< Psaumes 12 >
1 Pour la fin, pour l’octave, psaume de David. Sauvez-moi, Seigneur, car il n’y a plus de saint: les vérités ont diminué parmi les fils des hommes.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi. Bisa ga sheminit. Zabura ta Dawuda. Ka taimaka, Ubangiji, gama masu tsoron Allah ba sa nan kuma; masu aminci sun ɓace daga cikin mutane.
2 Ils ont dit des choses vaines, chacun à son prochain: leurs lèvres sont trompeuses; ils ont parlé avec un cœur et un cœur.
Kowa yana yi wa maƙwabcinsa ƙarya; zaƙin bakinsu maganar ƙarya ce suna cike da ruɗu a zukatansu.
3 Que Dieu perde entièrement toutes les lèvres trompeuses, et la langue qui profère des discours superbes,
Bari Ubangiji yă yanke dukan zaƙin bakinsu da kuma kowane harshe mai fariya,
4 Ils ont dit: Nous ferons éclater la puissance de notre langue; nos lèvres sont à nous, qui est notre maître?
masu cewa, “Da harsunanmu za mu yi nasara; leɓunanmu za su kāre mu, wane ne maigidanmu?”
5 À cause de la misère de ceux qui sont sans secours, et du gémissement des pauvres, maintenant je me lèverai, dit le Seigneur. Je les établirai dans le salut: j’agirai en cela avec une entière liberté.
“Saboda danniyar marasa ƙarfi da kuma nishin masu bukata, zan tashi yanzu,” in ji Ubangiji. “Zan kāre su daga masu yin musu sharri.”
6 Les paroles du Seigneur sont des paroles pures, un argent éprouvé par le feu, purifié dans la terre, raffiné jusqu’à sept fois.
Kalmomin Ubangiji kuwa ba su da kuskure, kamar azurfan da aka tace cikin matoyan yumɓu, aka tsabtacce sau bakwai.
7 C’est vous, Seigneur, vous qui nous sauverez, et qui nous préserverez de cette génération éternellement.
Ya Ubangiji, za ka kiyaye mu lafiya ka tsare mu daga irin mutanen nan har abada.
8 Les impies rôdent autour de nous; c’est dans la profondeur de vos desseins que vous avez multiplié les fils des hommes.
Mugaye suna yawo a sake sa’ad da ake girmama abin da ba shi da kyau a cikin mutane.