< 1 Tessalonikawa 1 >

1 Bulus, Sila da Timoti, Zuwa ga ikkilisiyar Tessalonikawa ta Allah Uba da Ubangiji Yesu Kiristi. Alheri da salama su kasance tare da ku.
Njafwe, Paulo ne Sailasi kayi ne Timoti. Tulamulembelenga ba Tesalonika momubungano mukasa a Lesa ne Mwami Yesu Klistu. Luse ne lumuno Lube nenjamwe.
2 Kullum muna gode wa Allah dominku duka, muna ambatonku cikin addu’o’inmu.
Tulalumbumga Lesa lyonse pacebo ca njamwe mwense kayi lyonse tulamushumbulunga mumipailo yetu.
3 Muna tunawa da aikinku ba fasawa a gaban Allah da Ubanmu ta wurin bangaskiya, da famar da kuke yi domin ƙauna, da kuma begenku marar gushewa ga Ubangijinmu Yesu Kiristi.
Tukute kumwanuka pamenso a Lesa pabintu mbyomwalensa pacebo ca lushomo lwenu, kayi mbuli ncomwalasebensa cangofu lushomo, kayi ne lusuno lwalapesheti musebense mwangofu, kayi ne kupembelela kwenu Mwami wetu Yesu Klistu ncekwashimpa.
4 Gama mun sani,’yan’uwa, ƙaunatattu na Allah, cewa ya zaɓe ku,
Mobanse tucinshi kwambeti Lesa umusuni kayi lamusala kuba bakendi.
5 domin bishararmu ba tă zo gare ku da kalmomi kawai ba, amma da iko, da Ruhu Mai Tsarki, da kuma cikakken tabbaci. Kun san irin rayuwar da muka yi a cikinku don amfaninku.
Pakwinga twalamuletela Mulumbe Waina, cakutasebensesha maswi onka, nsombi nengofu sha Mushimu Uswepa kayi cakutatonshanya sobwe. Mucinshi ncetwalikwikala nenjamwe, pakuyanda kumunyamfwilisha.
6 Har kuka zama masu koyi da mu da kuma Ubangiji; duk da tsananin wahala, kuka karɓi saƙon nan da farin ciki wanda Ruhu Mai Tsarki ya bayar.
Mwalakonkela bwikalo bwetu kayi ne bwa Mwami Yesu. Necikabeti mwalapita mumapensho anene, mwalatambula Mulumbe Waina mwakukondwa kwalakufuma ku Mushimu Uswepa.
7 Ta haka kuwa kuka zama gurbi ga dukan masu bi a Makidoniya da Akayya.
Neco mwalaba citondesho kubantu bashoma muli Yesu mu Makedoniya ne ku Akaya.
8 Saƙon Ubangiji ya fito daga gare ku ne ba a Makidoniya da Akayya kaɗai ba bangaskiyarku ga Allah ta zama sananne ko’ina. Saboda haka ba ma bukata mu faɗa wani abu a kai,
Bantu bangi balanyumfwa Mulumbe Waina kufuma kulinjamwe kutambowa abo baku Akaya ne ku Makedoniya bonka, nsombi impuwo ya lushomo lwenu muli Lesa yalamwaika ku masena onse. Neco lino kuliya ncotwela kwambapo sobwe.
9 gama su kansu su suke ba da labari irin karɓar da kuka yi mana. Suna faɗin yadda kuka juyo ga Allah daga gumaka don ku bauta wa Allah rayayye da kuma na gaskiya,
Bantu bonse balambanga sha ncemwalatutambula cena pacindi mpotwalamufwakashila, kayi mbuli ncemwalatushiya tumbwanga, nekusandukila kuli Lesa muyumi kwambeti mumusebenselenga.
10 ku kuma jira dawowar Ɗansa daga sama, wanda ya tasa daga matattu, Yesu, wanda ya cece mu daga fushi mai zuwa.
Kayi mulapembelelenga Mwanendi kufuma kwilu. Uyo ni Yesu, Lesa ngwalapundusha kubafu. Euyo latupulushunga ku bukalu bulesanga.

< 1 Tessalonikawa 1 >