those who were there knelt down and worshiped Yahweh.
30 Sarki Hezekiya da fadawansa suka umarci Lawiyawa su yabi Ubangiji da kalmomin Dawuda da na Asaf mai duba. Saboda haka suka rera yabai da murna, suka sunkuyar da kawunansu suka yi sujada.
Then King Hezekiah and his officials commanded the descendants of Levi to praise Yahweh, singing the songs [composed/written] by David and Asaph the prophet. So they sang songs joyfully and bowed their heads to worship.
31 Sa’an nan Hezekiya ya ce, “Yanzu kun keɓe kanku ga Ubangiji. Ku zo ku kuma kawo hadayu da hadayun godiya zuwa ga haikalin Ubangiji.” Saboda haka taron suka kawo hadayu da hadayun godiya, da kuma dukan waɗanda suke da niyya suka kawo hadayun ƙonawa.
Then Hezekiah said, “You have now dedicated yourselves to Yahweh. So come close to the temple and bring animals to be sacrificed and other offerings to thank [Yahweh for what he has done for you].” And those who wanted to bring animals to be completely burned [on the altar] brought them.
32 Yawan hadayun ƙonawan da taron suka kawo, bijimai saba’in ne, raguna ɗari da kuma bunsurai ɗari biyu, dukansu kuwa domin hadayun ƙonawa ga Ubangiji ne.
Altogether they brought 70 bulls, 100 rams, and 200 male lambs to be completely burned on the altar.
33 Dabbobin da aka tsarkake a matsayi hadayu sun kai bijimai ɗari shida da tumaki da kuma awaki dubu uku.
The other animals that they brought were 600 bulls and 3,000 sheep and goats that were set apart to be sacrifices.
34 Firistoci fa, suka kāsa sosai don fiɗan dukan dabbobin da za a miƙa don hadayun ƙonawa; saboda haka’yan’uwansu Lawiyawa suka taimake su har aka gama aiki kafin sauran firistoci su sami damar tsarkake kansu. Gama Lawiyawa sun fi firistoci himma wajen tsarkakewar kansu.
But there were not enough priests to remove the skins from the animals that would be completely burned [on the altar]. So their fellow descendants of Levi helped them until that work was finished, and until other priests had purified/consecrated themselves to do that work. It was necessary for them to do that because many of the priests had not yet performed the rituals to consecrate themselves for that work, like the descendants of Levi had done.
35 Aka kasance da hadayun ƙonawa a yalwace, tare da kitsen hadayun salama da hadayun sha da suke tafe da hadayun ƙonawa. Saboda haka aka sāke kafa hidimar haikalin Ubangiji.
In addition to the all the offerings that were completely burned [on the altar], the priests also burned the fat of the other animals that were sacrificed to maintain good fellowship with Yahweh, and the usual wine offerings. So the worship at the temple began again.
36 Hezekiya da dukan mutane suka yi farin ciki game da abin da Allah ya yi wa mutanensa, domin ya faru farat ɗaya.
And Hezekiah and all the other people of Judah celebrated, because God had enabled them to do all those things very quickly.

< 2 Tarihi 29 >