< 1 Korintiyawa 15 >
1 To,’yan’uwa, ina so in tuna muku da bisharar da na yi muku wa’azinta, wadda kuka karɓa, wadda kuma kuka yanke shawara ku tsaya a kai.
Now I make known unto you brethren, the gospel which I preached unto you, which also ye received, wherein also ye stand,
2 Ta wurin wannan bisharar ce kuka sami ceto, muddin kuna riƙe da wa’azin da na yi muku kam-kam. In ba haka ba, kun gaskata a banza ke nan.
by which also ye are saved; [I make known, I say], in what words I preached it unto you, if ye hold it fast, except ye believed in vain.
3 Gama abu farko mafi muhimmancin da na karɓo shi ne na ba ku cewa Kiristi ya mutu domin zunubanmu bisa ga Nassi,
For I delivered unto you first of all that which also I received, how that Christ died for our sins according to the scriptures;
4 cewa an binne shi an kuma tashe shi a rana ta uku bisa ga Nassi,
and that he was buried; and that he hath been raised on the third day according to the scriptures;
5 cewa ya bayyana ga Bitrus, sa’an nan ga Sha Biyun.
and that he appeared to Cephas; then to the twelve;
6 Bayan haka, ya bayyana ga fiye da ɗari biyar daga cikin’yan’uwa a lokaci guda. Yawancinsu kuwa suna nan da rai, ko da yake waɗansu sun riga sun yi barci.
then he appeared to above five hundred brethren at once, of whom the greater part remain until now, but some are fallen asleep;
7 Sa’an nan ya bayyana ga Yaƙub, sa’an nan ga dukan manzannin,
then he appeared to James; then to all the apostles;
8 a ƙarshe duka, ya bayyana a gare ni, kamar wanda an haifa a lokacin da bai kamata ba.
and last of all, as unto one born out of due time, he appeared to me also.
9 Gama ni ne mafi ƙanƙanta a cikin manzanni, ban kuma isa a kira ni manzo ba, domin na tsananta wa ikkilisiyar Allah.
For I am the least of the apostles, that am not meet to be called an apostle, because I persecuted the church of God.
10 Amma bisa ga alherin Allah, na zama abin da nake, alherinsa zuwa gare ni kuwa bai zama a banza ba. A’a, na yi aiki fiye da dukansu, duk da haka, ba ni ba ne, sai dai alherin Allah da yake tare da ni ne.
But by the grace of God I am what I am: and his grace which was bestowed upon me was not found vain; but I laboured more abundantly than they all: yet not I, but the grace of God which was with me.
11 To, ko ni ne, ko su ne, wannan shi ne abin da muke wa’azi, shi ne kuma abin da kuka gaskata.
Whether then [it be] I or they, so we preach, and so ye believed.
12 Amma in ana wa’azi cewa Kiristi ya tashi daga matattu, yaya waɗansu a cikinku suke cewa babu tashin matattu?
Now if Christ is preached that he hath been raised from the dead, how say some among you that there is no resurrection of the dead?
13 In babu tashin matattu, to, ba a tā da Kiristi ma ba ke nan.
But if there is no resurrection of the dead, neither hath Christ been raised:
14 In ba a tashe Kiristi ba kuwa, ai, wa’azinmu, da bangaskiyarku banza ne.
and if Christ hath not been raised, then is our preaching vain, your faith also is vain.
15 Sai ma ya zama mun zama masu ba da shaidar ƙarya game da Allah ke nan, domin mun shaida game da Allah cewa ya tashe Kiristi daga matattu. Bai tashe Kiristi ba ke nan, in lalle ba a tā da matattu.
Yea, and we are found false witnesses of God; because we witnessed of God that he raised up Christ: whom he raised not up, if so be that the dead are not raised.
16 Gama in ba a tā da matattu ba, to, Kiristi ma ba a tashe shi ba ke nan.
For if the dead are not raised, neither hath Christ been raised:
17 In kuwa ba a tashe Kiristi ba, bangaskiyarku a banza take, ya zama har yanzu kuna cikin zunubanku ke nan.
and if Christ hath not been raised, your faith is vain; ye are yet in your sins.
18 Ashe, waɗanda suka yi barci a cikin Kiristi ma sun hallaka ke nan.
Then they also which are fallen asleep in Christ have perished.
19 In a wannan rayuwar ce kaɗai muke da bege cikin Kiristi, mun zama abin tausayi fiye da dukan mutane.
If in this life only we have hoped in Christ, we are of all men most pitiable.
20 Amma tabbatacce, an tā da Kiristi daga matattu, nunan fari kuwa cikin waɗanda suka yi barci.
But now hath Christ been raised from the dead, the firstfruits of them that are asleep.
21 Da yake mutuwa ta zo ta wurin mutum, haka tashin matattu ma ya zo ta wurin mutum.
For since by man [came] death, by man [came] also the resurrection of the dead.
22 Kamar yadda duka suka mutu cikin Adamu, haka duka za su rayu cikin Kiristi.
For as in Adam all die, so also in Christ shall all be made alive.
23 Sai dai kowa da lokacinsa. Kiristi ne nunan fari; sa’an nan sa’ad da ya dawo; za a tā da waɗanda suke nasa.
But each in his own order: Christ the firstfruits; then they that are Christ’s, at his coming.
24 Sa’an nan sai ƙarshen ta zo, sa’ad da zai miƙa wa Allah Uba mulki, bayan ya hallaka dukan sarauta, mulki da iko.
Then [cometh] the end, when he shall deliver up the kingdom to God, even the Father; when he shall have abolished all rule and all authority and power.
25 Gama dole yă yi mulki har sai ya sa dukan abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
For he must reign, till he hath put all his enemies under his feet.
26 Abokin gāba na ƙarshen da za a hallaka kuwa, shi ne mutuwa.
The last enemy that shall be abolished is death.
27 Gama ya “sa kome a ƙarƙashin ƙafafunsa.” To, da aka ce an sa “kome” a ƙarƙashinsa, a fili yake cewa ba a haɗa da Allah a ciki ba, shi wannan da ya sa kome a ƙarƙashin Kiristi.
For, He put all things in subjection under his feet. But when he saith, All things are put in subjection, it is evident that he is excepted who did subject all things unto him.
28 Sa’ad da ya yi haka, sa’an nan Ɗan kansa yă koma a ƙarƙashin shi wanda ya sa kome a ƙarƙashinsa, domin Allah yă zama kome da kome.
And when all things have been subjected unto him, then shall the Son also himself be subjected to him that did subject all things unto him, that God may be all in all.
29 To, in babu tashin matattu, mene ne waɗanda ake musu baftisma saboda matattu za su yi? In ba a tā da matattu sam, me ya sa ake yin wa mutane baftisma saboda su?
Else what shall they do which are baptized for the dead? If the dead are not raised at all, why then are they baptized for them?
30 Mu ma don me muke sa kanmu cikin hatsari a kowace sa’a?
Why do we also stand in jeopardy every hour?
31 Ina fuskantar mutuwa kowace rana. I, kamar yadda yake tabbatacce cewa ina taƙama da ku cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu.
I protest by that glorying in you, brethren, which I have in Christ Jesus our Lord, I die daily.
32 In na yi kokawa da mugayen namomin jeji a Afisa bisa ga ra’ayin mutane ne kawai, mece ce ribata, in har ba a tā da matattu? Ai, “Sai mu ci mu sha, da yake gobe za mu mutu.”
If after the manner of men I fought with beasts at Ephesus, what doth it profit me? If the dead are not raised, let us eat and drink, for tomorrow we die.
33 Kada fa a ruɗe ku, “Ajiyar mugayen abokai yana ɓata hali mai kyau.”
Be not deceived: Evil company doth corrupt good manners.
34 Ku koma cikin hankalinku yadda ya kamata, ku kuma daina yin zunubi, gama akwai waɗansu da ba su san Allah ba, na faɗi wannan ne don ku kunyata.
Awake up righteously, and sin not; for some have no knowledge of God: I speak [this] to move you to shame.
35 Amma wani yana iya tambaya yă ce, “Ta yaya ake tā da matattun? Da wane irin jiki za su tashi?”
But some one will say, How are the dead raised? and with what manner of body do they come?
36 Kai, marar azanci! Abin da kuka shuka ba zai tsira ba sai ya mutu.
Thou foolish one, that which thou thyself sowest is not quickened, except it die:
37 Sa’ad da kuke shuki, ba tsiron da zai yi girma ba ne kuka shuka, ƙwayar ce kawai, ko ta alkama ko kuma na wani irin dabam.
and that which thou sowest, thou sowest not the body that shall be, but a bare grain, it may chance of wheat, or of some other kind;
38 Amma Allah yakan ba ƙwayar jiki yadda ya yi niyya, kuma ga kowane irin ƙwaya yakan ba ta irin jikinta.
but God giveth it a body even as it pleased him, and to each seed a body of its own.
39 Ba dukan nama ne iri ɗaya ba. Mutane da irin nasu, dabbobi da irin nasu, tsuntsaye da irin nasu, kifaye kuma da irin nasu.
All flesh is not the same flesh: but there is one [flesh] of men, and another flesh of beasts, and another flesh of birds, and another of fishes.
40 Akwai jikuna iri na samaniya, akwai kuma jikuna iri na duniya; sai dai darajar jikunan samaniya dabam take, darajar jikunan duniya kuma dabam take.
There are also celestial bodies, and bodies terrestrial: but the glory of the celestial is one, and the [glory] of the terrestrial is another.
41 Rana tana da wata irin daraja, wata yana da wata darajar dabam, taurari kuma suna da tasu dabam. Wani tauraro kuwa yakan bambanta da wani a wajen daraja.
There is one glory of the sun, and another glory of the moon, and another glory of the stars; for one star differeth from another star in glory.
42 Haka ne tashin matattu zai kasance. Abin da aka shuka yakan ruɓe, abin da aka tā da shi kuma ba ya ruɓewa;
So also is the resurrection of the dead. It is sown in corruption; it is raised in incorruption:
43 akan shuka shi cikin ƙasƙanci, a kuma tā da shi cikin ɗaukaka, akan shuka shi da rashin ƙarfi, a kuma tā da shi da ƙarfi;
it is sown in dishonour; it is raised in glory: it is sown in weakness; it is raised in power:
44 akan shuka shi da jiki na mutuntaka, a kuma tā da shi da jikin ruhaniya. In akwai jiki na mutuntaka, to, lalle akwai jikin ruhaniya ma.
it is sown a natural body; it is raised a spiritual body. If there is a natural body, there is also a spiritual [body].
45 Haka yake a rubuce cewa, “Adamu, mutumin farko ya zama mai rai”; Adamu na ƙarshe kuwa ruhu ne mai ba da rai.
So also it is written, The first man Adam became a living soul. The last Adam [became] a life-giving spirit.
46 Ba jikin ruhaniya ne ya zo da farko ba, na mutuntakan ne, daga baya kuma sai na ruhaniya.
Howbeit that is not first which is spiritual, but that which is natural; then that which is spiritual.
47 Mutumin farko daga turɓaya ce ya fito, mutum na biyu kuwa daga sama ne ya fito.
The first man is of the earth, earthy: the second man is of heaven.
48 Kamar yadda mutumin turɓaya yake, haka ma waɗanda suke na turɓaya. Kuma kamar yadda mutumin sama yake, haka ma waɗanda suke na sama.
As is the earthy, such are they also that are earthy: and as is the heavenly, such are they also that are heavenly.
49 Kamar dai yadda muka ɗauki siffar mutumin turɓaya, haka kuma za mu ɗauki siffar mutumin sama.
And as we have borne the image of the earthy, we shall also bear the image of the heavenly.
50 Ina sanar da ku,’yan’uwa, cewa nama da jini ba za su gāji mulkin Allah ba, haka ma ruɓa ba zai gāji rashin ruɓa ba.
Now this I say, brethren, that flesh and blood cannot inherit the kingdom of God; neither doth corruption inherit incorruption.
51 Ku saurara, in gaya muku wani asiri. Ba dukanmu ne za mu yi barci ba, sai dai duk za a sauya kamanninmu
Behold, I tell you a mystery: We shall not all sleep, but we shall all be changed,
52 farat ɗaya, cikin ƙyaftawar ido, da busan ƙaho na ƙarshe. Gama za a busa ƙaho, za a tā da matattu da jiki irin da ba ya ruɓewa, za a kuma sauya kamanninmu.
in a moment, in the twinkling of an eye, at the last trump: for the trumpet shall sound, and the dead shall be raised incorruptible, and we shall be changed.
53 Gama dole mai ruɓa yă maye wa mai ruɓan nan, marar mutuwa kuma yă maye wa mai mutuwan nan.
For this corruptible must put on incorruption, and this mortal must put on immortality.
54 Sa’ad da mai ruɓan nan ya maye marar ruɓan nan, mai mutuwa kuma ya maye marar mutuwan nan, sa’an nan ne karin maganar da yake a rubuce zai zama gaskiya cewa, “An haɗiye mutuwa cikin nasara.”
But when this corruptible shall have put on incorruption, and this mortal shall have put on immortality, then shall come to pass the saying that is written, Death is swallowed up in victory.
55 “Ya ke mutuwa, ina nasararki? Ya ke mutuwa, ina dafinki?” (Hadēs )
O death, where is thy victory? O death, where is thy sting? (Hadēs )
56 Zunubi ne yake ba wa mutuwa dafi, Doka kuma take ba wa zunubi iko.
The sting of death is sin; and the power of sin is the law:
57 Amma godiya ga Allah! Shi ne ya ba mu nasara ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi.
but thanks be to God, which giveth us the victory through our Lord Jesus Christ.
58 Saboda haka, ƙaunatattu’yan’uwana, ku tsaya da daram. Kada wani abu yă jijjiga ku. Ku ba da kanku kullum ga aikin Ubangiji, domin kun san cewa famar da kuke yi saboda Ubangiji ba a banza take ba.
Wherefore, my beloved brethren, be ye stedfast, unmoveable, always abounding in the work of the Lord, forasmuch as ye know that your labour is not vain in the Lord.