< 1 Tarihi 5 >
1 ’Ya’yan Ruben maza ɗan farin Isra’ila (shi ne ɗan fari, amma sa’ad da ya ƙazantar da gadon auren mahaifinsa, sai aka ba wa’yancin ɗan farinsa wa’ya’yan Yusuf maza ɗan Isra’ila; don kada a lissafta shi a tarihin zuriya bisa ga matsayin haihuwarsa,
Also the sones of Ruben, the firste gendrid sone of Israel; for he was the first gendrid sone of Israel, but whanne he hadde defoulid the bed of his fadir, the dignitye of his firste gendryng was youun to the sones of Joseph, the sone of Israel; and Ruben was not arettid in to the firste gendrid sone.
2 ko da yake Yahuda shi ne mafi ƙarfi cikin’yan’uwansa kuma mai mulki ya fito daga gare shi,’yancin zaman ɗan fari na Yusuf ne),
Forsothe Judas, that was the strongeste among hise britheren, prynces weren gaderid of his generacioun; forsothe the `riyt of firste gendryng was arettid to Joseph.
3 ’ya’yan Ruben ɗan farin Isra’ila maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
Therfor the sones of Ruben, the firste gendrid sone of Israel, weren Enoch, and Phallu, Esrom, and Charmy.
4 Zuriyar Yowel su ne, Shemahiya, Gog, Shimeyi,
The sones of Johel weren Samaie; his sone, Gog; his sone, Semey;
his sone, Mycha; his sone, Rema; his sone, Baal;
6 da Beyera, wanda Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya ɗauka zuwa zaman bauta. Beyera shi ne shugaban mutanen Ruben.
his sone, Bera; whom Theglatphalassar, kyng of Assyriens, ledde prisoner; and he was prince in the lynage of Ruben.
7 Danginsu bisa ga iyalansu da aka jera bisa ga tarihin zuriyarsu su ne, Yehiyel shi ne sarki, akwai Zakariya,
Sotheli hise britheren, and al the kynrede, whanne thei weren noumbrid bi her meynees, hadden princes Jehiel, and Zacharie.
8 da Bela ɗan Azaz. Azaz ɗan Shema daga dangin Yowel. Yowel ya yi zama a yankin Arower har zuwa Nebo da Ba’al-Meyon.
Forsothe Bala, the sone of Achaz, sone of Sama, sone of Johel, he dwellide in Aroer til to Nebo and Beelmoon;
9 Ta waje gabas sun zauna a ƙasar har zuwa bakin hamadan da ya nausa zuwa Kogin Yuferites, domin dabbobinsu sun ƙaru a Gileyad.
and he dwellide ayens the eest coost, til to the ende of deseert, `and to the flood Eufrates. And he hadde in possessioun myche noumbre of beestis in the lond of Galaad.
10 A zamanin Shawulu zuriyar Ruben sun yi yaƙi da Hagirawa, suka ci su da yaƙi, suka zauna a wuraren zaman Hagirawan ko’ina a dukan yankin gabashin Gileyad.
Forsothe in the daies of Saul the sones of Ruben fouyten ayens Agarenus, and killide hem; and dwelliden for hem in the tabernaclis of hem, in al the coost that biholdith to the eest of Galaad.
11 Mutanen Gad sun zauna kusa da mutanen Ruben a Bashan, har zuwa Saleka.
Sotheli the sones of Gad euene ayens hem dwelliden in the lond of Basan til to Selca;
12 Yowel shi ne babba, sai Shafan na biyu, sa’an nan Yanai da Shafat, su ne tushen Bashan.
Johel was in the bygynnyng, and Saphan was the secounde; also Janahi and Saphan weren in Basan.
13 Danginsu, bisa ga iyalai su ne, Mika’ilu, Meshullam, Sheba, Yorai, Yakan, Ziya da Eber, su bakwai ne duka.
Also her britheren bi the housis of her kynredis, Mychael, and Mosollam, and Sebe, and Jore, and Jachan, and Zie, and Heber, seuene.
14 Waɗannan su ne’ya’yan Abihayil ɗan Huri, ɗan Yarowa, ɗan Gileyad, ɗan Mika’ilu, ɗan Yeshishai, ɗan Yado, ɗan Buz.
These weren the sones of Abiahel, the sone of Vry, sone of Jaro, sone of Galaad, sone of Mychael, sone of Esesi, sone of Jeddo, sone of Buz.
15 Ahi ɗan Abiyel, ɗan Guni, shi ne kan iyalinsu.
Also the britheren of the sone of Abdiel, sone of Gumy, was prince of the hows in hise meynees.
16 Mutanen Gad sun zauna a Bashan da ƙauyukan da suke kurkusa da shi, da kuma a dukan makiyayan Sharon har zuwa iyaka inda suka kai.
And thei dwelliden in Galaad, and in Basan, and in the townes therof, in alle the subarbis of Arnon, til to the endis.
17 Dukan waɗannan sun shiga tarihin zuriya a lokacin mulkin Yotam sarkin Yahuda da Yerobowam sarkin Isra’ila.
Alle these weren noumbrid in the daies of Joathan, kyng of Juda, and in the daies of Jeroboam, kyng of Israel.
18 Mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse sun kasance da mutane 44,760 shiryayyu don aikin soja, jarumawan da za su iya riƙe garkuwa da takobi, waɗanda suke iya yin amfani da baka, waɗanda kuma aka horar don yaƙi.
The sones of Ruben, and of Gad, and of half the lynage of Manasses, weren men werriours, berynge scheeldis and swerdis, and beendynge bouwe, and tauyt to batels, foure and fourti thousynde seuene hundrid and sixti,
19 Suka yi yaƙi da Hagirawa, Yetur, Nafish da Nodab.
and thei yeden forth to batel, and fouyten ayens Agarenus. Forsothe Ethureis, and Napheis,
20 Aka taimake su a yaƙin, Allah kuma ya ba da Hagirawa da dukan abokansu gare su, domin sun yi kuka gare shi a lokacin yaƙin. Ya amsa addu’o’insu, domin sun dogara gare shi.
and Nadab, yauen help to hem; and Agarenus, and alle men that weren with hem, weren bitakun in to the hondis of Ruben, and Gad, and Manasses; for thei clepiden inwardli the Lord, while thei fouyten, and the Lord herde hem, for thei `hadden bileuyd in to him.
21 Suka ƙwace dabbobin Hagirawa, raƙuma dubu hamsin, tumaki dubu ɗari biyu da hamsin da kuma jakuna dubu biyu. Suka kuma kame mutane dubu ɗari ɗaya,
And thei token alle thingis whiche Agarenus hadden in possessioun, fifti thousynde of camels, and twei hundrid and fifty thousynde of scheep, twei thousynde of assis, and an hundrid thousynde persoones of men;
22 waɗansu suka mutu, domin yaƙin na Allah ne. Suka zauna a ƙasar har lokacin da aka kai su zaman bauta.
for many men weren woundid and felden doun; for it was the batel of the Lord. And thei dwelliden for Agarenus til to the conquest.
23 Mutanen rabin kabilar Manasse sun yi yawa; suka zauna a ƙasar daga Bashan har zuwa Ba’al-Hermon, wato, zuwa Senir (Dutsen Hermon).
Also the sones of the half lynage of Manasses hadden in possessioun the lond, fro the endis of Basan til to Baal Hermon, and Sanyr, and the hil of Hermon; for it was a greet noumbre.
24 Waɗannan su ne kawunan iyalansu. Efer, Ishi, Eliyel, Azriyel, Irmiya, Hodawiya da Yadiyel. Su jarumawa ne, sanannu, su ne kuma kawunan iyalansu.
And these weren the princes of the hows of her kynrede; Epher, and Jesi, and Heliel, and Esryel, and Jeremye, and Odoie, and Jedihel, strongeste men and myyti, and nemyd duykis in her meynees.
25 Amma ba su yi aminci da Allahn kakanninsu ba, suka kuma yi karuwanci ga waɗansu allolin mutanen ƙasar, waɗanda Allah ya hallaka a gabansu.
Forsothe thei forsoken the God of her fadris, and diden fornycacioun after the goddis of puplis of the lond, whiche the Lord took awei bifor hem.
26 Saboda haka Allah na Isra’ila ya zuga ruhun Ful sarkin Assuriya (wato, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya), wanda ya kwashe mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse zuwa zaman bauta. Ya kwashe su zuwa Hala, Habor, Hara da kuma kogin Gozan, inda suke har wa yau.
And the Lord God of Israel reiside the spirit of Phul, kyng of Assiriens, and the spirit of Theglatphalasser, kyng of Assur; and he translatide Ruben, and Gad, and the half lynage of Manasses, and brouyte hem in to Ale, and Abor, and Aram, and in to the ryuer of Gozam, til to this dai.