< 1 Yohanna 3 >

1 Dubi irin ƙaunar da Uba ya ƙaunace mu da ita mana, har ana ce da mu’ya’yan Allah! Haka kuwa muke! Dalilin da ya sa duniya ba tă san mu ba shi ne, don ba tă san shi ba.
Behold what kind of love the Father has given to us, that we may be called children of God. Because of this the world does not know you, because it did not know him.
2 Abokaina ƙaunatattu, yanzu, mu’ya’yan Allah ne, kuma abin da za mu zama nan gaba ba a riga an bayyana ba. Sai dai mun san cewa sa’ad da Kiristi ya bayyana, za mu zama kamar sa, domin za mu gan shi kamar yadda yake.
Beloved, now we are children of God, and it is not yet made known what we will be. But we know that whenever he is made known we will be like him, because we will see him as he is.
3 Duk mai wannan bege a cikinsa yakan tsarkake kansa, kamar yadda shi Kiristi yake da tsabta.
And every man who has this hope in him purifies himself, just as that man is pure.
4 Duk mai yin zunubi yana karya doka ne; tabbatacce, zunubi, karya doka ne.
Every man doing sin also does lawlessness, and sin is lawlessness.
5 Sai dai kun san cewa Kiristi ya bayyana ne domin yă ɗauke zunubanmu. A cikinsa kuwa babu zunubi.
And ye know that that man was made known so that he might take up our sins. And in him is no sin.
6 Ba mai rayuwa a cikinsa da yake cin gaba da yin zunubi. Kowa da yake aikata zunubi, bai taɓa ganinsa ba, bai ma san shi ba.
Every man abiding in him does not sin. Every man who is sinning has not seen him, nor has known him.
7 ’Ya’yana ƙaunatattu, kada ku yarda wani yă ruɗe ku. Duk mai yin abin da yake daidai mai adalci ne, yadda Kiristi yake mai adalci.
Little children, let no man lead you astray. He who is doing righteousness is righteous, just as that man is righteous.
8 Duk mai aikata abin da yake zunubi shi na Iblis ne, domin Iblis mai aikata zunubi ne tun farko. Dalilin da ya sa Ɗan Allah ya bayyana kuwa shi ne don yă rushe aikin Iblis.
He who is doing sin is of the devil, because the devil sinned from the beginning. The Son of God was made known for this, so that he might destroy the works of the devil.
9 Babu haifaffe na Allah da zai ci gaba da yin zunubi, domin iri na Allah yana a cikinsa; ba zai iya ci gaba da yin zunubi ba, domin haifaffe ne na Allah.
Every man who has been begotten of God is not doing sin, because his seed abides in him, and he cannot sin, because he has been begotten of God.
10 Ta haka muka san waɗanda suke’ya’yan Allah da kuma waɗanda suke’ya’yan Iblis. Duk wanda ba ya yin abin da yake daidai, ba ɗan Allah ba ne; haka ma wanda ba ya ƙaunar ɗan’uwansa.
By this the children of God are visible, and the children of the devil. Every man not doing righteousness is not of God, and he who is not loving his brother.
11 Wannan shi ne saƙon da kuka ji tun farko. Ya kamata mu ƙaunaci juna.
Because this is the message that ye heard from the beginning, that we should love each other.
12 Kada ku zama kamar Kayinu, wanda ya zama na mugun nan, ya kuma kashe ɗan’uwansa. Me ya sa ya kashe shi? Domin ayyukansa mugaye ne, na ɗan’uwansa kuma na adalci ne.
Not as Cain. He was of the wicked, and murdered his brother. And why did he murder him? Because his works were wrong, and his brother's right.
13 Kada ku yi mamaki’yan’uwana, in duniya ta ƙi ku.
Marvel not, my brothers, if the world hates you.
14 Mun san cewa mun riga mun ratsa daga mutuwa zuwa rai, domin muna ƙaunar’yan’uwanmu. Duk wanda ba ya ƙauna matacce ne har yanzu.
We know that we have passed out of death into life, because we love the brothers. He who is not loving the brother abides in death.
15 Duk mai ƙin ɗan’uwansa mai kisankai ne, kun kuma san cewa ba mai kisankan da yake da rai madawwami a cikinsa. (aiōnios g166)
Every man hating his brother is a man-killer. And ye know that no man-killer has eternal life abiding in him. (aiōnios g166)
16 Yadda muka san ƙauna ke nan, wato, Yesu Kiristi ya ba da ransa dominmu. Ya kamata mu ma mu ba da rayukanmu domin’yan’uwanmu.
By this we know love, because that man laid down his life for us. And we ought to lay down our lives for the brothers.
17 In wani yana da arziki, ya kuma ga ɗan’uwansa cikin rashi, bai kuwa taimake shi ba, anya, ƙaunar Allah tana a cikinsa kuwa?
But whoever has the world's living, and sees his brother having need, and closes his bowels from him, how does the love of God abide in him?
18 ’Ya’yana ƙaunatattu, kada mu yi ƙauna da fatar baki kawai, sai dai mu nuna ta ta wurin aikatawa da kuma gaskiya.
My little children, we should not love in word, nor with the tongue, but in deed and in truth.
19 Ta haka muka san cewa mu na gaskiya ne, kuma za mu iya tsaya a gaban Allah ba tare da rawar jiki ba.
And by this we know that we are of the truth, and will assure our hearts before him.
20 Idan zuciyarmu ta nuna mana muna da laifi, mun san cewa Allah ya fi zuciyarmu, ya kuma san dukan kome.
Because if our heart should condemn us, that God is greater than our heart, and knows all things.
21 Abokaina ƙaunatattu, in zukatanmu ba su ba mu laifi ba, muna da ƙarfin halin tsayawa a gaban Allah ke nan.
Beloved, if our heart should not condemn us, we have confidence toward God,
22 Muna kuma samun dukan abin da muka roƙa daga gare shi, domin muna biyayya da umarnansa, muna kuma yin abin da ya gamshe shi.
and whatever we may ask we receive from him, because we keep his commandments and do things pleasing in his sight.
23 Umarninsa kuwa shi ne, mu gaskata da sunan Ɗansa, Yesu Kiristi, mu kuma ƙaunaci juna kamar yadda ya umarce mu.
And this is his commandment, that we should believe in the name of his Son Jesus Christ, and love each other, just as he gave command.
24 Waɗanda suke biyayya da umarnansa kuwa suna rayuwa a cikinsa, shi kuma a cikinsu. Ta haka muka san cewa yana raye a cikinmu. Mun san haka ta wurin Ruhun da ya ba mu.
And he who keeps his commandments abides in him, and he in him. And by this we know that he abides in us, from the Spirit that he gave us.

< 1 Yohanna 3 >