< Matthieu 19 >

1 Or, il arriva que lorsque Jésus eut achevé ses discours, il partit de Galilée et vint aux confins de la Judée, au-delà du Jourdain;
Sai ya zama sa'adda Yesu ya gama wadannan maganganu, sai ya bar Galili ya zo kan iyakokin Yahudiya, ketaren kogin Urdun.
2 Et de grandes troupes le suivirent, et il les guérit.
Taro mai yawa suka bi shi, ya kuma warkar da su a wurin.
3 Et les pharisiens s’approchèrent de lui pour le tenter, disant: Est-il permis à un homme de renvoyer sa femme pour quelque cause que ce soit?
Farisawa suka zo wurinsa, suna gwada shi, suka ce masa, ''Ya hallata bisa ga doka mutum ya saki matarsa don kowanne dalili?''
4 Jésus répondant, leur dit: N’avez-vous pas lu que celui qui fit l’homme au commencement, les fit mâle et femelle, et qu’il dit:
Yesu ya amsa ya ce, ''Baku karanta ba, cewa shi wanda ya yi su tun farko ya yi su miji da mace?
5 À cause de cela l’homme quittera son père et sa mère, et s’attachera à sa femme, et ils seront deux dans une seule chair?
Shi wanda ya yi su kuma ya ce, “Saboda wannan dalilin, mutum zai rabu da mahaifinsa da mahaifiyarsa ya hade da matarsa, su biyun su zama jiki daya?”
6 Ainsi ils ne sont plus deux, mais une seule chair. Ce que Dieu donc a uni, que l’homme ne le sépare point.
Su ba biyu ba ne kuma, amma jiki daya. Don haka, duk abin da Allah ya hada, kada wani ya raba.''
7 Ils lui demandèrent: Pourquoi donc Moïse a-t-il commandé de lui donner un acte de répudiation et de la renvoyer?
Sai suka ce masa, ''To me yasa Musa ya umarcemu mu bada takardar saki, mu kuma kore ta?''
8 II leur répondit: Parce que Moïse, à cause de la dureté de votre cœur, vous a permis de renvoyer vos femmes; mais au commencement il n’en fut pas ainsi.
Sai ya ce masu, ''Saboda taurin zuciyarku, shi yasa Musa ya yarda maku ku saki matanku, amma da farko ba haka yake ba.
9 Aussi je vous dis que quiconque renvoie sa femme, si ce n’est pour cause d’adultère, et en épouse une autre, commet un adultère; et celui qui épouse une femme renvoyée se rend adultère.
Ina gaya maku, duk wanda ya saki matarsa in ba saboda zina ba, ya kuma auri wata, yana zina kenan. Wanda kuma ya auri macen da aka saka, yana aikata zina.''
10 Ses disciples lui dirent: Si telle est la condition de l’homme à l’égard de sa femme, il n’est pas bon de se marier.
Almajiran suka ce wa Yesu, ''Idan haka yake game da mutum da matarsa, ba kyau ayi aure ba.''
11 Jésus leur dit: Tous ne comprennent pas cette parole, mais ceux à qui il a été donné.
Amma Yesu yace masu, ''Ba kowa ne zai karbi wannan koyarwa ba, amma sai wadanda an yardar masu su karbe ta.
12 Car il y a des eunuques qui sont nés tels dès le sein de leur mère; il y en a que les hommes ont fait eunuques; et il y en a qui se sont eux-mêmes rendus eunuques, à cause du royaume des cieux. Que celui qui peut comprendre comprenne.
Akwai wadanda aka haife su babanni. Akwai wadanda mutane ne suka maida su babanni. Sa'annan akwai wadanda sun mayar da kansu babanni saboda mulkin sama. Duk wanda zai iya karbar wannan koyarwa, ya karba.''
13 Alors on lui présenta des petits enfants, pour qu’il leur imposât les mains et priât. Or les disciples les rebutaient.
Sai aka kawo masa yara kanana don ya dibiya hannuwansa akansu, yayi masu addu'a, amma almajiran suka kwabe su.
14 Mais Jésus leur dit: Laissez-ces petits enfants et ne les empêchez point de venir à moi; car à de tels appartient le royaume des cieux.
Amma Yesu ya ce masu, ''Ku bar yara kanana, kada ku hana su zuwa wuri na, domin mulkin sama na irinsu ne.''
15 Et lorsqu’il leur eut imposé les mains, il partit de là.
Ya sa hannuwa akan su, sa'annan ya bar wurin.
16 Et voilà que quelqu’un s’approchant, lui dit: Bon maître, que ferai-je de bon pour avoir la vie éternelle? (aiōnios g166)
Sai wani mutum ya zo wurin Yesu, ya ce, ''Malam, wanne ayyuka nagari ne zan yi domin in sami rai madawwami?'' (aiōnios g166)
17 Jésus lui répondit: Pourquoi m’interroges-tu sur ce qui est bon? Dieu seul est bon. Mais si tu veux entrer dans la vie, garde les commandements.
Yesu ya ce masa, ''Me yasa kake tambaya ta game da abin da ke nagari? Daya ne kawai ke nagari, amma idan kana so ka shiga cikin rai, ka kiyaye dokokin.''
18 Lesquels? demanda-t-il. Jésus répondit: Tu ne tueras point: Tu ne commettras point d’adultère: Tu ne déroberas point: Tu ne rendras point de faux témoignage:
Mutumin ya ce masa, ''Wadanne dokokin?'' Yesu ya ce masa, ''Kada kayi kisa, kada kayi zina, kada kayi sata, kada kayi shaidar zur,
19 Honore ton père et ta mère, et aime ton prochain comme toi-même.
ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.''
20 Le jeune homme lui dit: J’ai observé tout cela depuis ma jeunesse; que me manque-t-il encore?
Saurayin nan ya ce masa, ''Ai na kiyaye duk wadannan. Me nake bukata kuma?''
21 Jésus lui dit: Si tu veux être parfait, va, vends ce que tu as et donne-le aux pauvres, et tu auras un trésor dans le ciel; viens ensuite, et suis-moi.
Yesu ya ce masa, ''Idan kana so ka zama cikakke, ka tafi ka sayar da mallakarka, ka kuma ba matalauta, zaka sami dukiya a sama. Sa'annan ka zo ka biyo ni.''
22 Lorsque le jeune homme eut entendu cette parole, il s’en alla triste; car il avait de grands biens.
Amma da saurayin nan ya ji abin da Yesu ya fada, ya koma da bakin ciki, domin shi mai arziki ne kwarai.
23 Alors Jésus dit à ses disciples: En vérité, je vous dis qu’un riche entrera difficilement dans le royaume des cieux.
Yesu ya ce wa almajiransa, ''Hakika ina gaya maku, zai zama da wuya mai arziki ya shiga mulkin sama.
24 Et je vous dis encore: Il est plus facile à un chameau de passer par le chas d’une aiguille, qu’à un riche d’entrer dans le royaume des cieux.
Ina sake gaya maku, zai fi wa rakumi sauki ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.''
25 Or, ces choses entendues, ses disciples s’étonnaient grandement, et disaient: Qui donc pourra être sauvé?
Da almajiran sun ji haka, suka yi mamaki kwarai da gaske, suka ce, ''Wanene zai sami ceto?''
26 Mais Jésus les regardant leur dit: Aux hommes, cela est impossible, mais à Dieu tout est possible.
Yesu ya dube su, ya ce, ''A wurin mutane wannan ba zai yiwu ba, amma a wurin Allah, kome mai yiwuwa ne.''
27 Alors reprenant, Pierre lui dit: Et nous, voici que nous avons tout quitté pour vous suivre: qu’y aura-t-il donc pour nous?
Sai Bitrus ya amsa ya ce masa, ''Duba, mun bar kome da kome mun bi ka. To me za mu samu?''
28 Jésus leur dit: En vérité, je vous dis que vous qui m’avez suivi, lorsqu’à la régénération, le Fils de l’homme sera assis sur le trône de sa gloire, vous aussi, vous serez assis sur douze trônes, jugeant les douze tribus d’Israël.
Yesu ya ce masu, ''Hakika ina gaya maku, ku da kuka bi ni, a sabuwar haihuwa, lokacin da Dan Mutum ya zauna a kursiyin daukakarsa, ku ma zaku zauna a kursiyoyi goma sha biyu, kuna shari'anta kabilu goma sha biyu na Isra'ila.
29 Et quiconque aura quitté ou maison, ou frères, ou sœurs, ou père, ou mère, ou femme, ou fils, ou terre, à cause de mon nom, recevra le centuple, et aura pour héritage la vie éternelle. (aiōnios g166)
Duk wanda ya bar gidaje, 'yan'uwa maza, 'yan'uwa mata, mahaifi, mahaifiya, 'ya'ya, ko gonaki, saboda sunana, zai sami ninkin su dari, ya kuma gaji rai madawwami. (aiōnios g166)
30 Mais beaucoup de premiers seront les derniers, et beaucoup de derniers les premiers.
Amma dayawa dake farko yanzu, za su zama na karshe, dayawa dake karshe kuma, su zama na farko.

< Matthieu 19 >