< 1 Sarakuna 12 >

1 Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra’ila sun je can don su naɗa shi sarki.
Forsothe Roboam cam in to Sichem; for al Israel was gaderid thidur to make hym kyng.
2 Sa’ad da Yerobowam ɗan Nebat ya ji labari (gama har yanzu yana a Masar, inda ya gudu daga Sarki Solomon), sai ya dawo daga Masar.
`And sotheli Jeroboam, sone of Nabath, whanne he was yit in Egipt, and fledde fro the face of kyng Salomon, turnede ayen fro Egipt, for the deeth of Salomon was herd;
3 Saboda haka mutane suka aika Yerobowam yă zo, sai shi da dukan taron Isra’ila suka tafi wurin Rehobowam, suka ce masa,
and thei senten, and clepiden hym. Therfor Jeroboam cam, and al the multitude of Israel, and thei spaken to Roboam,
4 “Mahaifinka ya sa mana kaya mai nauyin gaske, amma yanzu ka sassauta wannan aiki mai zafi, da kuma kaya masu nauyin da ya sa a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
and seiden, Thi fadir puttide hardeste yok on vs, therfor abate thou a litil now of the hardest comaundement of thi fadir, and of the greuousiste yok which he puttide on vs, and we schulen serue to thee.
5 Rehobowam ya amsa, “Ku tafi, bayan kwana uku, ku dawo.” Sai mutane suka watse.
Which Roboam seide to hem, Go ye `til to the thridde dai, and turne ye ayen to me.
6 Sai Sarki Rehobowam ya nemi shawarar dattawa waɗanda suka yi wa mahaifinsa Solomon, hidima a kwanakinsa. Ya ce, “Wace shawara ce za ku ba ni don in amsa wa waɗannan mutane?”
And whanne the puple hadde go, kyng Roboam took counsel with the eldere men, that stoden bifor Salomon, his fadir, while he lyuyde yit; and Roboam seide, What counsel yyue ye to me, that Y answere to the puple?
7 Suka amsa, “In a yau za ka zama bawan waɗannan mutane, ka kuma yi musu hidima, ka ba su amsa mai kyau, kullum za su kasance bayinka.”
Whiche seiden to hym, If thou obeiest to dai to this puple, and seruest this puple, and yyuest stide to her axyng, and spekist to hem liyte wordis, thei schulen be seruauntis to thee in alle daies.
8 Amma Rehobowam ya ƙi shawarar da dattawan suka ba shi, sai ya nemi shawarar matasa waɗanda suka yi girma tare, waɗanda kuma suke masa hidima.
Which Roboam forsook the counsel of elde men, which thei yauen to hym, and took yonge men, that weren nurschid with hym, and stoden nyy him;
9 Ya tambaye su, “Mece ce shawararku? Yaya za mu amsa wa waɗannan mutane masu cewa, ‘Ka sassauta nauyin da mahaifinka ya sa a kanmu’?”
and he seide to hem, What counsel yyue ye to me, that Y answere to this puple, that seiden to me, Make thou esyere the yok which thi fadir puttide on vs?
10 Matasan, waɗanda suka yi girma tare da shi, suka amsa, “Faɗa wa waɗannan mutanen da suka ce maka, ‘Mahaifinka ya sa kaya masu nauyi a kanmu, amma ka sassauta kayanka.’ Ka ce musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun tsohona kauri.
And the yonge men, that weren nurschid with hym, seiden to hym, Thus speke thou to this puple, that spaken to thee, and seiden, Thi fadir made greuouse oure yok, releeue thou vs; thus thou schalt speke to hem, My leest fyngur is grettere than the bak of my fader;
11 Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.’”
and now my fadir puttide on you a greuouse yok, forsothe Y schal adde on youre yok; my fadir beet you with scourgis, forsothe Y schal bete you with scorpiouns.
12 Bayan kwana uku, Yerobowam da dukan mutane suka dawo wurin Rehobowam yadda sarki ya faɗa, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.”
Therfor Jeroboam, and al the puple, cam to Roboam, in the thridde dai, as the kyng spak, seiynge, Turne ye ayen to me in the thridde dai.
13 Sai Sarki ya amsa wa mutane da zafi. Yana ƙin shawarar da dattawa suka ba shi.
And the kyng answeride harde thingis to the puple, while the counsel of eldere men was forsakun, which thei hadden youe to hym;
14 Ya bi shawarar matasa, ya ce, “Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.”
and he spak to hem bi the counsel of yonge men, and seide, My fadir made greuouse youre yok, forsothe Y schal adde to youre yok; my fadir beet you with scourgis, forsothe Y schal bete you with scorpiouns.
15 Saboda haka sarki bai saurare mutane ba, gama wannan abin da ya faru daga wurin Ubangiji ne, don a cika maganar Ubangiji da ya yi wa Yerobowam ɗan Nebat ta wurin Ahiya, mutumin Shilo.
And the kyng assentide not to the puple, for the Lord hadde turned awey, `ether hadde wlatid hym, that the Lord schulde reise his word, which he hadde spoke in the hond of Ahias of Silo to Jeroboam, sone of Nabath.
16 Da dukan Isra’ila suka ga sarki ya ƙi yă saurare su, sai suka amsa wa sarki, “Ina ruwanmu da Dawuda! Ai! Ba mu da gādo wurin ɗan Yesse. Ya Isra’ila, kowa yă koma tentinsa! Dawuda, sai ka lura da gidanka!” Saboda haka Isra’ilawa suka watse zuwa gida.
Therfor the puple siy, that the kyng nolde here hem; and the puple answeride to the kyng, and seide, What part is to vs in Dauid, ether what eritage in the sone of Ysay? Israel, turne thou ayen in to thi tabernaclis; now, Dauid, se thou thin hows. And Israel yede in to hise tabernaclis.
17 Amma ga Isra’ilawan da suke zama a garuruwan Yahuda kuwa, Rehobowam ya ci gaba da mulki a kansu.
Forsothe Roboam regnede on the sones of Israel, whiche euere dwelliden in the citees of Juda.
18 Sarki Rehobowam ya aiki Adoniram wanda yake shugaban aikin gandu, amma Isra’ila suka jajjefe shi da dutse har ya mutu. Sarki Rehobowam, ya sullale ya hau keken yaƙinsa ya tsere zuwa Urushalima.
Therfore kyng Roboam sente Adhuram, that was on the tributis; and al the puple of Israel stonyde hym, and he was deed.
19 Tun daga wannan ranar ne mutanen Isra’ila suka shiga gāba da gidan Dawuda har wa yau.
Forsothe kyng Roboam stiede hastili on the chare, and fledde in to Jerusalem; and Israel departide fro the hows of Dauid, til in to present dai.
20 Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ji Yerobowam ya dawo, sai suka aika, suka kira shi zuwa taro, suka kuma naɗa shi sarki bisa dukan Isra’ila. Kabila Yahuda kaɗai ta kasance mai biyayya ga gidan Dawuda.
Forsothe it was doon, whanne al Israel hadde herd that Jeroboam turnede ayen, thei senten, and clepiden hym, whanne the cumpany was gaderid togidere, and thei maden hym kyng on al Israel; and no man suede the hows of Dauid, outakun the lynage aloone of Juda.
21 Da Rehobowam ya isa Urushalima, ya tattara dukan gidan Yahuda da kabilar Benyamin, ya sami sun kai mayaƙa dubu da tamanin. Sai aka shirya don su yaƙi gidan Isra’ila, su kuma mayar da masarautar wa Rehobowam ɗan Solomon.
Forsothe Roboam cam to Jerusalem, and gaderide al the hows of Juda, and the lynage of Beniamyn, an hundrid and fourescore thousynde of chosun men and weriours, that thei schulden fiyte ayens the hows of Israel, and schulden brynge ayen the rewme to Roboam, sone of Solomon.
22 Amma waɗannan kalmomin Allah suka zo wa Shemahiya, mutumin Allah, cewa,
Forsothe the word of God was made to Semeia, the man of God, and seide,
23 “Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon, sarkin Yahuda, ka faɗa wa dukan gidan Yahuda da Benyamin, da kuma dukan sauran mutane,
Speke thou to Roboam, sone of Salomon, the kyng of Juda, and to al the hows of Juda and of Beniamyn, and to the residue of the puple, and seie thou, The Lord seith thes thingis,
24 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku, Isra’ilawa. Ku koma gida, kowannenku, gama wannan aikina ne.”’” Saboda haka suka yi biyayya da maganar Ubangiji, suka sāke watse zuwa gida, yadda Ubangiji ya umarta.
Ye schulen not stie, nether ye schulen fiyte ayens youre britheren, the sones of Israel; `a man turne ayen in to his hows, for this word is doon of me. Thei herden the word of the Lord, and thei turneden ayen fro the iurney, as the Lord comaundide to hem.
25 Sai Yerobowam ya ƙara gina Shekem a ƙasar tudu ta Efraim, ya zauna a can. Daga can ya tafi ya gina Fenuwel.
Forsothe Jeroboam bildide Sichem, in the hil of Effraym, and dwellide there; and he yede out fro thennus, and bildide Phanuel.
26 Yerobowam ya yi tunani a ransa ya ce, “Mai yiwuwa mulkin yă koma gidan Dawuda.
And Jeroboam seide in his herte, Now the rewme schal turne ayen to the hows of Dauid,
27 In waɗannan mutane sun riƙa haurawa don su miƙa hadayu a haikalin Ubangiji a Urushalima. Za su sāke nuna biyayya ga mai girma, Rehobowam, sarkin Yahuda. Za su kashe ni su kuma koma ga Sarki Rehobowam.”
if this puple stieth to Jerusalem, that it make sacrifices in the hows of the Lord in Jerusalem; and the herte of this puple schal turne to her lord, Roboam, kyng of Juda; and thei schulen sle me, and schulen turne ayen to hym.
28 Bayan ya nemi shawara, sai sarki ya yi siffofin’yan maruƙa biyu na zinariya. Ya ce wa mutane, “Kun daɗe kuna haurawa zuwa can Urushalima. Ga allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga ƙasar Masar.”
And by counsel thouyt out, he made tweyne goldun caluys, and seide to hem, Nyle ye stie more in to Jerusalem; Israel, lo! thi goddis, that ledden thee out of the lond of Egipt.
29 Sai ya kafa ɗaya a Betel, ɗaya kuma a Dan.
And he settide oon in Bethel, and the tother in Dan.
30 Wannan ya zama zunubi, gama mutane suna tafiya yin wa wannan da yake a Betel sujada, su kuma je har Dan don su yi wa ɗayan sujada.
And this word was maad to Israel in to synne; for the puple yede til in to Dan, to worschipe the calf.
31 Yerobowam ya gina masujadai da suke kan tuddai, ya kuma naɗa firistoci barkatai daga cikin mutanen da ba na zuriyar Lawi ba.
And Jeroboam made templis in hiye placis, and `he made preestis of the laste men of the puple, that weren not of the sones of Leuy.
32 Ya kafa biki a rana ta goma sha biyar ta watan takwas, kamar bikin da ake yi a Yahuda, ya kuma miƙa hadayu a bisa bagade. Ya yi haka a Betel, yana miƙa wa siffofin maruƙan da ya yi hadayu. A Betel kuma ya naɗa firistoci a wuraren tudun da ya yi.
And he ordeynede a solempne dai in the eiythe monethe, in the fiftenthe dai of the monethe, bi the licnesse of solempnyte which was halewid in Juda. And he stiede, and made in lijk maner an auter in Bethel, that he schulde offre to the calues, whiche he hadde maad; and he ordeynede in Bethel preestis of the hiye places, whiche he hadde maad.
33 A rana ta goma sha biyar ta watan takwas, watan da ya zaɓa, ya miƙa hadayu a bisa bagaden da ya gina a Betel. Saboda haka ya kafa biki don Isra’ilawa, ya kuma haura zuwa bagade don yă miƙa hadayu.
And he styede on the auter, which he hadde bildid in Bethel, in the fiftenthe day of the eiythe monethe, which he hadde feyned of his herte; and he made solempnyte to the sones of Israel, and he stiede on the auter, that he schulde brenne encence.

< 1 Sarakuna 12 >