< Matthieu 18 >
1 En ce moment-là les disciples s’approchèrent de Jésus, disant: Qui, pensez-vous, est le plus grand dans le royaume des cieux?
Daidai wannan lokacin, almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, ''Wanene mafi girma a mulkin sama?''
2 Et Jésus appelant un petit enfant, le plaça au milieu d’eux,
Sai Yesu ya kira karamin yaro gunsa, ya sa shi a tsakaninsu,
3 Et dit: En vérité, je vous le dis, si vous ne vous convertissez, et ne devenez comme les petits enfants, vous n’entrerez point dans le royaume des cieux.
ya ce, ''Hakika ina gaya maku, idan baku juya kun zama kamar kananan yara ba, babu yadda zaku shiga mulkin sama.
4 Quiconque donc se fait petit comme cet enfant, celui-là est le plus grand dans le royaume des cieux.
Saboda haka, duk wanda ya kaskantar da kansa kamar karamin yaron nan, shi ne mafi girma a mulkin sama.
5 Et qui reçoit en mon nom un petit enfant semblable, me reçoit.
Duk wanda ya karbi karamin yaro a suna na, ya karbe ni.
6 Mais celui qui scandalise un de ces petits qui croient en moi, il vaudrait mieux pour lui que l’on suspendît une meule de moulin à son cou, et qu’on le précipitât au profond de la mer.
Amma duk wanda ya sa daya daga cikin 'yan yaran nan da suka gaskanta da ni zunubi, gwamma a rataya dutsen nika a wuyansa a jefa shi cikin zurfin teku.
7 Malheur au monde, à cause des scandales; car il est nécessaire qu’il vienne des scandales: cependant malheur à l’homme par qui le scandale arrive.
Kaiton duniya saboda lokacin tuntube! Lallai ne wadannan lokuta su zo, amma kaiton mutumin da ta wurinsa ne wadannan lokutan za su zo!
8 Si donc, ta main ou ton pied te scandalise, coupe-le, et jette-le loin de toi; il vaut mieux pour toi entrer dans la vie, privé d’une main ou d’un pied, que d’être jeté, ayant deux mains ou deux pieds, dans le feu éternel. (aiōnios )
Idan hannunka ko kafarka ce za ta sa ka tuntube, ka yanke ta, ka yar daga gare ka. Zai fi maka kyau ka shiga rai da nakasa ko gurguntaka, da a jefa ka cikin madawwamiyar wuta tare da hannayenka ko kafafunka. (aiōnios )
9 Et si ton œil te scandalise, arrache-le et le jette loin de toi; il vaut mieux pour toi entrer dans la vie avec un seul œil, que d’être jeté ayant deux yeux dans la géhenne du feu. (Geenna )
Idan idonka zai sa ka tuntube, ka kwakule shi, ka yar. Zai fi maka kyau ka shiga rai da ido daya, da a jefa ka cikin madawwamiyar wuta da idanu biyu. (Geenna )
10 Prenez garde de mépriser un seul de ces petits; parce que, je vous le dis, leurs anges voient sans cesse dans le ciel la face de mon Père qui est dans les cieux.
Ku kula fa kada ku rena kananan nan. Domin koyaushe a sama, mala'ikunsu na duban fuskar Ubana da ke sama.
11 Car le Fils de l’homme est venu sauver ce qui avait péri.
[Dan Mutum ya zo ya ceci abinda ya bata].
12 Que vous en semble? Si quelqu’un a cent brebis, et qu’une d’elles s’égare, ne laisse-t-il pas les quatre-vingt-dix-neuf dans les montagnes, et ne s’en va-t-il pas chercher celle qui s’est égarée?
Menene tunaninku? Idan mutum na da tumaki dari, sa'annan daya ta bata, ashe ba zai bar tassa'in da tara a gefen tudu ya tafi neman wadda ta bata ba?
13 Et s’il arrive qu’il la trouve, en vérité, je vous dis, elle lui donne plus de joie que les quatre vingt-dix-neuf qui ne se sont pas égarées.
In ya same ta, hakika ina gaya maku, farin cikinsa na samun dayan nan da ta bace, zai fi na tassa'in da taran nan da basu bata ba.
14 Ainsi ce n’est pas la volonté de votre Père qui est dans les deux, qu’un seul de ces petits périsse.
Hakanan fa, ba nufin Ubanku dake sama ba ne da ya daga cikin wadannan kananan ya hallaka.
15 Si ton frère a péché contre toi, va et reprends-le entre toi et lui seul: s’il t’écoute, tu auras gagné ton frère;
Idan dan'uwanka yayi maka laifi, fada masa tsakaninku, kai da shi kadai. Idan ya saurare ka, ka maido da dan'uwanka kenan.
16 S’il ne t’écoute point, prends encore avec toi une ou deux personnes, afin que sur la parole de deux ou trois témoins tout soit avéré.
Amma in ya ki ya saurare ka, ka je da 'yan'uwa biyu ko uku su zama shaidu, don ta wurin shaidu biyu ko uku ake tabbatar da kowacce kalma.
17 Que s’il ne les écoute point, dis-le à l’Église; et s’il n’écoute point l’Église, qu’il te soit comme un païen et un publicain.
In kuma ya ki ya saurare su, ka kai lamarin ga ikklisiya. Idan ya ki ya saurari ikklisiya, ka maishe shi ba'al'umme da mai karbar haraji.
18 En vérité, je vous le dis, tout ce que vous lierez sur la terre, sera lié aussi dans le ciel: et tout ce que vous délierez sur la terre, sera délié aussi dans le ciel.
Hakika ina gaya maku, duk abin da kuka daure a duniya, a daure yake a sama. Abin da kuka kwance kuma, a kwance yake a sama.
19 Je vous dis encore, que si deux d’entre vous s’accordent sur la terre, quelque chose qu’ils demandent, il le leur sera fait par mon Père qui est dans les cieux.
Kuma ina gaya maku, idan mutum ku biyu zaku yarda akan duk abin da zaku roka, Ubana wanda ke a sama zai yi maku shi.
20 Car là où deux ou trois sont réunis en mon nom, je suis au milieu d’eux.
Wurin da mutum biyu ko uku suka taru a cikin sunana, zan kasance tare da su.''
21 Alors, s’approchant, Pierre lui dit: Seigneur, combien de fois, mon frère péchant contre moi, lui pardonnerai-je? jusqu’à sept fois?
Bitrus ya zo ya ce wa Yesu, ''Ubangiji, sau nawa ne dan'uwana zai yi mani laifi in gafarta masa? Har sai ya kai sau bakwai?''
22 Jésus lui dit: Je ne te dis pas jusqu’à sept fois, mais jusqu’à septante fois sept fois.
Yesu ya amsa ya ce masa, ''Ban gaya maka sau bakwai ba, amma bakwai din ma har sau saba'in.
23 C’est pourquoi le royaume des cieux est comparé à un homme-roi qui voulut compter avec ses serviteurs.
Saboda haka, za a kwatanta mulkin sama da wani sarki da yake so ya lisafta dukiyarsa dake a hannun barorinsa.
24 Or, lorsqu’il eut commencé à compter, on lui en présenta un qui lui devait dix mille talents.
Da ya fara yin haka, sai aka kawo masa daya daga cikin barorinsa da yake binsa talanti dubu goma.
25 Et comme il n’avait pas de quoi les rendre, son maître ordonna qu’on le vendît, lui, sa femme et ses filles, et tout ce qu’il avait, et qu’on payât.
Amma tunda ba shi da abin biya, ubangidansa ya bada umurni a sayar da shi, tare da matarsa da 'ya'yansa da duk mallakarsa, domin a biya.
26 Mais se jetant à ses pieds, le serviteur le priait, disant: Ayez patience à mon égard, et je vous rendrai tout.
Sai baran ya fadi kasa, ya rusuna a gaban ubangidansa ya ce, “Maigida, kayi mani hakuri, zan biya duk abin da na karba.”
27 Alors le maître de ce serviteur ayant pitié de lui, le renvoya et lui remit sa dette.
Don haka ubangidansa yayi juyayi, sai ya ce, ya yafe bashin, a saki baran.
28 Mais ce serviteur étant sorti, rencontra un de ses compagnons qui lui devait cent deniers; et l’ayant saisi, il l’étouffait, disant: Rends-moi ce que tu dois.
Amma bayan an saki wannan baran, ya je ya sami wani baran kamar sa da yake bi bashin dinari dari. Ya cafke shi, ya shake shi a wuya, ya ce, 'Ka biya bashin da nake bin ka.'
29 Et se jetant à ses pieds, son compagnon le priait, disant: Aie patience à mon égard, et je te rendrai tout.
Amma dan'uwansa bara ya roke shi ya ce, kayi mani hakuri, zan biya ka duk abinda na karba.'
30 Mais lui ne voulut pas; et il s’en alla, et le fit mettre en prison jusqu’à ce qu’il payât sa dette.
Amma baran nan na farko ya ki. A maimakon haka, ya sa aka jefa dan'uwansa bara a kurkuku sai ya biya bashin nan.
31 Voyant ce qui se passait, les autres serviteurs furent grandement contristés; ils vinrent et racontèrent à leur maître tout ce qui s’était fait.
Da sauran barori suka ga abin da ya faru, suka damu kwarai. Sai suka je suka fada wa ubangidansu yadda abin ya faru duka.
32 Alors son maître l’appela, et lui dit: Méchant serviteur, je t’ai remis toute ta dette, parce que tu m’as prié:
Sai ubangidansa ya kirawo shi, ya ce masa, ''Kai mugun bawa, na gafarta maka bashin nan duka, domin ka roke ni.
33 Ne fallait-il donc pas que toi aussi tu eusses pitié de ton compagnon, comme j’ai eu moi-même pitié de toi?
Ashe, bai kamata kaima ka nuna jinkai ga dan'uwanka bara kamar yadda na nuna maka jinkai ba?'
34 Et son maître irrité le livra aux bourreaux, jusqu’à ce qu’il payât toute sa dette.
Ubangidansa yayi fushi, ya danka shi ga masu azabtarwa, har sai ya gama biyan dukan bashin da ake binsa.
35 C’est ainsi que vous traitera aussi mon Père céleste, si chacun de vous ne pardonne à son frère du fond de son cœur.
Hakanan Ubana dake a sama zai yi maku, idan kowannenku bai gafarta wa dan'uwansa daga zuciya ba.''