< 1 Yohanna 2 >

1 ’Ya’yana ƙaunatattu, ina rubuta muku wannan ne don kada ku yi zunubi. Amma in wani ya yi zunubi, muna da wani wanda yake magana da Uba don taimakonmu, wato, Yesu Kiristi, Mai Adalci.
My little children, I write these things to you so that ye may not sin. And if any man does sin, we have an advocate with the Father-righteous Jesus Christ.
2 Shi ne hadayar kafara saboda zunubanmu, kuma ba don namu kaɗai ba amma har ma da zunuban duniya duka.
And he is the atonement for our sins, and not for ours only, but also for the whole world.
3 Ta haka za mu tabbata cewa mun san shi in muna yin biyayya da umarnansa.
And by this we know that we know him, if we keep his commandments.
4 Mutumin da ya ce, “Na san shi,” amma ba ya yin abin da ya umarta, maƙaryaci ne, gaskiya kuwa ba ta cikinsa.
He who says, I know him, and does not keep his commandments, is a liar, and the truth is not in this man.
5 Amma in wani ya yi biyayya da maganarsa, ƙaunar Allah ta zama cikakkiya ke nan a cikinsa. Ta haka muka san cewa muna cikinsa.
But whoever keeps his word, truly in this man the love of God is fully perfected. By this we know that we are in him.
6 Duk wanda ya ce yana rayuwa a cikinsa dole yă yi tafiya kamar yadda Yesu ya yi.
He who claims to abide in him he also ought so to walk just as that man walked.
7 Abokaina ƙaunatattu, ba sabon umarni nake rubuta muku ba, a’a, daɗaɗɗen umarnin nan ne, wanda kuke da shi tun farko. Wannan tsohon umarni shi ne saƙon da kuka riga kuka ji.
Brothers, I write no new commandment to you, but an old commandment that ye had from the beginning. The old commandment is the word that ye heard from the beginning.
8 Duk da haka ina rubuta muku sabon umarni; ana ganin gaskiyar umarnin a cikinsa da kuma cikinku, gama duhu yana shuɗewa, haske na gaskiya kuwa yana haskakawa.
Again, a new commandment I write to you, which is true in him and in you, because the darkness is passing away, and the true light now shines.
9 Duk wanda ya ce yana cikin haske yana kuma ƙin ɗan’uwansa, ashe a duhu yake har yanzu.
He who claims to be in the light, and hates his brother, is in the darkness until now.
10 Duk wanda yake ƙaunar ɗan’uwansa, a cikin hasken yake rayuwa ke nan, kuma babu wani abin da yake cikinsa da zai sa yă yi tuntuɓe.
He who loves his brother abides in the light, and no cause of stumbling is in him.
11 Amma duk wanda yake ƙin ɗan’uwansa, cikin duhu yake, yana kuma tafiya cikin duhu ke nan; bai ma san inda za shi ba, domin duhun ya makanta shi.
But he who hates his brother is in the darkness, and he goes about in the darkness, and knows not where he goes, because the darkness has blinded his eyes.
12 Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin an gafarta muku zunubanku saboda sunansa.
I write to you, little children, because your sins have been forgiven you through his name.
13 Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kun ci nasara a kan mugun nan.
I write to you, fathers, because ye have known him from the beginning. I write to you, young men, because ye have overcome evil. I write to you, children, because ye know the Father.
14 Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin kun san Uba. Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kuna da ƙarfi, maganar Allah kuwa tana zaune a cikinku, kun kuma ci nasara a kan mugun nan.
I wrote to you, fathers, because ye have know him from the beginning. I wrote to you, young men, because ye are strong, and the word of God abides in you, and ye have overcome evil.
15 Kada ku ƙaunaci duniya, ko wani abin da yake cikinta. In wani yana ƙaunar duniya, ƙaunar Uba ba ta cikinsa.
Love not the world, nor the things in the world. If any man loves the world, the love of the Father is not in him.
16 Gama duk abin da yake na duniya, kamar sha’awace-sha’awacen mutuntaka, sha’awar idanunsa, da kuma taƙama da abin da yake da shi, yake kuma yi, ba daga wurin Uba suke fitowa ba sai dai daga duniya.
Because everything in the world, the lust of the flesh, and the lust of the eyes, and the arrogance of life, is not of the Father, but is of the world.
17 Duniya da sha’awace-sha’awacenta suna shuɗewa, amma mutumin da yake aikata nufin Allah, zai rayu har abada. (aiōn g165)
And the world passes away, and the lust of it, but he who does the will of God abides into the age. (aiōn g165)
18 ’Ya’yana ƙaunatattu, waɗannan su ne kwanakin ƙarshe; kuma kamar yadda kuka ji cewa magabcin Kiristi yana zuwa, ko yanzu ma abokan gāban Kiristi da yawa sun zo. Ta haka muka san cewa kwanakin ƙarshe sun iso.
Children, it is the last hour. And as ye heard that the antichrist comes, and now many antichrists have developed, from which we know that it is the last hour.
19 Waɗannan masu gāba da Kiristi suna cikinmu a dā, amma sun bar mu, don tun dā ma su ba namu ba ne. Ai, da su namu ne, da har yanzu suna tare da mu. Amma sun bar mu, wannan ya nuna a fili cewa su ba namu ba ne.
They went out from us, but they were not of us. For if they were of us, they would have continued with us, but-so that they might be made known, that they are not all of us.
20 Amma ku kam, kuna da shafewa daga wurin Mai Tsarkin nan, kuma dukanku kun san gaskiya.
And ye have an anointing from the Holy, and ye know all the things.
21 Ina rubuta muku ba domin ba ku san gaskiya ba ne, a’a, sai dai domin kun santa, kun kuma san cewa babu yadda ƙarya za tă fito daga gaskiya.
I wrote to you not because ye know not the truth, but because ye know it, and because no lie is of the truth.
22 Wane ne maƙaryaci? Ai, shi ne mutumin da yake mūsun cewa Yesu shi ne Kiristi. Irin wannan mutum shi ne magabcin Kiristi, ya yi mūsun Uban da kuma Ɗan.
Who is the liar if not he who denies that Jesus is the Christ? This is the antichrist, he who denies the Father and the Son.
23 Ba wanda yake mūsun Ɗan, sa’an nan yă ce yana da Uban; duk wanda ya yarda da Ɗan, yana da Uban a cikinsa ke nan.
Every man who denies the Son, also does not have the Father.
24 Ku lura fa cewa abin da kuka ji daga farko, bari yă ci gaba da kasance a cikinku. In kuwa ya ci gaba da zama a cikinku, za ku kasance a cikin Ɗan, da kuma a cikin Uban.
Therefore ye, let what ye heard from the beginning abide in you. If what ye heard from the beginning abides in you, ye also will abide in the Son and in the Father.
25 Wannan shi ne abin da ya yi mana alkawari, wato, rai madawwami. (aiōnios g166)
And this is the promise that he promised us: the eternal life. (aiōnios g166)
26 Ina rubuta muku waɗannan abubuwa ne game da waɗanda suke ƙoƙari su sa ku kauce.
I wrote these things to you concerning those who lead you astray.
27 Game da ku kuwa, shafan nan da kuka karɓa daga gare shi tana nan a cikinku, ba kwa kuma bukata wani yă koyar da ku. Amma kamar yadda shafan nan tasa tana koya muku kome, ita kuwa gaskiya ce ba ƙarya ba, yadda dai ta koya muku, to, sai ku zauna a cikinsa.
And for you, the anointing that ye received from him abides in you, and ye have no need that any man teach you, but as the same anointing teaches you about all things, and is true and is no lie, and just as it taught you, ye will abide in him.
28 Yanzu fa, ya ku’ya’yana ƙaunatattu, sai ku ci gaba a cikinsa, domin sa’ad da ya bayyana, mu iya tsaya gabagadi babu kunya a dawowarsa.
And now, little children, abide in him, so that when he is made known, we may have confidence, and not be shamed by him at his coming.
29 In kun san cewa shi mai adalci ne, to, kun dai san cewa duk mai aikata abin da yake daidai haifaffensa ne.
If ye know that he is righteous, know ye that every man doing righteousness has been begotten of him.

< 1 Yohanna 2 >