< 1 Tarihi 20 >

1 Da bazara, a lokacin da sarakuna kan tafi yaƙi, Yowab ya jagorance mayaƙa. Ya lalatar da ƙasar Ammonawa ya kuma tafi Rabba ya yi mata kwanto, amma Dawuda ya zauna a Urushalima. Yowab ya yaƙi Rabba, ya kuma bar ta kango.
L'année suivante, au temps où les rois se mettaient en campagne, Joab conduisit le gros de l'armée; il ravagea le pays des enfants d'Ammon et vint assiéger Rabba, tandis que David restait à Jérusalem. Or Joab battit Rabba et la détruisit.
2 Dawuda ya ɗauki rawani daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti na zinariya, aka kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, sai Dawuda kuwa ya sa a kansa. Ya kuma kwashi ganima mai yawa daga birnin
Et David prit la couronne de dessus la tête de leur roi, et la trouva du poids d'un talent d'or; et il y avait des pierres précieuses. On la mit sur la tête de David, qui emmena de la ville un fort grand butin.
3 ya kuma fitar da mutanen da suke can, ya sa su aiki da zartuna da makamai masu kaifi da kuma gatura. Dawuda ya yi haka da dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da mayaƙansa gaba ɗaya suka koma Urushalima.
Il fit sortir aussi les habitants et les mit en pièces avec des scies, des herses de fer et des faux. David traita de même toutes les villes des enfants d'Ammon. Puis David retourna à Jérusalem avec tout le peuple.
4 Ana nan, sai yaƙi ya ɓarke a Gezer tsakanin Isra’ila da Filistiyawa. Sai Sibbekai mutumin Husha ya kashe Siffai, ɗaya daga cikin zuriyar Refahiyawa, ta haka kuma aka ci Filistiyawa da yaƙi.
Après cela la guerre continua à Guézer avec les Philistins. Alors Sibbécaï, le Hushathite, tua Sippaï, l'un des enfants de Rapha; et ils furent humiliés.
5 Yaƙi kuma ya sāke tashi tsakanin Isra’ilawa da Filistiyawa, Elhanan ɗan Yayir ya kashe Lahmi ɗan’uwan Goliyat mutumin Gat, wanda yake riƙe da māshi mai sandan masaƙa.
Il y eut encore guerre avec les Philistins. Et Elchanan, fils de Jaïr, tua Lachmi, frère de Goliath, le Guitthien, qui avait une lance dont le bois était comme une ensuble de tisserand.
6 Aka sāke yin wani yaƙin kuma, wanda ya faru a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu da kuma yatsotsi shida a kowace ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriyar Rafa ce.
Il y eut encore une autre guerre, à Gath, où se trouva un homme de haute taille, qui avait six doigts à chaque main et à chaque pied, vingt-quatre en tout, et qui était aussi de la race de Rapha.
7 Sa’ad da ya yi wa Isra’ila ba’a, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwan Dawuda ya kashe shi.
Il outragea Israël; mais Jonathan, fils de Shimea, frère de David, le tua.
8 Waɗannan su ne zuriyar Rafa a Gat, Dawuda da mutanensa sun kashe su.
Ceux-là étaient nés à Gath, de la race de Rapha, et ils périrent de la main de David, et de la main de ses serviteurs.

< 1 Tarihi 20 >