< Proverbes 1 >
1 Paraboles de Salomon, fils de David et roi d’Israël,
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 Utiles pour connaître la sagesse et la discipline,
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 Pour comprendre les paroles de la prudence, pour recevoir l’instruction de la doctrine, la justice, et le jugement et l’équité,
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 Afin que soit donnée aux tout petits la finesse, à l’adolescent la science et l’intelligence.
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 Le sage, en écoutant, sera plus sage, et l’intelligent possédera les moyens de gouverner.
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 Il découvrira le proverbe et l’interprétation, les paroles des sages et leurs énigmes.
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 La crainte du Seigneur est le principe de la sagesse. La sagesse et la doctrine, les insensés les méprisent.
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 Écoute, mon fils, la discipline de ton père, et ne rejette pas la loi de ta mère,
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 Afin que soit ajouté un agrément à ta tête, et un collier à ton cou.
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 Mon fils, si des pécheurs veulent l’attirer, n’y acquiesce pas.
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 S’ils disent: Viens avec nous, dressons des embûches au sang, cachons des pièges à l’innocent qui ne l’a pas mérité;
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 Comme l’enfer, engloutissons-le vivant et entier, comme celui qui descend dans la fosse. (Sheol )
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol )
13 Nous trouverons toutes sortes de biens précieux: nous remplirons nos maisons de dépouilles.
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 Mets ta part avec nous, qu’une seule bourse soit pour nous tous.
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 Mon fils, ne marche pas avec eux, écarte ton pied de leurs sentiers.
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 Car leurs pieds courent au mal, et ils se hâtent afin de verser le sang.
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 Mais en vain l’on jette le filet devant les yeux des oiseaux.
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 Eux aussi à leur propre sang dressent des embûches, et
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 Ainsi sont les sentiers de tout avare, ils ravissent lame de tous ceux qui possèdent.
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 La sagesse prêche dehors; dans les places publiques elle élève sa voix;
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 À la tête des foules elle crie, aux portes de la ville elle profère ses paroles disant:
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 Jusques à quand, tout petits enfants, aimerez-vous l’enfance, et les insensés désireront-ils ce qui leur est pernicieux, et les imprudents haïront-ils la science?
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 Convertissez-vous à mes remontrances: voici que je vous révélerai mon esprit, et que je vous ferai comprendre mes paroles.
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 Parce que j’ai appelé, et que vous avez refusé de m’entendre; que j’ai tendu ma main, et qu’il n’y a eu personne qui m’ait regardé;
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 Que vous avez méprisé tous mes conseils, et négligé mes réprimandes:
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 Moi aussi, à votre mort, je rirai et je me moquerai, lorsque ce que vous craigniez vous sera arrivé.
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 Lorsqu’une calamité arrivera tout d’un coup, et que la mort, comme une tempête, fondra violemment sur vous; quand, viendront sur vous la tribulation et l’angoisse:
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 Alors ils m’invoqueront, et je ne les exaucerai pas; dès le matin ils se lèveront, et ils ne me trouveront pas;
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 Parce qu’ils ont haï la discipline, et qu’ils n’ont pas reçu la crainte du Seigneur,
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 Qu’ils n’ont pas acquiescé à mes conseils, qu’ils ont déprécié toutes mes remontrances.
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 Aussi ils mangeront les fruits de leurs voies, et ils seront rassasiés de leurs conseils.
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 L’égarement des tout petits les tuera; et la prospérité des insensés les perdra.
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 Mais celui qui m’écoute reposera sans terreur et jouira de l’abondance, la crainte des maux ayant été enlevée.
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”