< 1 Tarihi 22 >

1 Sai Dawuda ya ce, “Gidan Ubangiji Allah zai kasance a nan, haka kuma bagaden hadaya ta ƙonawa don Isra’ila.”
Et David dit: C’est ici la maison de l’Éternel Dieu, et c’est ici l’autel pour l’holocauste d’Israël.
2 Dawuda kuwa ya umarta a tattara baƙin da suke zama a Isra’ila, daga cikinsu ya sa masu farfasa duwatsu don su shirya duwatsun da aka sassaƙa saboda ginin gidan Allah.
Et David ordonna de rassembler les étrangers qui étaient dans le pays d’Israël, et il établit des tailleurs de pierres pour tailler des pierres de taille, pour bâtir la maison de Dieu.
3 Ya tanada ƙarfe mai yawa don ƙusoshi saboda ƙyamaren hanyoyin shiga da kuma saboda mahaɗai, da ƙarin tagulla fiye da ƙirge.
Et David prépara du fer en abondance, pour les clous pour les battants des portes et pour les assemblages, et de l’airain en abondance, sans poids,
4 Ya kuma tanada gumaguman al’ul masu yawa fiye da ƙirge, gama Sidoniyawa da mutanen Taya sun kawo su wa Dawuda da yawa.
et des bois de cèdre sans nombre, car les Sidoniens et les Tyriens amenèrent à David des bois de cèdre en abondance.
5 Dawuda ya ce, “Ɗana Solomon matashi ne kuma bai gogu ba, kuma gidan da za a gina wa Ubangiji zai zama mai ƙayatarwa ƙwarai, sananne da kuma mai daraja a idon dukan al’ummai. Saboda haka zan yi shirye-shirye saboda shi.” Sai Dawuda ya yi ɗumbun shirye-shirye kafin mutuwarsa.
Car David dit: Salomon, mon fils, est jeune et délicat, et la maison à bâtir pour l’Éternel doit être très grande en renom et en beauté dans tous les pays; ainsi je préparerai pour elle [ce qu’il faut]: et David le prépara en abondance avant sa mort.
6 Sa’an nan ya kira ɗansa Solomon ya umarce shi yă gina gida domin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Et il appela Salomon, son fils, et lui commanda de bâtir une maison à l’Éternel, le Dieu d’Israël.
7 Dawuda ya ce wa Solomon, “Ɗana, na yi niyya a zuciyata in gina gida saboda Sunan Ubangiji Allahna.
Et David dit à Salomon: Mon fils, j’ai eu à cœur de bâtir une maison pour le nom de l’Éternel, mon Dieu;
8 Amma wannan maganar Ubangiji ta zo mini, ‘Ka zub da jini mai yawa ka kuma yi yaƙe-yaƙe masu yawa. Ba za ka gina gida domin Sunana ba, domin ka zub da jini da yawa a duniya a idona.
mais la parole de l’Éternel vint à moi, disant: Tu as versé beaucoup de sang, et tu as fait de grandes guerres; tu ne bâtiras point une maison à mon nom, car tu as versé beaucoup de sang sur la terre devant moi.
9 Amma za ka haifi ɗa wanda zai zama mutumin salama da kuma hutu, zan kuma ba shi hutu daga dukan abokan gābansa a kowane gefe. Za a kira shi Solomon, zai kuma kawo wa Isra’ila salama da natsuwa a zamanin mulkinsa.
Voici, un fils te naîtra; lui, sera un homme de paix; et je lui donnerai du repos de tous ses ennemis tout à l’entour; car son nom sera Salomon. Et en ses jours je donnerai paix et tranquillité à Israël.
10 Shi ne wanda zai gina gida saboda Sunana. Zai zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa. Zan kafa kujerar sarautarsa a bisa Isra’ila har abada.’
Lui, bâtira une maison à mon nom; et il me sera pour fils, et moi je lui serai pour père; et j’affermirai le trône de son royaume sur Israël pour toujours.
11 “Yanzu, ɗana, Ubangiji ya kasance tare da kai, bari kuma ka yi nasara ka kuma gina gidan Ubangiji Allahnka, kamar yadda ya ce za ka yi.
Maintenant, mon fils, que l’Éternel soit avec toi, et te fasse prospérer; et tu bâtiras la maison de l’Éternel, ton Dieu, selon ce qu’il a prononcé à ton sujet.
12 Bari Ubangiji ya ba ka basira da fahimi sa’ad da ya sa ka shugaba a bisa Isra’ila, saboda ka kiyaye dokar Ubangiji Allahnka.
Seulement, que l’Éternel te donne de la sagesse et de l’intelligence, et qu’il t’établisse sur Israël, et pour garder la loi de l’Éternel, ton Dieu.
13 Ta haka za ka yi nasara in ka mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa saboda Isra’ila. Ka yi ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya.
Alors tu prospéreras, si tu prends garde à pratiquer les statuts et les ordonnances que l’Éternel commanda à Moïse pour Israël. Fortifie-toi, et sois ferme; ne crains point, et ne t’effraie point.
14 “Na sha wahala da yawa don in yi tanadi talentin dubu ɗari na zinariya, talenti miliyon na azurfa, ɗumbun tagulla da ƙarfe da suka wuce ƙirge da katako da dutse saboda haikalin Ubangiji. Za ka iya ƙara su.
Et voici, dans mon affliction, j’ai préparé pour la maison de l’Éternel de l’or, 100 000 talents, et de l’argent, 1 000 milliers de talents, et de l’airain et du fer, sans poids, car il est en abondance; et j’ai préparé du bois et des pierres; et tu y ajouteras.
15 Kana da ma’aikata masu yawa, masu fafarshe duwatsu, masu gini da masu aikin katako, da kuma gwanaye a kowane irin aikin
Et tu as avec toi beaucoup d’ouvriers, des tailleurs de pierres, des maçons, et des charpentiers, et toute espèce d’hommes experts en tout ouvrage;
16 zinariya da azurfa, tagulla da ƙarfe, masu sana’a waɗanda suka wuce ƙirge. Yanzu ka fara aiki, Ubangiji kuma ya kasance tare da kai.”
l’or, l’argent, et l’airain, et le fer, sont sans nombre: lève-toi, et agis, et l’Éternel sera avec toi.
17 Sai Dawuda ya umarta dukan shugabannin Isra’ila su taimake ɗansa Solomon.
Et David commanda à tous les chefs d’Israël d’aider Salomon, son fils, [disant]:
18 Ya ce musu, “Ba Ubangiji Allahnku yana tare da ku ba? Bai kuma ba ku hutu a kowane gefe ba? Gama ya ba da mazaunan ƙasar gare ni, ƙasar kuma ta Ubangiji ce da mutanensa.
L’Éternel, votre Dieu, n’est-il pas avec vous, et ne vous a-t-il pas donné du repos tout à l’entour? Car il a livré en ma main les habitants du pays, et le pays est soumis devant l’Éternel et devant son peuple.
19 Yanzu fa sai ku sa zuciyarku da ranku ga neman Ubangiji Allahnku. Ku fara ginin wuri mai tsarki na Ubangiji Allah, don ku kawo akwatin alkawarin Ubangiji da kayayyaki masu tsarki na Allah a cikin haikalin da za a gina saboda Sunan Ubangiji.”
Maintenant, appliquez vos cœurs et vos âmes à rechercher l’Éternel, votre Dieu; et levez-vous, et bâtissez le sanctuaire de l’Éternel Dieu, pour amener l’arche de l’alliance de l’Éternel et les ustensiles du sanctuaire de Dieu dans la maison qui sera bâtie pour le nom de l’Éternel.

< 1 Tarihi 22 >