< 2 Samuel 11 >

1 Or, il arriva qu’au retour de l’année, au temps que les rois ont coutume d’aller à la guerre, David envoya Joab et ses serviteurs avec lui et tout Israël, et il ravagèrent les enfants d’Ammon et assiégèrent Rabba; mais David demeura à Jérusalem.
Da bazara, a lokacin da sarakuna sukan fita zuwa yaƙi, sai Dawuda ya aiki Yowab tare da mutanen sarki, da dukan Isra’ila. Suka je suka hallaka Ammonawa, suka kuma yi wa Rabba kwanton ɓauna. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima.
2 Pendant que ces choses se passaient, il advint que David se levait de son lit après midi, et qu’il se promenait sur la terrasse du palais; or il vit une femme qui se baignait vis-à-vis sur sa terrasse; et cette femme était fort belle.
Wata rana da yamma, Dawuda ya tashi daga gadonsa, ya zaga kewaye a rufin fadansa. Daga rufin ya ga wata mace tana wanka. Matar kyakkyawa ce ƙwarai.
3 Le roi donc envoya, et demanda quelle était cette femme. Et on lui annonça que c’était Bethsabée, fille d’Eliam, femme d’Urie, l’Héthéen.
Sai Dawuda ya aiki wani yă bincika ko wace ce ita, sai mutumin ya dawo ya ce, “Wannan ba Batsheba ba ce,’yar Eliyam matar Uriya, mutumin Hitti?”
4 C’est pourquoi David, ayant envoyé des messagers, l’enleva. Lorsqu’elle fut entrée auprès de lui, il dormit avec elle: et aussitôt elle se purifia de son impureté;
Sa’an nan Dawuda ya aiki manzanni su kawo masa ita. Ta zo wurinsa shi kuma ya kwana da ita (A lokacin kuwa ta gama tsarkake kanta ke nan daga jinin haila.) Sa’an nan ta tafi gida.
5 Et elle retourna en sa maison, après avoir conçu. Et envoyant, elle annonça à David, et dit: J’ai conçu.
Matar ta yi ciki, ta kuwa aika wa Dawuda, tana cewa, “Ina da ciki.”
6 Or, David envoya vers Joab, disant: Envoie-moi Urie, l’Héthéen. Et Joab envoya Urie à David.
Saboda haka Dawuda ya aika saƙo wa Yowab ya ce, “Ka aiko mini da Uriya mutumin Hitti.” Yowab kuwa ya aika da shi wajen Dawuda.
7 Et Urie vint vers David; et David demanda si Joab allait bien ainsi que le peuple, et comment la guerre était conduite.
Da Uriya ya zo wurinsa, sai Dawuda ya tambaye shi lafiyar Yowab da sojojin, da kuma yaya yaƙin yake tafiya.
8 Puis David dit à Urie: Va en ta maison, et lave tes pieds. Et Urie sortit de la maison du roi, et les mets du roi le suivirent.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa Uriya, “Gangara gidanka ka wanke ƙafafunka.” Saboda haka Uriya ya bar fadar, sarki kuma ya aika masa da kyauta.
9 Mais Urie dormit devant la porte de la maison du roi avec les autres serviteurs de son seigneur, et il ne descendit point en sa maison.
Amma Uriya ya kwanta a ƙofar fada tare da dukan bayin maigidansa, bai kuwa tafi gidansa ba.
10 Et on l’annonça à David, en disant: Urie n’est pas allé en sa maison. Et David demanda à Urie: Est-ce que tu ne viens pas d’un voyage? pourquoi n’es-tu pas descendu en ta maison?
Da aka gaya wa Dawuda, “Uriya bai tafi gida ba,” sai Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Ba ka zo daga wuri mai nisa ba? Me ya sa ba ka je gida ba?”
11 Et Urie répondit à David: L’arche de Dieu, et Israël, et Juda, habitent dans les pavillons, et mon seigneur Joab, et les serviteurs de mon seigneur demeurent sur la face de la terre, et moi, j’entrerai en ma maison, pour manger et boire, et pour dormir avec ma femme? Par votre salut, et par le salut de votre âme, je ne ferai pas cette chose.
Sai Uriya ya ce wa Dawuda, “Akwatin Alkawari, da Isra’ila, da Yahuda suna zama cikin tentuna, kuma maigidana Yowab da mutanen ranka yă daɗe suna a sansani a fili. Yaya zan je gidana in ci in sha in kuma kwana da matata? Muddin kana a raye, ba zan yi irin wannan abu ba!”
12 David donc dit à Urie: Demeure ici encore aujourd’hui, et demain je te renverrai. Urie demeura à Jérusalem ce jour-là et le lendemain.
Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ƙara dakata a nan kwana ɗaya, gobe kuwa in sallame ka.” Saboda haka Uriya ya dakata a Urushalima a ranar, da kuma ta biye.
13 Alors David l’appela pour qu’il mangeât devant lui et qu’il bût, et il l’enivra. Urie étant sorti le soir, dormit dans son lit avec les serviteurs de son seigneur, et il ne descendit pas en sa maison.
Dawuda ya gayyace shi, ya kuwa ci ya sha tare da shi, Dawuda ya sa ya bugu tilis. Amma da yamma Uriya ya koma ya kwanta a tabarmarsa cikin bayin maigidan sarki; bai je gida ba.
14 Il arriva donc le matin que David écrivit une lettre à Joab, et l’envoya par la main d’Urie,
Da safe Dawuda ya rubuta wa Yowab wasiƙa ya ba wa Uriya.
15 Ecrivant dans la lettre: Placez Urie au premier rang dans la bataille, là où le combat est le plus fort; et abandonnez-le, afin que, frappé, il périsse.
A ciki wasiƙar ya rubuta, “Tura Uriya a gaba inda yaƙi ya fi zafi. Sa’an nan ka janye daga gare shi don a buge shi yă mutu.”
16 Comme donc Joab assiégeait la ville, il plaça Urie dans le lieu où il savait qu’étaient les hommes les plus vaillants.
Saboda haka yayinda Yowab ya kai yaƙi kusa da birnin, sai tura Uriya a inda ya sani akwai jarumawan Ammon na gaske.
17 Et les hommes, étant sortis de la cité, combattaient contre Joab, et dans la multitude des serviteurs de David plusieurs tombèrent, et Urie, l’Héthéen, mourut aussi.
Sa’ad da mutanen garin suka fito suka yaƙi Yowab, sai waɗansu mutane daga sojojin Dawuda suka mutu; Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.
18 C’est pourquoi Joab envoya, et annonça à David tous les événements du combat,
Yowab ya aika wa Dawuda cikakken labari batun yaƙin.
19 Et il ordonna au messager, disant: Lorsque tu auras achevé au roi tout ton récit de la guerre,
Ya umarci manzon ya ce, “Da ka gama yin wa sarki wannan batun yaƙin,
20 Si tu vois qu’il s’indigne et dise: Pourquoi vous êtes-vous approchés du mur pour combattre? est-ce que vous ignoriez que beaucoup de traits sont lancés du haut du mur?
wataƙila sarki yă husata, yă tambaye ka, ‘Me ya sa kuka je kusa da birnin don ku yi yaƙi? Ba ku san cewa za su yi harbi daga katanga ba?
21 Qui frappa Abimélech, fils de Jérobaal? n’est-ce pas une femme qui lança du mur sur lui un morceau de meule, et le tua à Thébès? Pourquoi vous êtes-vous approchés du mur? tu diras: Votre serviteur Urie l’Héthéen est tombé mort aussi.
Wane ne ya kashe Abimelek ɗan Yerub-Beshet? Ba mace ce ta jefa dutsen niƙa a kansa daga katanga, ta haka ya mutu a Tebez ba? Me ya sa kuka je kurkusa da katangar?’ In ya tambaye ka wannan, sai ka ce masa, ‘Har bawanka Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.’”
22 Le messager donc partit, et il vint et raconta à David tout ce que lui avait ordonné Joab.
Manzon ya tashi ya tafi, da ya iso kuwa sai ya gaya wa Dawuda dukan abin da Yowab ya aike shi yă faɗa.
23 Et le messager dit à David: Les hommes ont prévalu contre nous, et ils sont sortis sur nous dans la campagne; mais nous, ayant fait une irruption, nous les avons poursuivis jusqu’à la porte de la ville.
Manzon ya ce wa Dawuda, “Mutanen sun sha kanmu suka fito suka yaƙe mu a fili, amma muka kore su har ƙofar birni.
24 Et les archers ont lancé des traits contre vos serviteurs du haut du mur; et il est mort des serviteurs du roi, et, qui plus est, votre serviteur Urie, l’Héthéen, est mort.
Sa’an nan maharba suka yi ta harbi daga katanga har waɗansu mutanen sarki suka mutu. Ban da haka ma, Uriya mutumin Hitti bawan sarki ya mutu.”
25 Et David répondit au messager: Tu diras ceci à Joab: Que cela ne t’abatte point; car divers est le succès de la guerre; c’est maintenant celui-ci, et maintenant celui-là que dévore le glaive: anime tes combattants contre la ville, afin que tu la détruises, et encourage-les.
Dawuda ya ce wa manzon, “Ka gaya wa Yowab, ‘Kada ka bar wannan yă dame ka; yadda takobi ya lamushe wannan, haka zai lamushe wancan ma. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku hallaka shi.’ Ka faɗa haka don ka ƙarfafa Yowab.”
26 Or, la femme d’Urie apprit qu’Urie, son mari, était mort, et elle le pleura.
Da matar Uriya ta ji cewa mijinta ya mutu, sai ta yi makoki saboda shi.
27 Mais, le deuil passé, David envoya, et il l’introduisit en sa maison; alors elle devint sa femme, et elle lui enfanta un fils. Or, cette action qu’avait faite David déplut au Seigneur.
Bayan kwanakin makoki suka ƙare, Dawuda ya sa aka kawo ta gidansa, ta kuwa zama matarsa, ta kuma haifa masa ɗa. Sai dai abin da Dawuda ya yi bai gamshi Ubangiji ba.

< 2 Samuel 11 >