< 1 Tarihi 19 >

1 Ana nan, sai Nahash sarkin Ammonawa ya mutu, sai ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Il arriva, après cela, que Nachash, roi des enfants d'Ammon, mourut; et son fils régna à sa place.
2 Dawuda ya yi tunani, “Zan nuna jinƙai ga Hanun ɗan Nahash, domin mahaifinsa ya nuna alheri gare ni.” Saboda haka Dawuda ya aika da tawaga don yă yi wa Hanun ta’aziyya game da mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka iso wurin Hanun a ƙasar Ammonawa don su ta’azantar da shi,
Et David dit: J'userai de bonté envers Hanun, fils de Nachash; car son père a usé de bonté envers moi. David envoya donc des messagers pour le consoler au sujet de son père; et les serviteurs de David vinrent au pays des enfants d'Ammon vers Hanun, pour le consoler.
3 sai manyan Ammonawa suka ce wa Hanun, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aika mutanen nan wurinka su ta’azantar da kai? Ba mutanensa sun zo ne su bincika su kuma leƙi ƙasar su tumɓuke ta ba?”
Mais les chefs des enfants d'Ammon dirent à Hanun: Penses-tu que ce soit pour honorer ton père, que David t'envoie des consolateurs? N'est-ce pas pour examiner la ville et pour la détruire, et pour explorer le pays, que ses serviteurs sont venus auprès de toi?
4 Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda, ya yi musu aski, ya yayyanka rigunansu a daidai ɗuwawunsu, sa’an nan ya sallame su.
Alors Hanun prit les serviteurs de David, les fit raser, et fit couper leurs habits par le milieu, jusqu'au haut des jambes, et les renvoya.
5 Da wani ya zo ya faɗa wa Dawuda game da mutanen, sai ya aiki’yan aika su sadu da su, gama an ƙasƙantar da su ainun. Sarki ya ce, “Ku zauna a Yeriko har sai gemunku sun yi girma, sa’an nan ku dawo.”
Cependant on vint informer David de ce qui était arrivé à ces hommes, et il envoya à leur rencontre, car ces hommes étaient fort confus; et le roi leur fit dire: Restez à Jérico jusqu'à ce que votre barbe ait repoussé, et alors vous reviendrez.
6 Sa’ad da Ammonawa suka gane cewa sun zama abin wurin a kafan hancin Dawuda, Hanun da Ammonawa suka aika da talenti dubu na azurfa don su yi haya da kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi daga Aram-Naharayim, Aram Ma’aka da Zoba.
Or les enfants d'Ammon virent qu'ils s'étaient mis en mauvaise odeur auprès de David. Hanun et les enfants d'Ammon, envoyèrent donc mille talents d'argent, pour prendre à leur solde des chars et des cavaliers chez les Syriens de Mésopotamie, et chez les Syriens de Maaca et de Tsoba;
7 Suka yi hayar kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi dubu talatin da biyu, da kuma sarkin Ma’aka tare da mayaƙansa, waɗanda suka zo suka kafa sansani kusa da Medeba, yayinda Ammonawa suka tattaru daga garuruwansu suka fita yaƙi.
Et ils prirent à leur solde trente-deux mille chars, et le roi de Maaca avec son peuple, lesquels vinrent et campèrent devant Médéba. Les enfants d'Ammon se rassemblèrent aussi de leurs villes, et vinrent pour combattre.
8 Da jin haka, Dawuda ya aiki Yowab tare da dukan mayaƙa masu yaƙi.
David l'apprit, et il envoya Joab et toute l'armée, les hommes vaillants.
9 Ammonawa suka fito suka ja dāgā a ƙofar birninsu, yayinda sarakunan da suka zo, su kansu suka ware suna a fili.
Et les enfants d'Ammon sortirent et se rangèrent en bataille à l'entrée de la ville; et les rois qui étaient venus, étaient à part dans la campagne.
10 Yowab ya ga cewa akwai dāgā a gabansa da bayansa; sai ya zaɓi waɗansu mayaƙa mafi kyau a Isra’ila ya sa su a kan Arameyawa.
Alors Joab, voyant que l'armée était tournée contre lui devant et derrière, choisit, de toutes les troupes d'élite d'Israël, des gens qu'il rangea contre les Syriens;
11 Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin kulawar Abishai ɗan’uwansa, aka sa a kan Ammonawa.
Et il donna la conduite du reste du peuple à Abishaï, son frère; et ils se rangèrent contre les enfants d'Ammon.
12 Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ni ƙarfi, sai ka kawo mini ɗauke da ni; amma in Ammonawa sun fi ka ƙarfi, sai in kawo maka ɗauke.
Et il dit: Si les Syriens sont plus forts que moi, tu viendras à mon secours; et si les enfants d'Ammon sont plus forts que toi, je te délivrerai.
13 Ka yi ƙarfin hali bari mu yi yaƙi da jaruntaka saboda mutanenmu da biranen Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da ya ga ya yi masa kyau.”
Sois ferme, et montrons-nous vaillants pour notre peuple, et pour les villes de notre Dieu; et que l'Éternel fasse ce qui lui semblera bon!
14 Sai Yowab da ƙungiyoyin mayaƙan da suke tare da shi suka matso don su yi yaƙi da Arameyawa, Arameyawan kuwa suka gudu a gabansa.
Alors Joab, et le peuple qui était avec lui, s'approchèrent pour livrer bataille aux Syriens, et ils s'enfuirent devant lui.
15 Sa’ad da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka guda a gaban ɗan’uwansa Abishai suka shiga cikin birni. Sai Yowab ya koma Urushalima.
Et les enfants d'Ammon, voyant que les Syriens s'étaient enfuis, s'enfuirent aussi devant Abishaï, frère de Joab, et rentrèrent dans la ville. Et Joab revint à Jérusalem.
16 Bayan Arameyawa suka ga cewa Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka aiki’yan aika suka sa aka kawo Arameyawan da suke hayen Kogi waɗanda Shobak shugaban mayaƙan Hadadezer yake shugabanta.
Les Syriens, voyant qu'ils avaient été battus par Israël, envoyèrent des messagers, et firent venir les Syriens qui étaient de l'autre côté du fleuve; et Shophac, chef de l'armée de Hadarézer, était à leur tête.
17 Sa’ad da aka faɗa wa Dawuda wannan, sai tattara dukan Isra’ila ya haye Urdun; ya tafi wurinsu ya kuwa ja dāgā ɗaura da su. Dawuda ya ja dāgārsa don yă sadu da Arameyawa a yaƙi, su kuwa suka yi yaƙi da shi.
Cela fut rapporté à David, qui rassembla tout Israël, passa le Jourdain, vint vers eux, et se rangea en bataille contre eux. David rangea donc son armée en bataille contre les Syriens, et ils combattirent contre lui.
18 Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, mutanen Dawuda kuwa suka kashe masu hawan keken yaƙinsu dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya kuma kashe Shobak shugaban mayaƙansu.
Mais les Syriens s'enfuirent devant Israël; et David tua aux Syriens les combattants de sept mille chars, et quarante mille hommes de pied, et mit à mort Shophac, chef de l'armée.
19 Da abokan tarayyar Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka nemi salama da Dawuda suka kuma zama bayinsa. Saboda haka Arameyawa ba su ƙara yarda su taimaki Ammonawa ba.
Et les serviteurs de Hadarézer, voyant qu'ils avaient été battus par Israël, firent la paix avec David, et lui furent assujettis. Et les Syriens ne voulurent plus secourir les enfants d'Ammon.

< 1 Tarihi 19 >