< Matthieu 25 >
1 Alors le royaume des cieux sera semblable à dix vierges qui, ayant pris leurs lampes, allèrent au-devant de l’époux et de l’épouse.
Sa'annan mulkin sama zai zama kamar budurwai goma da suka dauki fitilunsu domin su taryi ango.
2 Cinq d’entre elles étaient folles et cinq sages.
Biyar daga cikin su masu hikima ne biyar kuma wawaye.
3 Les cinq folles, en prenant leurs lampes, n’emportèrent point d’huile avec elles:
Sa'adda wawayen budurwai suka dauki fitilunsu, ba su dauki karin mai ba.
4 Mais les sages prirent de l’huile dans leurs vases avec les lampes.
Amma budurwai masu hikimar suka dauki gorar mai tare da fitilunsu.
5 Or l’époux tardant à venir, elles s’assoupirent toutes, et s’endormirent.
To da angon ya makara, dukkan su sai suka fara gyangyadi sai barci ya dauke su.
6 Mais au milieu de la nuit, un cri s’éleva: Voici l’époux qui vient; sortez au-devant de lui.
Amma da tsakkar dare sai aka yi shela, 'Ga ango ya iso! Ku fito taryensa.
7 Aussitôt toutes ces vierges se levèrent, et préparèrent leurs lampes.
Sai dukka budurwan nan suka tashi suka gyaggyara fitilunsu.
8 Mais les folles dirent aux sages: Donnez-nous de votre huile, parce que nos lampes s’éteignent.
Wawayen su ka ce da masu hikimar, 'Ku sammana kadan daga manku gama fitilunmu su na mutuwa.'
9 Les sages répondirent, disant: De peur qu’il n’y en ait pas assez pour nous et pour vous, allez plutôt à ceux qui en vendent, et achetez-en pour vous.
“Amma masu hikimar suka ce 'Tun da man ba zai ishe mu tare da ku ba, sai ku je gun ma su sayarwa ku sayo wa kanku.
10 Or pendant qu’elles allaient en acheter l’époux arriva; et celles qui étaient prêtes entrèrent avec lui dans la salle des noces, et la porte fut fermée.
Sa'adda suka tafi sayan man, sai angon ya shigo, kuma wadanda suke a shirye su ka shiga tare da shi bukin auren, sai aka rufe kofar.
11 Enfin les autres vierges vinrent aussi, disant: Seigneur, Seigneur, ouvrez-nous.
Bayan dan lokaci kadan sauran budurwan suka dawo suna cewa, 'Mai gida, mai gida, bude mana kofar.'
12 Mais l’époux répondant, dit: En vérité je vous dis que je ne vous connais point.
Amma ya amsa ya ce, 'A gaskiya ina gaya maku, ni ban san ku ba.'
13 Veillez donc, parce que vous ne savez ni le jour ni l’heure.
Don haka sai ku lura, don baku san rana ko sa'a ba.
14 C’est comme un homme qui, partant pour un voyage, appela ses serviteurs et leur remit ses biens.
Domin yana kama da wani mutum da zai tafi wata kasa. Ya kira barorinsa ya ba su dukiyar sa.
15 À l’un il donna cinq talents, à un autre deux, à un autre un, à chacun selon sa capacité, et il partit aussitôt.
Ga wani ya ba shi talanti biyar, ga wani ya ba shi biyu, ga wani kuma ya ba shi talanti daya. kowa an bashi gwargwadon iyawarsa, sai wannan mutum ya yi tafiyar sa
16 Or celui qui avait reçu les cinq talents s’en alla, les fit valoir et en gagna cinq autres.
nan da nan sai wanda ya karbi talanti biyar ya sa nasa a jari, ya sami ribar wasu talanti biyar.
17 Pareillement celui aussi, qui en avait reçu deux, en gagna deux autres.
Haka ma wanda ya karbi talanti biyu ya sami ribar wasu biyu.
18 Mais celui qui n’en avait reçu qu’un, s’en allant, creusa la terre maître.
Amma bawan da ya karbi talanti dayan ya yi tafiyar sa, ya haka rami, ya binne kudin mai gidansa.
19 Longtemps après, le maître de ces serviteurs revint et compta avec eux.
To bayan tsawon lokaci sai ubangidan barorin nan ya dawo, domin yayi lissafin kudinsu.
20 Alors celui qui avait reçu cinq talents s’approchant, lui présenta cinq autres talents, disant: Seigneur, vous m’avez remis cinq talents, en voici cinq autres que j’ai gagnés de plus.
Bawan da ya karbi talanti biyar, ya kawo nasa da ribar wasu biyar. Yace, 'Maigida, ka bani talanti biyar, gashi na samo ribar karin talanti biyar.'
21 Son maître lui répondit: Fort bien, serviteur bon et fidèle: parce que tu as été fidèle en peu de choses, je t’établirai sur beaucoup: entre dans la joie de ton maître.
Maigidansa yace masa, 'Madalla, bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abu kadan. Zan sa ka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'
22 Celui qui avait reçu deux talents vint aussi, et dit: Seigneur, vous m’aviez remis deux talents; en voici deux autres que j’ai gagnés.
Bawan da ya karbi talanti biyun, ya zo yace, 'Maigida, ka ba ni talanti biyu. Gashi kuwa na sami karin ribar wasu biyun.'
23 Son maître lui répondit: Fort bien, serviteur bon et fidèle: parce que tu as été fidèle en peu de choses, je t’établirai sur beaucoup: entre dans la joie de ton maître.
Ubangidansa yace masa, 'Madalla, kai bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abubuwa kadan. Zan saka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'
24 Puis s’approchant aussi, celui qui avait reçu un seul talent dit: Seigneur, je sais que vous êtes un homme sévère; vous moissonnez où vous n’avez point semé, et recueillez où vous n’avez rien mis.
Sai bawan da ya karbi talanti daya ya zo yace, 'Maigida, na san kai mai tsanani ne. Kana girbi inda baka yi shuka ba, kuma kana tattarawa inda ba ka watsa ba.
25 Aussi, craignant, je m’en suis allé et j’ai caché votre talent dans la terre: voici, je vous rends ce qui est à vous.
Na ji tsoro, don haka sai na je na boye talantinka a rami. Duba, ga abinda yake naka.'
26 Son maître répondant lui dit: Serviteur mauvais et paresseux, tu savais que je moissonne où je n’ai point semé, et que je recueille où je n’ai rien mis:
Amma ubangidansa ya amsa yace, kai mugu malalacin bawa, ka san cewa ni mai girbi ne inda ban shuka ba kuma ina tattarawa inda ban zuba ba.
27 Il fallait donc remettre mon argent aux banquiers, et, revenant, j’aurais reçu avec usure ce qui est à moi.
To da ba sai ka kai kudina a banki ba, da bayan na dawo da sai in karbi abina da riba.
28 Reprenez-lui donc le talent, et donnez-le à celui qui a dix talents.
Saboda haka ku kwace talantin daga gare shi ku baiwa mai talanti goman nan.
29 Car on donnera à celui qui a, et il sera dans l’abondance; mais à celui qui n’a pas, même ce qu’il semble avoir, lui sera ôté.
Gama ga wanda yake da shi za'a kara masa har ma a yalwace za'a kara bashi. Amma ga wanda bashi da komai abinda ke nasa ma za'a kwace.
30 Et jetez ce serviteur inutile dans les ténèbres extérieures: là sera le pleur et le grincement de dents.
Ku jefa wannan mugun bawan marar amfani, cikin duhu mai zurfi, inda ake kuka da cizon hakora.'
31 Or, quand le Fils de l’homme viendra dans sa majesté, et tous les anges avec lui, alors il s’assiéra sur le trône de sa majesté.
Sa'adda Dan mutum zai zo cikin daukakarsa da dukan Mala'iku tare da shi, sa'annan zai zauna kursiyinsa na daukaka.
32 Et toutes les nations seront rassemblées devant lui, et il les séparera les uns d’avec les autres, comme le pasteur sépare les brebis d’avec les boucs;
A gabansa za'a tattara dukkan al'ummai, zai rarraba mutanen daya'daya, kamar yadda makiyayi yake rarraba tumaki daga awaki.
33 Et il placera les brebis à sa droite et les boucs à sa gauche.
Zai sa tumakin a hannunsa na dama, amma awakin a hannunsa na hagu.
34 Alors, le roi dira à ceux qui seront à sa droite: Venez, les bénis de mon père; possédez le royaume préparé pour vous depuis la fondation du monde:
Sa'annan sarkin zai ce wa na hannun damarsa, 'Ku zo ku da Ubana ya albarkata, ku gaji mulkin da aka shirya maku kafin a kafa duniya.
35 Car j’ai eu faim, et vous m’avez donné à manger; j’ai eu soif, et vous m’avez donné à boire; j’étais sans asile, et vous m’avez recueilli;
Gama na ji yunwa kuka bani abinci; Na ji kishi kuka bani ruwa; Na yi bakunci kun bani masauki;
36 Nu, et vous m’avez vêtu; malade, et vous m’avez visité; en prison, et vous êtes venus à moi.
Na yi huntanci kuka tufasar dani; Na yi ciwo kuka kula dani; Ina kurkuku kuka ziyarceni.'
37 Alors les justes lui répondront: Seigneur, quand est-ce que nous vous avons vu ayant faim, et que nous vous avons rassasié; ayant soif, et que nous vous avons donné à boire?
Sa'annan masu adalcin za su amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa muka baka abinci? Ko kana jin kishi muka baka ruwan sha?
38 Quand est-ce que nous vous avons vu sans asile, et que nous vous avons recueilli; ou nu, et que nous vous avons vêtu?
Kuma yaushe muka ganka kana bakunci har muka baka masauki? Ko kuma kana huntanci da muka tufatar da kai?
39 Ou quand est-ce que nous vous avons vu malade ou en prison, et que nous sommes venus à vous?
Yaushe kuma muka ganka kana ciwo ko a kurkuku har muka ziyarce ka?'
40 Et le roi répondra, disant: En vérité, je vous dis: Chaque fois que vous l’avez fait à l’un de ces plus petits d’entre mes frères, c’est à moi que vous l’avez fait.
Sa'annan Sarkin zai amsa masu yace, 'Hakika Ina gaya maku, duk abinda kuka yi wa daya mafi kakanta daga cikin 'yan'uwana a nan ni kuka yi wa.'
41 Alors il dira aussi à ceux qui seront à sa gauche: Allez loin de moi, maudits, au feu éternel, qui a été préparé au diable et à ses anges; (aiōnios )
Sa'annan zai cewa wadanda suke hannunsa na hagu, 'Ku rabu da ni, ku la'anannu, ku tafi cikin wutar jahannama da aka shirya wa Shaidan da aljannunsa, (aiōnios , questioned)
42 Car j’ai eu faim, et vous ne m’avez point donné à manger; j’ai eu soif, et vous ne m’avez point donné à boire;
domin ina jin yunwa baku bani abinci ba; ina jin kishi ba ku bani ruwa ba;
43 J’étais sans asile, et vous ne m’avez point recueilli; nu, et vous ne m’avez point vêtu; malade et en prison, et vous ne m’avez point visité.
Ina bakunci amma baku bani masauki ba; ina huntanci, baku tufasar da ni ba; ina ciwo kuma ina kurkuku, baku kula da ni ba.'
44 Alors, eux aussi lui répondront, disant: Seigneur, quand est-ce que nous vous avons vu ayant faim, ou soif, ou sans asile, ou nu, ou malade, ou en prison, et que nous ne vous avons point assisté?
Sa'annan suma zasu amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa, ko kishin ruwa, ko kana bakunci, ko kana huntanci, ko ciwo, kuma a kurkuku, da bamu yi maka hidima ba?'
45 Alors il leur répondra, disant: En vérité, je vous le dis, chaque fois que vous ne l’avez point fait à l’un de ces petits, à moi non plus, vous ne l’avez point fait.
Sa'annan zai amsa ya ce masu, 'Ina gaya maku hakika abin da baku iya yiwa mafi karanta daga cikin wadannan ba, ba ku yi mani ba.'
46 Et ceux-ci s’en iront à l’éternel supplice, et les justes dans la vie éternelle. (aiōnios )
Wadannan kuwa zasu tafi cikin madawwamiyar azaba amma adalai zuwa rai madawwami.” (aiōnios )