< 1 Tarihi 12 >

1 Waɗannan su ne mutanen da suka zo wurin Dawuda a Ziklag, yayinda aka kore shi daga gaban Shawulu ɗan Kish (suna cikin jarumawan da suka taimake shi a yaƙi;
Et ceux-ci vinrent vers David à Tsiklag, lorsqu’il se tenait loin encore de la face de Saül, fils de Kis; et ceux-ci étaient parmi les hommes forts qui lui donnaient du secours dans la guerre,
2 suna da baka suna kuma iya harba kibiya, ko majajjawa da hannun dama ko na hagu; su’yan’uwan Shawulu ne daga kabilar Benyamin):
armés d’arcs, se servant de la main droite et de la main gauche [pour lancer] des pierres, et [pour tirer] des flèches avec l’arc; ils étaient d’entre les frères de Saül, de Benjamin:
3 Ahiyezer babbansu da Yowash’ya’yan Shema’a maza daga Gibeya; Yeziyel da Felet’ya’yan Azmawet; Beraka, Yehu daga Anatot,
le chef Akhiézer, et Joas, [tous deux] fils de Shemaa, le Guibhathite; et Jeziel, et Péleth, les fils d’Azmaveth; et Beraca, et Jéhu, l’Anathothite;
4 da Ishmahiya daga Gibeyon, wani jarumi a cikin Talatin nan, wanda shi ne shugaban Talatin; Irmiya, Yahaziyel, Yohanan, Yozabad daga Gedera,
et Jishmahia, le Gabaonite, homme fort parmi les 30, et au-dessus des 30; et Jérémie, et Jakhaziel, et Jokhanan, et Jozabad, le Guedérathite;
5 Eluzai, Yerimot, Beyaliya, Shemariya da Shefatiya daga Haruf;
Elhuzaï, et Jerimoth, et Bealia, et Shemaria, et Shephatia, le Haruphite;
6 Elkana, Isshiya, Azarel, Yoyezer da Yashobeyam daga Kora;
Elkana, et Jishija, et Azareël, et Joézer, et Jashobham, Corites;
7 da Yoyela da Zebadiya’ya’yan Yeroham maza daga Gedor.
et Joéla et Zebadia, les fils de Jerokham, de Guedor.
8 Sai waɗansu mutanen Gad suka koma suna goyon bayan Dawuda suka kuma haɗa kai da shi a kagararsa a hamada. Su ƙwararrun mayaƙa ne, a shirye don yaƙi, kuma suna iya riƙe garkuwa da māshi. Fuskokinsu kamar fuskoki zakoki, kuma suna da sauri kamar bareyi a kan duwatsu.
Et, des Gadites, il se détacha, [pour se joindre] à David dans le lieu fort au désert, des hommes forts et vaillants, hommes exercés pour la guerre, armés de boucliers et de piques; et leurs faces étaient comme des faces de lions, et ils étaient prompts comme des gazelles sur les montagnes:
9 Ezer shi ne babba, Obadiya shi ne mai binsa a shugabanci, Eliyab na uku,
Ézer, le premier; Abdias, le second; Éliab, le troisième;
10 Mismanna na huɗu, Irmiya na biyar,
Mishmanna, le quatrième; Jérémie, le cinquième;
11 Attai na shida, Eliyel na bakwai,
Atthaï, le sixième; Éliel, le septième;
12 Yohanan na takwas, Elzabad na tara,
Jokhanan, le huitième; Elzabad, le neuvième;
13 Irmiya na goma da kuma Makbannai na goma sha ɗaya.
Jérémie, le dixième; Macbannaï, le onzième.
14 Waɗannan mutanen Gad shugabannin mayaƙa ne; ƙarami a cikinsu zai iya ƙara da mutum ɗari, kuma babba a cikin zai iya ƙara da dubu.
Ceux-là, d’entre les fils de Gad, étaient chefs de l’armée; le moindre [était chef] de 100 [hommes], et le plus grand, de 1 000.
15 Su ne suka haye Urdun a wata na farko sa’ad da kogin ya yi ambaliya, suka kuma kori duk mai rai a kwarin, na wajen gabas da na wajen yamma.
Ce sont ceux qui traversèrent le Jourdain au premier mois, quand il regorge par-dessus tous ses bords; et ils mirent en fuite ceux de toutes les vallées, vers le levant et vers le couchant.
16 Sauran mutanen Benyamin da waɗansu mutanen Yahuda su ma suka zo wurin Dawuda a kagararsa.
Et des fils de Benjamin et de Juda allèrent vers David dans le lieu fort.
17 Sai Dawuda ya fita don yă tarye su, ya kuma ce musu, “In kun zo wurina da salama, don ku taimake ni, to, ina a shirye in bar ku ku haɗa kai tare da ni. Amma in kun zo don ku bashe ni ga abokan gābana sa’ad da hannuwana ba su da laifi a rikici, bari Allah na kakanninmu yă duba yă kuma shari’anta ku.”
Et David sortit à leur rencontre, et prit la parole et leur dit: Si c’est pour la paix que vous venez vers moi, pour m’aider, mon cœur sera uni à vous; mais si c’est pour me livrer à mes ennemis, quand il n’y a pas de violence en ma main, que le Dieu de nos pères regarde, et punisse.
18 Sai Ruhu ya sauko a kan Amasai, shugaban Talatin nan, sai ya ce, “Mu naka ne, ya Dawuda! Muna tare da kai, ya ɗan Yesse! Nasara, nasara gare ka, nasara kuma ga waɗanda suke taimakonka. Gama Allahnka zai taimake ka.” Saboda haka Dawuda ya karɓe su ya kuma mai da su shugabannin ƙungiyoyin maharansa.
Et l’Esprit revêtit Amasçaï, chef des principaux capitaines: Nous sommes à toi, David, et avec toi, fils d’Isaï! Paix, paix à toi, et paix à ceux qui t’aident, car ton Dieu t’aide! Et David les reçut, et les établit chefs de bandes.
19 Waɗansu mutanen Manasse suka haɗa kai da Dawuda sa’ad da ya tafi tare da Filistiyawa don yă yaƙi Shawulu (Shi da mutanensa ba su taimaki Filistiyawa ba domin bayan shawarwari, shugabanninsu suka salame shi. Sun ce, “Za mu biya da kawunanmu in ya koma ga maigidansa Shawulu.”)
Et, de Manassé, il y en eut qui passèrent à David quand il vint avec les Philistins pour la bataille contre Saül; mais ils ne les aidèrent point, car, après avoir tenu conseil, les princes des Philistins le renvoyèrent, disant: Au péril de nos têtes il passera à son seigneur Saül.
20 Da Dawuda ya tafi Ziklag, waɗannan mutanen Manasse ne suka haɗa kai da shi. Adna, Yozabad, Yediyayel, Mika’ilu, Yozabad, Elihu da Zilletai, shugabannin ƙungiyoyi na dubu a cikin Manasse.
Quand il s’en alla à Tsiklag, [ceux-ci], de Manassé, passèrent à lui: Adnakh, et Jozabad, et Jediaël, et Micaël, et Jozabad, et Élihu, et Tsilthaï, chefs des milliers qui étaient dans Manassé;
21 Suka taimaki Dawuda a kan ƙungiyoyin hari, gama dukansu jarumawa ne sosai, kuma su shugabanni ne a cikin mayaƙansa.
et ils aidèrent David dans ses expéditions, car ils étaient tous forts et vaillants, et ils furent chefs dans l’armée.
22 Kowace rana mutane suka riƙa zuwa don su taimaki Dawuda, sai da ya kasance da runduna mai girma, kamar mayaƙan Allah.
Car de jour en jour il arrivait [des gens] vers David pour l’aider, jusqu’à ce que le camp fut grand, comme un camp de Dieu.
23 Ga yawan mutanen shiryayyu don yaƙi waɗanda suka zo wurin Dawuda a Hebron don su mai da mulkin Shawulu gare shi, yadda Ubangiji ya faɗa.
Et c’est ici le nombre des hommes équipés pour l’armée, qui vinrent vers David à Hébron, afin de lui transférer le royaume de Saül, selon le commandement de l’Éternel:
24 Mutanen Yahuda, masu riƙe garkuwa da māshi, su 6,800 shiryayyu don yaƙi;
Fils de Juda, portant le bouclier et la pique, 6 800, équipés pour l’armée.
25 mutanen Simeyon, jarumawa shiryayyu don yaƙi, su 7,100;
Des fils de Siméon, hommes forts et vaillants pour l’armée, 7 100.
26 mutanen Lawi, su 4,600,
Des fils de Lévi, 4 600.
27 haɗe da Yehohiyada, shugaban iyalin Haruna tare da mutane 3,700,
Et Jehoïada, prince [des fils] d’Aaron, et avec lui 3 700.
28 da Zadok, matashi jarumi sosai, tare da shugabanni su 22 daga iyalinsa;
Et Tsadok, jeune homme fort et vaillant; et la maison de son père, 22 chefs.
29 mutanen Benyamin,’yan’uwan Shawulu, su 3,000, yawanci waɗanda suke biyayya ga gidan Shawulu sai lokacin;
Et, des fils de Benjamin, frères de Saül, 3 000; car jusqu’alors la plus grande partie d’entre eux faisaient la garde de la maison de Saül.
30 mutanen Efraim, jarumawa, sanannu cikin gidajensu, su 20 800;
Et, des fils d’Éphraïm, 20 800 hommes forts et vaillants, hommes de renom dans leurs maisons de pères.
31 mutanen rabin kabilar Manasse, sanannu da sunaye suka zo suka mai da Dawuda sarki, su 18,000;
Et, de la demi-tribu de Manassé, 18 000, qu’on avait nommés par nom pour aller établir David roi.
32 mutanen Issakar, masu fahimtar lokuta suka kuma san abin da ya kamata Isra’ila ya yi, manya 200, tare da danginsu a ƙarƙashin shugabancinsu;
Et, des fils d’Issacar, qui savaient discerner les temps pour savoir ce que devait faire Israël: leurs chefs, 200, et tous leurs frères à leur commandement.
33 mutanen Zebulun, ƙwararru sojoji shiryayyu don yaƙi da kowane irin makami, suka zo don su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya, su 50,000;
De Zabulon, ceux qui allaient à l’armée, préparés pour le combat, avec toutes les armes de guerre: 50 000, gardant leur rang, n’ayant point un cœur double.
34 mutanen Naftali su 1,000 shugabanni, tare da mutane 37,000 masu riƙe garkuwa da masu;
Et, de Nephthali, 1 000 chefs, et avec eux, portant le bouclier et la lance, 37 000.
35 mutanen Dan, shiryayyu don yaƙi, su 28,600;
Et, des Danites, préparés pour la guerre, 28 600.
36 mutanen Asher, ƙwararrun sojoji shiryayyu don yaƙi, su 40,000;
Et, d’Aser, qui allaient à l’armée pour se mettre en ordre de bataille pour le combat, 40 000.
37 kuma daga gabashin Urdun, mutanen Ruben, Gad da kuma rabin kabilar Manasse, masu kayan yaƙi iri-iri, su 120,000.
Et, d’au-delà le Jourdain, des Rubénites, et des Gadites, et de ceux de la demi-tribu de Manassé, avec toutes les armes de guerre pour combattre: 120 000.
38 Dukan waɗannan mayaƙa ne waɗanda suka ba da kansu da yardar rai su yi hidima. Suka zo Hebron da cikakken niyya don su naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila. Duka sauran Isra’ilawa su ma suka goyi baya a naɗa Dawuda sarki.
Tous ceux-là, hommes de guerre, gardant leurs rangs en ordre de bataille, vinrent à Hébron d’un cœur droit, pour établir David roi sur tout Israël; et aussi tout le reste d’Israël était d’un seul cœur pour établir David roi.
39 Mutanen suka yi kwana uku a can tare da Dawuda, suna ci suna sha, gama iyalansu sun yi musu tanadi.
Et ils furent là avec David trois jours, mangeant et buvant; car leurs frères leur avaient [tout] préparé.
40 Haka ma, maƙwabtansu daga nesa har Issakar, Zebulun da Naftali suka zo suka kawo abinci a kan jakuna, raƙuma, alfadarai da shanu. Akwai tanadin mai yawa na gari, kauɗar ɓaure, nonnan busassun’ya’yan inabi, ruwan inabi, mai, shanu da tumaki. Duk an yi haka don a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra’ila.
Et même, ceux qui étaient le plus rapprochés d’eux, jusqu’à Issacar et à Zabulon et à Nephthali, apportaient des vivres sur des ânes et sur des chameaux et sur des mulets et sur des bœufs, des aliments de farine, des gâteaux de figues sèches, et des gâteaux de raisins secs, et du vin, et de l’huile, et du gros et du menu bétail en abondance; car il y avait de la joie en Israël.

< 1 Tarihi 12 >