< Psaumes 22 >
1 Pour la fin, pour le secours du matin, psaume de David. Dieu, mon Dieu, regardez-moi: pourquoi m’avez-vous délaissé? Les paroles de mes péchés sont loin de mon salut.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
2 Mon Dieu, je crierai pendant le jour, et vous ne m’exaucerez pas: et pendant la nuit, et ce n’est point à moi une folie.
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
3 Mais vous, vous habitez dans un sanctuaire, vous la louange d’Israël.
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
4 C’est en vous qu’ont espéré nos pères: ils ont espéré, et vous les avez délivrés.
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
5 Vers vous ils ont crié et ils ont été sauvés: en vous ils ont espéré, et ils n’ont point été confondus.
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
6 Pour moi je suis un ver et non pas un homme; l’opprobre des hommes et l’abjection du peuple.
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
7 Tout ceux qui m’ont vu m’ont tourné en dérision: ils ont parlé du bout des lèvres, et ils ont secoué la tête.
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
8 Il a espéré dans le Seigneur, qu’il le délivre; qu’il le sauve, puisqu’il l’aime.
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
9 Cependant c’est vous qui m’avez tiré du sein de ma mère: vous êtes mon espérance depuis que je suçais les mamelles de ma mère.
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
10 C’est sur vous que j’ai été posé, en sortant de son sein; depuis que j’étais dans les entrailles de ma mère, vous êtes mon Dieu.
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
11 Ne vous éloignez pas de moi:
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
12 De jeunes taureaux en grand nombre m’ont environné; des taureaux gras m’ont assiégé.
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13 Ils ont ouvert sur moi leur gueule comme un lion ravissant et rugissant.
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14 Je me suis épanché comme de l’eau, et tous mes os se sont déboîtés. Mon cœur est devenu au dedans de moi comme une cire qui se fond.
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15 Ma force s’est desséchée comme un têt, et ma langue s’est attachée à mon palais; et vous m’avez conduit à la poussière de la mort.
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16 Parce que des chiens nombreux m’ont environné; un conseil de méchants m’a assiégé: Ils ont percé mes mains et mes pieds:
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17 Ils ont compté tous mes os. Ils m’ont eux-mêmes considéré et regardé attentivement.
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18 Ils se sont partagé mes vêtements, et sur ma robe ils ont jeté le sort.
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19 Mais vous, Seigneur, n’éloignez pas votre secours de moi: voyez à ma défense.
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20 Arrachez mon âme à l’épée à double tranchant; et mon unique de la main du chien.
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21 Sauvez-moi de la gueule du lion; et ma faiblesse des cornes des licornes.
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
22 Je raconterai votre nom à mes frères; je vous louerai au milieu de l’assemblée.
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 Vous qui craignez le Seigneur, louez-le; race entière de Jacob, glorifiez-le:
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 Que toute la race d’Israël le craigne, parce qu’il n’a pas méprisé ni dédaigné la supplication du pauvre; Et qu’il n’a point détourné sa face de moi, et que lorsque je criais vers lui, il m’a exaucé.
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25 Devant vous sera ma louange dans une grande assemblée: je rendrai mes vœux en présence de ceux qui le craignent.
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
26 Les pauvres mangeront et seront rassasiés; et ils loueront le Seigneur, ceux qui le recherchent; leurs cœurs vivront dans les siècles des siècles.
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
27 Tous les confins de la terre se souviendront du Seigneur et se convertiront à lui: Et toutes les familles des nations adoreront en sa présence.
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
28 Parce qu’au Seigneur appartient le règne; et que c’est lui qui dominera sur les nations.
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
29 Tous les riches de la terre ont mangé et ont adoré: en sa présence tomberont tous ceux qui descendent dans la terre.
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
30 Et mon âme vivra pour lui; et ma postérité le servira.
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
31 La génération qui doit venir sera annoncée au Seigneur; et les cieux annonceront sa justice au peuple qui naîtra, et qu’a fait le Seigneur.
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.