< 2 Tarihi 11 >

1 Sa’ad da Rehobowam ya iso Urushalima, ya tattara mayaƙa dubu ɗari takwas daga gidan Yahuda da Benyamin, don su yi yaƙi da Isra’ila su sāke mai da mulki wa Rehobowam.
And Roboam came to Jerusalem, and called together all the house of Juda and of Benjamin, a hundred and fourscore thousand chosen men and warriors, to fight against Israel, and to bring back his kingdom to him.
2 Amma wannan maganar Ubangiji ta zo ga Shemahiya mutumin Allah.
And the word of the Lord came to Semeias the man of God, saying:
3 “Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon sarkin Yahuda da kuma dukan Isra’ilawan da suke a Yahuda da Benyamin,
Speak to Roboam the son of Solomon the king of Juda, and to all Israel, in Juda and Benjamin:
4 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku. Ku tafi gida kowannenku, gama wannan yi na ne.’” Saboda haka suka yi biyayya ga maganar Ubangiji suka kuma koma daga takawa don yaƙi da Yerobowam.
Thus saith the Lord: You shall not go up, nor fight against your brethren: let every man return to his own house, for by my will this thing has been done. And when they heard the word of the Lord, they returned, and did not go against Jeroboam,
5 Rehobowam ya zauna a Urushalima ya kuma gina garuruwa don kāriya a cikin Yahuda.
And Roboam dwelt in Jerusalem, and built walled cities in Juda.
6 Betlehem, Etam, Tekowa,
And he built Bethlehem, and Etam, and Thecue,
7 Bet-Zur, Soko, Adullam,
And Bethsur, and Socho, and Odollam,
8 Gat, Maresha, Zif,
And Geth, and Maresa, and Ziph,
9 Adorayim, Lakish, Azeka,
And Aduram, and Lachis, and Azecha,
10 Zora, Aiyalon da Hebron. Waɗannan su ne garuruwan katanga a cikin Yahuda da Benyamin.
Saraa also, and Aialon, and Hebron, which are in Juda and Benjamin, well fenced cities.
11 Ya ƙarfafa kāriyarsu ya kuma sa shugabannin mayaƙa a cikinsu, tare da tanadin abinci, man zaitun da kuma ruwan inabi.
And when he had enclosed them with walls, he put in them governors and storehouses of provisions, that is, of oil and of wine.
12 Ya sa garkuwoyi da māsu a cikin dukan biranen, ya kuma sa suka zama da ƙarfi. Saboda haka Yahuda da Benyamin suka zama nasa.
Moreover in every city he made an armoury of shields and spears, and he fortified them with great diligence, and he reigned over Juda, and Benjamin,
13 Firistoci da Lawiyawa daga dukan yankuna ko’ina a Isra’ila suka haɗa kai da shi.
And the priests and Levites, that were in all Israel, came to him out of all their seats,
14 Lawiyawa suka ma bar makiyayansu da mallakarsu, suka zo Yahuda da Urushalima domin Yerobowam da’ya’yansa maza sun ƙi su a matsayin firistocin Ubangiji.
Leaving their suburbs, and their possessions, and passing over to Juda, and Jerusalem, because Jeroboam and his sons had cast them off, from executing the priestly office to the Lord.
15 Yerobowam ya naɗa firistocinsa domin masujadan kan tudu da kuma domin gumakan nan na akuya da maraƙin da ya yi.
And he made to himself priests for the high places, and for the devils, and for the calves which he had made.
16 Waɗanda suke daga kowane kabilar Isra’ila waɗanda suka sa zuciya a kan neman Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka bi Lawiyawa zuwa Urushalima don su miƙa hadayu ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
Moreover out of all the tribes of Israel, whosoever gave their heart to seek the Lord the God of Israel, came into Jerusalem to sacrifice their victims before the Lord the God of their fathers.
17 Suka ƙarfafa mulkin Yahuda suka kuma goyi bayan Rehobowam ɗan Solomon shekaru uku, suna tafiya a hanyoyin Dawuda da Solomon a wannan lokaci.
And they strengthened the kingdom of Juda, and established Roboam the son of Solomon for three years: for they walked in the ways of David and of Solomon, only three years.
18 Rehobowam ya auri Mahalat,’yar Yerimot ɗan Dawuda wadda Abihayil’yar Eliyab ɗan Yesse ta haifa.
And Roboam took to wife Mahalath, the daughter of Jerimoth the son of David: and Abihail the daughter of Eliab the son of Isai.
19 Ta haifa masa’ya’ya maza. Yewush, Shemariya da Zaham.
And they bore him sons Jehus, and Somorias, and Zoom.
20 Sa’an nan ya auri Ma’aka’yar Absalom, wadda ta haifa masa Abiya, Attai, Ziza da kuma Shelomit.
And after her he married Maacha the daughter of Absalom, who bore him Abia and Ethai, and Ziza, and Salomith.
21 Rehobowam ya ƙaunaci Ma’aka’yar Absalom fiye da sauran matansa da ƙwarƙwaransa. Duka-duka dai ya auri mata goma sha takwas da ƙwarƙwarai sittin, yana da’ya’ya maza ashirin da takwas da’ya’ya mata sittin.
And Roboam loved Maacha the daughter of Absalom above all his wives, and concubines: for he had married eighteen wives, and threescore concubines: and he beget eight and twenty sons, and threescore daughters.
22 Rehobowam ya naɗa Abiya ɗan Ma’aka yă zama babba yerima a cikin’yan’uwansa, don dai yă naɗa shi sarki.
But he put at the head of them Abia the son of Maacha to be the chief ruler over all his brethren: for he meant to make him king,
23 Ya yi hikima, ya watsar da waɗansu’ya’yansa a dukan yankunan Yahuda da Benyamin, da kuma a dukan birane masu katanga. Ya ba su tanadi mai yawa ya kuma aurar musu mata masu yawa.
Because he was wiser and mightier than all his sons, and in all the countries of Juda, and of Benjamin, and in all the walled cities: and he gave them provisions in abundance, and he sought many wives.

< 2 Tarihi 11 >