< Matthieu 24 >
1 Et Jésus étant sorti du temple, s’en alla. Alors ses disciples s’approchèrent pour lui faire remarquer les constructions du temple.
Yesu ya fita daga cikin haikalin ya kama hanyar sa. Almajiran sa suka zo suna nuna masa ginin haikali.
2 Mais lui-même, prenant la parole, leur dit: Voyez-vous toutes ces choses? En vérité je vous dis: Il ne restera pas là pierre sur pierre qui ne soit détruite.
Amma ya amsa masu yace, “kun ga dukkan wadannan abubuwan? Ina gaya maku gaskiya, ba ko dutse daya da za'a bari akan dan'uwansa wanda ba za'a rushe shi ba.”
3 Et comme il était assis sur le mont des Oliviers, ses disciples s’approchèrent de lui en particulier, disant: Dites-nous quand ces choses arriveront? et quel sera le signe de votre avènement et de la consommation du siècle? (aiōn )
Yayin da ya zauna a kan dutsen zaitun, almajiran sa suka zo wurin sa a boye suka ce, “me zai zama alamar zuwanka da kuma na karshen duniya?” (aiōn )
4 Et Jésus répondant, leur dit: Prenez garde que quelqu’un ne vous séduise;
Yesu ya amsa yace dasu, “Ku kula kada wani yasa ku kauce.”
5 Car beaucoup viendront en mon nom, disant: Je suis le Christ, et beaucoup seront séduits par eux.
Gama da yawa za su zo da sunana. Za su ce, “ni ne almasihu,” kuma za su sa da yawa su kauce.
6 Vous entendrez parler de combats et de bruits de combats. N’en soyez point troublés, car il faut que ces choses arrivent; mais ce n’est pas encore la fin.
Za ku ji labarin yake-yake da kuma shelar yake-yake. Ku kula kar ku tsorata, domin dole abubuwan nan su faru; amma karshen dai tukunna.
7 Car un peuple se soulèvera contre un peuple, un royaume contre un royaume; et il y aura des pestes et des famines, et des tremblements de terre en divers lieux.
Gama al'umma zata tayarwa al'umma, kuma mulki zai tayarwa mulki. Za'a yi yunwa da girgizar kasa a wurare dabam dabam.
8 Mais toutes ces choses sont le commencement des douleurs.
Amma dukkan wadannan farkon ciwon haihuwa ne kawai.
9 Alors on vous livrera aux tribulations et à la mort, et vous serez en haine à toutes les nations à cause de mon nom.
Bayan haka za'a bada ku ga tsanani a kuma kashe ku. Dukkan al'ummai za su tsane ku saboda sunana.
10 Alors beaucoup se scandaliseront; ils se trahiront et se haïront les uns les autres.
Daga nan da yawa za su yi tuntube, kuma su ci amanar juna, su kuma tsani juna.
11 Beaucoup de faux prophètes aussi s’élèveront, et beaucoup seront séduits par eux.
Annabawan karya da yawa za su taso kuma susa da yawa su kauce.
12 Et parce que l’iniquité aura abondé, la charité d’un grand nombre se refroidira.
Domin mugunta zata ribambanya, kaunar masu yawa zata yi sanyi.
13 Mais celui qui persévérera jusqu’à la fin, celui-là sera sauvé.
Amma duk wanda ya jure har karshe, zai sami ceto.
14 Et cet Evangile du royaume sera prêché dans le monde entier, en témoignage à toutes les nations; et alors viendra la fin.
Za'a yi wa'azin wannan bisharar mulkin a dukkan duniya don ya zama shaida akan dukkan al'ummai. Daganan karshen zai zo.
15 Quand donc vous verrez l’abomination de la désolation, prédite par le prophète Daniel, régnant dans le lieu saint (que celui qui lit entende):
Don haka, idan kun ga abin kyama mai lalatarwa, wanda Annabi Daniyel ya yi maganar sa, Ya tsaya a wuri mai tsarki (bari mai karatu ya fahimta),
16 Alors, que ceux qui sont dans la Judée fuient sur les montagnes;
bari wadanda ke yahudiya su gudu zuwa kan duwatsu,
17 Et que celui qui sera sur le toit ne descende pas pour emporter quelque chose de sa maison:
Bari wanda yake kan bene kada ya sauko don daukar wani abu a cikin gidansa,
18 Et que celui qui sera dans les champs ne revienne pas pour prendre sa tunique.
kuma wanda yake gona kar ya dawo gida domin daukar babbar rigarsa.
19 Mais malheur aux femmes enceintes et à celles qui nourriront en ces jours-là!
Amma kaito ga wadanda suke dauke da yaro, ko masu shayarwa a wannan kwanakin!
20 Priez donc que votre fuite n’arrive pas en hiver, ni en un jour de sabbat.
Ku yi addu'a kada gudun ku ya zama lokacin hunturu, ko ranan asabaci.
21 Car alors la tribulation sera grande, telle qu’il n’y en a point eu depuis le commencement du monde jusqu’à présent, et qu’il n’y en aura point.
Domin za'ayi tsanani mai girma, wanda ba'a taba yin irin shi ba, tun farkon duniya har ya zuwa yau, a'a ba za ayi irin shi ba kuma.
22 Et si ces jours n’eussent été abrégés, nulle chair n’aurait été sauvée; mais à cause des élus, ces jours seront abrégés.
In ba don an rage kwanakin ba, da ba mahalukin da zai tsira. Amma albarkacin zababbun, za a rage kwanakin.
23 Alors, si quelqu’un vous dit: Voici le Christ, ici, ou là, ne le croyez pas.
Sa'annan idan wani yace maku, duba, “ga Almasihu a nan!” ko, “ga Almasihu a can!” kar ku gaskata.
24 Car il s’élèvera de faux Christs et de faux prophètes; et ils feront de grands signes et des prodiges, en sorte que soient induits en erreur (s’il peut se faire) même les élus.
Gama annabawan karya da almasihan karya za su zo suna nuna alamu da al'ajibai, don su yaudari masu yawa zuwa ga bata, in ya yiwuma har da zababbun.
25 Voilà que je vous l’ai prédit.
Kun gani, na gaya maku kafin lokacin ya zo.
26 Si donc on vous dit: Le voici dans le désert, ne sortez point: le voilà dans le lieu le plus retiré de la maison, ne le croyez pas.
Saboda haka, idan suka ce maku, “ga shi a jeji,” kar ku je jejin. Ko, “ga shi a can cikin kuryar daki,” kar ku gaskata.
27 Car, comme l’éclair part de l’orient et apparaît jusqu’à l’occident, ainsi sera l’avènement du Fils de l’homme.
Yadda walkiya ke haskakawa daga gabas zuwa yamma, haka nan zuwan Dan mutum zai zama.
28 Partout où sera le corps, là aussi s’assembleront les aigles.
Duk inda mushe yake, nan ungulai suke taruwa.
29 Mais aussitôt après la tribulation de ces jours, le soleil s’obscurcira, et la lune ne donnera plus sa lumière; les étoiles tomberont du ciel et les vertus des cieux seront ébranlées.
Amma nan da nan bayan kwanakin tsananin nan, rana za ta duhunta, wata kuma ba zai ba da haskensa ba, taurari kuma za su fado daga sama, ikokin sammai za su girgiza.
30 Alors apparaîtra le signe du Fils de l’homme dans le ciel; alors pleureront toutes les tribus de la terre, et elles verront le Fils de l’homme venant dans les nuées du ciel, avec une grande puissance et une grande majesté.
Sa'annan alamar Dan Mutum za ta bayyana a sararin sama, kuma dukkan kabilun duniya za su yi bakin ciki. Za su ga Dan Mutun na zuwa a gajimarai da iko da daukaka mai girma.
31 Et il enverra les anges, qui, avec une trompette et une voix éclatante, rassembleront ses élus des quatre vents de la terre, du sommet des cieux jusqu’à leurs dernières profondeurs.
Zai aiki mala'ikunsa, da karar kaho mai karfi, kuma za su tattara dukkan zababbu daga dukkan kusurwoyi hudu, daga karshen sararin sama har zuwa wani karshen.
32 Apprenez la parabole prise du figuier. Quand ses rameaux sont encore tendres et ses feuilles naissantes, vous savez que l’été est proche.
Kuyi koyi da itacen baure. Da zaran reshen sa ya yi toho ya fara bada ganye, za ku sani bazara ta kusa.
33 Ainsi vous-mêmes, lorsque vous verrez toutes ces choses, sachez que le Christ est proche, à la porte.
Haka kuma, idan kun ga dukkan wadannan abubuwa, ya kamata ku sani, Ya yi kusa, ya na bakin kofa.
34 En vérité je vous dis que cette génération ne passera point jusqu’à ce que toutes ces choses s’accomplissent.
Ina gaya maku gaskiya, wannan zamanin ba zai wuce ba, sai dukkan wadannan abubuwan sun faru.
35 Le ciel et la terre passeront, mais mes paroles ne passeront point.
Sama da kasa za su shude, amma kalmomina ba za su shude ba.
36 Mais pour ce jour et cette heure, personne ne les sait, pas même les anges du ciel; il n’y a que le Père.
Amma game da ranan nan ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai Uban kadai.
37 Et comme aux jours de Noé, ainsi sera l’avènement du Fils de l’homme.
Kamar yadda kwanakin Nuhu suke, haka zai zama game da zuwan Dan Mutum.
38 Car, comme ils étaient aux jours d’avant le déluge, mangeant et buvant, se mariant et mariant leurs enfants, jusqu’au jour où Noé entra dans l’arche,
A wadannan kwankin kafin zuwan ruwan tsufana suna ci suna sha, suna aure suna aurarwa har ranar da Nuhu ya shiga jirgin,
39 Et qu’ils ne reconnurent point de déluge, jusqu’à ce qu’il arriva et les emporta tous: ainsi sera l’avènement même du Fils de l’homme.
ba su san kome ba har ruwan ya zo ya cinye su haka ma zuwan Dan Mutun zai zama.
40 Alors de deux hommes qui seront dans un champ, l’un sera pris et l’autre laissé.
Sa'annan mutane biyu zasu kasance a gona za a dauke daya, a bar daya a baya.
41 De deux femmes qui moudront ensemble, l’une sera prise et l’autre laissée.
Mata biyu na nika a manika za a dauke daya, za a bar dayar.
42 Veillez donc, parce que vous ne savez pas à quelle heure votre Seigneur doit venir.
Don haka sai ku yi zaman tsaro, domin baku san ranar da Ubangijinku zai zo ba.
43 Mais sachez ceci: Si le père de famille savait à quelle heure le voleur doit venir, il veillerait certainement et ne laisserait pas percer sa maison.
Amma ku san wannan, idan maigida ya san lokacin da barawo zai zo, zai zauna a shirye ba zai bar gidan sa har a balle a shiga ba.
44 C’est pourquoi vous aussi, tenez-vous prêts; car vous ignorez l’heure à laquelle le Fils de l’homme doit venir.
Don haka sai ku shirya, domin Dan Mutum zai zo a sa'ar da ba ku yi zato ba.
45 Qui, pensez-vous, est le serviteur fidèle et prudent que son maître a établi sur tous ses serviteurs, pour leur distribuer dans le temps leur nourriture?
To wanene amintaccen bawannan mai hikima, wanda maigidan sa ya sa ya kula mar da gida, domin ya ba su abinci a kan lokaci?
46 Heureux ce serviteur, que son maître, lorsqu’il viendra, trouvera agissant ainsi.
Mai albarka ne bawan, da mai gidan zai same shi a kan aikin sa a lokacin da ya dawo.
47 En vérité, je vous dis qu’il l’établira sur tous ses biens.
Ina gaya maku gaskiya mai gidan zai dora shi a kan dukkan a binda yake da shi.
48 Mais si ce mauvais serviteur dit en son cœur: Mon maître tarde à venir;
Amma idan mugun bawa ya ce a zuciyarsa, “maigida na ya yi jinkiri,”
49 Et qu’il se mette à battre ses compagnons, à manger et à boire avec des ivrognes,
sai ya fara dukan sauran barorin, ya yi ta ci da sha tare da mashaya,
50 Le maître de ce serviteur viendra le jour où il ne s’y attend pas, et à l’heure qu’il ignore;
uban gidan bawan zai dawo a ranar da bawan bai zata ba, a lokacin da bai sani ba.
51 Et il le divisera, et il lui donnera ainsi sa part avec les hypocrites: là sera le pleur et le grincement de dents.
Uban gidansa zai datsa shi biyu, karshen sa zai zama daidai da na munafukai, za a sashi inda a ke kuka da cizon hakora.