< Psaumes 28 >

1 Vers vous, Seigneur, je crierai: Mon Dieu, ne gardez pas le silence, en vous éloignant de moi, de peur que si vous vous taisez, en vous éloignant de moi, je ne devienne semblable à ceux qui descendent dans la fosse.
Ta Dawuda. A gare ka nake kira, ya Ubangiji Dutsena; kada ka yi mini kunnen ƙashi. Gama in ka yi shiru, zan zama kamar waɗanda suka gangara rami.
2 Exaucez, Seigneur, la voix de ma supplication, lorsque je vous prie, lorsque j’élève mes mains vers votre temple saint.
Ka ji kukata ta neman jinƙai yayinda nake kira ka don neman taimako, yayinda nake daga hannuwana wajen Wurinka Mafi Tsarki.
3 Ne m’entraînez pas avec des pécheurs, et ne me perdez pas avec des hommes qui opèrent l’iniquité: Qui parlent paix avec leur prochain, et qui ont le mal dans leurs cœurs.
Kada ka ja ni tare da mugaye, tare da masu yin mugunta, masu magana kamar ta alheri ce da maƙwabtansu amma suna riƙe da su a zukatansu.
4 Donnez-leur selon leurs œuvres et selon la méchanceté de leurs inventions: Accordez-leur, selon leurs œuvres de leurs mains; rendez-leur leur salaire.
Ka sāka musu da ayyukansu da kuma don mugun aikinsu; ka sāka musu saboda abin da hannuwansu suka yi ka kuma mayar musu abin da ya dace da su.
5 Parce qu’ils n’ont pas appliqué leur esprit aux œuvres du Seigneur, et aux œuvres de ses mains, vous les détruirez, et vous ne les rétablirez pas.
Da yake ba su kula da ayyukan Ubangiji da abin da hannuwansa suka yi ba, zai rushe su ba kuwa zai ƙara gina su ba.
6 Béni le Seigneur! parce qu’il a exaucé la voix de ma supplication.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya ji kukata na neman jinƙai.
7 Le Seigneur est mon aide et mon protecteur: en lui a espéré mon cœur, et j’ai été secouru: Et ma chair a refleuri; aussi de toute mon âme je le glorifierai.
Ubangiji shi ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta amince da shi, kuma na sami taimako. Zuciyata ta yi tsalle don farin ciki zan kuwa yi godiya gare shi cikin waƙa.
8 Le Seigneur est la force de son peuple; le protecteur et le sauveur de son Christ.
Ubangiji shi ne ƙarfin mutanensa, kagarar ceto domin shafaffensa.
9 Sauvez votre peuple, Seigneur, et bénissez votre héritage; dirigez-les, et élevez-les jusque dans l’éternité.
Ka cece mutanenka ka kuma albarkace gādonka; ka zama mai kiwonsu ka kuma riƙe su har abada.

< Psaumes 28 >