< Proverbes 2 >
1 Mon fils, si tu reçois mes paroles, et si tu caches mes commandements en toi,
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2 En sorte que ton oreille écoute la sagesse: incline ton cœur pour connaître la prudence.
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3 Car si tu invoques la sagesse, et que tu inclines ton cœur vers la prudence;
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4 Si tu la recherches comme l’argent, et que tu creuses pour la trouver, comme les trésors:
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5 Alors tu comprendras la crainte du Seigneur, et tu trouveras la science de Dieu.
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6 Parce que c’est le Seigneur qui donne la sagesse, et que de sa bouche sortent la prudence et la science.
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7 Il veillera au salut des hommes droits, et protégera ceux qui marchent dans la simplicité,
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8 Conservant les sentiers de la justice, et gardant les voies des saints.
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9 C’est alors que tu comprendras la justice et le jugement, et l’équité et tout bon sentier.
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
10 Si la sagesse entre dans ton cœur, et que la science à ton âme plaise,
Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
11 Le conseil te gardera, et la prudence te sauvera,
Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
12 Afin que tu sois arraché à une voie mauvaise, et à l’homme qui tient des discours pervers;
Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
13 À ceux qui abandonnent le droit chemin, et qui marchent par des voies ténébreuses,
waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
14 Qui se réjouissent lorsqu’ils ont mal fait, qui tressaillent de joie dans les choses les plus mauvaises,
waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
15 Dont les voies son perverses, et dont les démarches sont infâmes.
waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
16 Afin que tu sois arraché à la femme d’autrui, et à l’étrangère, qui amollit ses paroles;
Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
17 Qui abandonne le guide de sa jeunesse,
wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
18 Et qui a oublié l’alliance de son Dieu: sa maison penche vers la mort, et ses sentiers vers les enfers;
Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
19 Tous ceux qui entrent chez elle ne reviendront pas, et ne prendront pas les sentiers de la vie.
Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
20 Afin que tu marches dans une voie bonne, et que tu gardes les sentiers des justes.
Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
21 Car les hommes qui sont droits habiteront sur la terre, et les simples y demeureront constamment.
Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
22 Mais les impies seront exterminés de la terre; et les méchants en seront enlevés.
amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.