< 1 Sama’ila 29 >

1 Filistiyawa suka tattara dukan rundunoninsu a Afek. Isra’ila kuwa suka yi sansani kusa da maɓulɓular da take Yezireyel.
Filistejci so torej vse svoje vojske zbrali skupaj k Aféku, Izraelci pa so se utaborili pri studencu, ki je v Jezreélu.
2 Sa’ad da sarakuna Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari-ɗari da na dubu-dubu. Dawuda da mutanensa suna biye a baya tare da Akish.
Knezi izmed Filistejcev so šli mimo po stotnijah in po tisočnijah, toda David in njegovi možje so šli mimo v zadnji straži z Ahíšem.
3 Komandodin Filistiyawa suka ce, “Waɗannan Ibraniyawa kuma fa?” Akish ya ce, “Wannan shi ne Dawuda hafsan Shawulu, sarkin Isra’ila. Yana nan tare da ni shekara guda ke nan. Ban kuwa taɓa samunsa da wani lahani ba tun daga ranar da ya bar Shawulu.”
Potem so princi Filistejcev rekli: »Kaj počnejo tukaj ti Hebrejci?« Ahíš je rekel princem Filistejcev: » Ali ni to David, služabnik Savla, Izraelovega kralja, ki je bil z menoj te dni ali ta leta in v njem nisem našel nobenega madeža, odkar je pripadel k meni, do tega dne?«
4 Amma komandodin Filistiyawa suka yi fushi, suka ce, “Ka sa mutumin nan yă koma zuwa wurin da ka ba shi yă zauna. Ba zai bi mu zuwa wurin yaƙi ba. Yana iya juya a kanmu lokacin yaƙin. Zai iya yin amfani da wannan zarafi yă ciccire kawunanmu don yă faranta wa maigidansa rai?
Filistejski princi pa so bili ogorčeni nad njim in filistejski princi so mu rekli: »Primoraj tega pajdaša, da se vrne, da bo lahko ponovno šel na svoj kraj, ki si mu ga določil in naj ne gre z nami dol v bitko, da nam v bitki ne bi bil nasprotnik, kajti s čim se bo prikupil svojemu gospodarju? Ali naj to ne bi bilo z glavami teh ljudi?«
5 Tuna fa, ba shi ne Dawuda ɗin da ake girmama da rawa da waƙoƙi ana cewa, “‘Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa dubbun dubbai ba’?”
Ali ni to David, o katerem so druga drugi pele v plesih, rekoč: »Savel je usmrtil svoje tisoče, David pa svoje deset tisoče?«
6 Saboda haka Akish ya kira Dawuda ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, na amince da kai tun daga ranar da ka zo wurina har yă zuwa yau, ban same ka da wani laifi ba, na kuma yi farin ciki in sa ka a cikin sojojina don ka yi mini aiki. Amma masu mulki nawa ba su yarda da kai ba.
Potem je Ahíš poklical Davida in mu rekel: »Zagotovo, kakor Gospod živi, si bil pošten in tvoje odhajanje in tvoje prihajanje z menoj v vojsko je dobro v mojem pogledu, kajti nisem našel zla v tebi od dneva tvojega prihoda k meni, do tega dne, pa vendar ti knezi niso naklonjeni.
7 Sai ka juya ka koma ka isa lafiya ba tare da ɓata wa masu mulkin Filistiyawa rai ba.”
Zato se sedaj vrni in pojdi v miru, da ne razžališ filistejskih knezov.«
8 Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Ka taɓa samun bawanka da laifi tun daga ranar da na zo har zuwa yanzu? Ina dalilin da ba zan tafi tare da kai in yaƙi maƙiyin ranka yă daɗe, sarki ba?”
David je rekel Ahíšu: »Toda kaj sem storil? Kaj si našel na svojem služabniku, dokler sem bil s teboj, do tega dne, da se ne smem iti bojevat zoper sovražnike svojega gospoda kralja?«
9 Akish ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala’ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’
Ahíš je odgovoril in Davidu rekel: »Vem, da si dober v mojih očeh, kakor Božji angel. Vendar so princi Filistejcev rekli: ›Ta ne bo šel z nami gor v bitko.‹
10 Ka tashi da sassafe, kai da bayin shugabanka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.”
Zato sedaj vstani zgodaj zjutraj s služabniki svojega gospoda, ki so prišli s teboj in takoj, ko boste zgodaj zjutraj pokonci in imeli svetlobo, odidite.«
11 Gari na wayewa tun da sassafe Dawuda da mutanensa suka tashi suka kama hanyar komawa ƙasar Filistiyawa. Filistiyawa kuwa suka haura zuwa Yezireyel.
Tako so David in njegovi možje zgodaj zjutraj vstali, da odrinejo, da se vrnejo v deželo Filistejcev. Filistejci pa so šli gor k Jezreélu.

< 1 Sama’ila 29 >