< Ézéchiel 36 >
1 Mais toi, fils d’un homme, prophétise sur les montagnes d’Israël, et tu diras: Montagnes d’Israël, écoutez la parole du Seigneur;
“Ɗan mutum, ka yi annabci wa duwatsun Isra’ila ka ce, ‘Ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji.
2 Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Parce que l’ennemi a dit de vous: Très bien, des hauteurs éternelles nous ont été données pour héritage;
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa abokin gāba yana magana game da ku cewa, “Yauwa! Tsofaffin tuddai sun zama mallakarmu yanzu.”’
3 À cause de cela, prophétise, et dis: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Parce que vous avez été désolées et foulées aux pieds de tous côtés, et que vous avez été l’héritage des autres nations, et que vous êtes devenues la raillerie et l’opprobre du peuple;
Saboda haka ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin sun lalace ku suka kuma maishe ku kufai marar amfani a kowane gefe saboda ku zama mallakar sauran al’ummai da kuma abin magana da tsegumi ga mutane,
4 À cause de cela, montagnes d’Israël, écoutez la parole du Seigneur Dieu aux montagnes et aux collines, aux torrents, et aux vallées, et aux déserts, aux maisons ruinées, et aux villes abandonnées qui ont été dépeuplées et insultées par les autres nations d’alentour;
saboda haka, ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana faɗa wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, wa kufai da garuruwan da suka zama kango waɗanda aka washe aka wulaƙanta suka zama ganimar sauran al’ummai da suke kewaye da ku,
5 À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur Dieu: Puisque dans le feu de mon zèle j’ai parlé contre les autres nations et contre toute l’Idumée, qui se sont attribué ma terre comme un héritage, avec joie, et de tout leur coeur et de toute leur âme, et qui l’ont dépeuplée pour la ravager.
ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa cikin kishina mai ƙuna na yi magana gāba da sauran al’ummai, da kuma gāba da Edom, gama da farin ciki da reni a zukatansu suka mai da ƙasata mallakarsu don su washe wuraren kiwonta.’
6 En ce cas, prophétise sur la terre d’Israël, et tu diras aux montagnes, aux collines, et aux coteaux et aux vallées: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Voilà que moi j’ai parlé dans mon zèle et dans ma fureur, parce que vous avez été couverts de confusion par les nations.
Saboda haka ka yi annabci game da ƙasar Isra’ila ka kuma ce wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ga shi, na yi magana da kishina da hasalata saboda sun sha zargi wurin al’ummai.
7 C’est pourquoi voici ce que dit le Seigneur Dieu: Moi, j’ai levé ma main, afin que les nations qui sont autour de vous portent elles-mêmes leur confusion.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa na ɗaga hannuna sama na rantse cewa al’ummai da suke kewaye da ku za su sha ba’a.
8 Et vous, montagnes d’Israël, poussez vos branches et portez votre fruit pour mon peuple Israël; car il est près de venir;
“‘Amma ku, ya duwatsun Isra’ila, za ku miƙa rassanku ku ba da amfani ga mutanena Isra’ila, gama ba da daɗewa ba za su komo gida.
9 Parce que voici que je viens vers vous, et que je me retournerai vers vous; et que vous serez labourées, et que vous recevrez la semence.
Na damu da ku kuma zan dube ku da tausayi; za ku nome ku kuma shuka,
10 Et je multiplierai en vous les hommes, et j’y ferai croître toute la maison d’Israël; et les cités seront habitées, et les lieux ruinés seront rétablis.
zan kuma riɓaɓɓanya mutane a kanku, dukan gidan Isra’ila ke nan. Za a zauna a birane a kuma sāke gina rusassun wurare.
11 Et je vous remplirai d’hommes et de bêtes; et ils se multiplieront et ils croîtront; et je vous ferai habiter comme dès le principe, je vous donnerai de plus grands biens que vous n’en avez eu au commencement, et vous saurez que je suis le Seigneur.
Zan sa mutane da dabbobi su yi yawa a kanku, za su kuma ba da’ya’ya su kuma yi yawa. Zan zaunar da mutane a kanku kamar dā zan kuma sa ku wadaita fiye da dā. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
12 Et j’amènerai sur vous des hommes, mon peuple Israël; et ils te posséderont comme leur héritage, et tu ne seras plus de nouveau sans eux.
Zan sa mutanena Isra’ila su yi tafiya a kanku. Za su mallake ku, za ku kuma zama gādonsu; ba za ku ƙara sa su rasa’ya’yansu ba.
13 Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Parce qu’on a dit de vous: Tu dévores les hommes, tu étouffes ta propre nation;
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin mutane suna magana game da ku cewa, “Kun cinye mutane kuka kuma sa al’ummarku ta rasa’ya’yanta,”
14 À cause de cela, tu ne dévoreras plus les hommes, et tu ne détruiras plus ta nation, dit le Seigneur Dieu.
saboda haka ba za ku ƙara cinye mutane ko ku sa al’ummarku ta rasa’ya’ya ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Je ne ferai plus entendre en toi la confusion dont te couvraient les nations, et tu ne porteras en aucune manière l’opprobre des peuples; et tu ne perdras plus ta nation, dit le Seigneur Dieu.
Ba zan ƙara bari ku ji maganar banza ta al’ummai ba, ba kuwa za ku ƙara shan ba’ar mutane ko in sa al’ummarku ta fāɗi ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
16 Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
Maganar Ubangiji ta sāke zuwa mini cewa,
17 Fils d’un homme, les enfants d’Israël ont habité dans leur terre; ils l’ont souillée par leurs voies et par leurs affections; comme est l’impureté de la femme qui a ses mois, ainsi est devenue leur voie devant moi.
“Ɗan mutum, sa’ad da mutanen Isra’ila suke zama a ƙasarsu, sun ƙazantar da ita ta wurin halinsu da kuma ayyukansu. Halinsu ya yi kamar rashin tsarkin mace a lokacin al’adarta a gabana.
18 Aussi ai-je répandu mon indignation sur eux, à cause du sang qu’ils ont versé sur la terre, et à cause de leurs idoles, par lesquelles ils l’ont souillée.
Saboda haka na husata da su domin sun yi kisankai a ƙasar kuma domin sun ƙazantar da ita da gumakansu.
19 Et je les ai dispersés parmi les nations, et ils ont été jetés au vent dans les divers pays; et selon leurs voies et leurs inventions, je les ai jugés.
Na warwatsa su cikin al’ummai, suka kuwa warwatsu cikin dukan ƙasashe; na hukunta su gwargwadon halinsu da ayyukansu.
20 Ils sont entrés chez les nations vers lesquelles ils étaient allés et ils ont souillé mon saint nom, lorsqu’on disait d’eux: C’est le peuple du Seigneur, et c’est de sa terre qu’ils sont sortis.
Kuma ko’ina da suka tafi a cikin al’ummai sun ɓata sunana mai tsarki, gama an yi magana a kansu cewa, ‘Waɗannan mutanen Ubangiji ne, duk da haka dole su bar ƙasarsa.’
21 Et j’ai épargné la sainteté de mon nom, qu’avait souillé la maison d’Israël parmi les nations chez lesquelles ils entrèrent.
Na damu saboda sunana mai tsarki, wanda gidan Isra’ila ya ɓata a cikin al’ummai inda suka tafi.
22 C’est pour cela que tu diras à la maison d’Israël: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Ce n’est pas à cause de vous, maison d’Israël, que j’agirai, mais c’est à cause de mon nom saint que vous avez souillé parmi les nations chez lesquelles vous êtes entrés.
“Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba dominku ba ne, ya gidan Isra’ila da nake yin waɗannan abubuwa, amma saboda sunana ne mai tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al’ummai inda kuka tafi.
23 Et je sanctifierai mon grand nom, qui a été souillé parmi les nations et que vous avez souillé au milieu d’elles; afin que les nations sachent que je suis le Seigneur, dit le Seigneur des armées, lorsque j’aurai été sanctifié parmi vous devant eux.
Zan nuna tsarkin girman sunana, wanda aka ɓata a cikin al’umma, sunana da kuka ɓata a cikinsu. Sa’an nan al’ummai za su san cewa ni ne Ubangiji, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinku a idanunsu.
24 Car je vous retirerai d’entre les nations, et je vous rassemblerai de tous les pays, et je vous ramènerai dans votre terre.
“‘Gama zan fitar da ku daga al’ummai; zan tattara ku daga dukan ƙasashe in komo da ku zuwa ƙasarku.
25 Et je répandrai sur vous une eau pure, et vous serez purifiés de toutes vos souillures, et je vous purifierai de toutes vos idoles.
Zan yayyafa muku ruwa mai tsabta, zan kuwa tsarkake ku daga dukan ƙazantarku daga kuma dukan gumakanku.
26 Et je vous donnerai un cœur nouveau, et je mettrai un esprit nouveau au milieu de vous; et j’ôterai le cœur de pierre de votre chair, et je vous donnerai un cœur de chair.
Zan ba ku sabuwa zuciya in kuma sa sabon ruhu a cikinku; zan fid da zuciyar dutse in kuma ba ku zuciyar nama.
27 Et mon esprit, je le mettrai au milieu de vous; et je ferai que vous marchiez dans mes préceptes, et que vous gardiez mes ordonnances, et que vous les pratiquiez.
Zan kuma sa Ruhuna a cikinku in kuma motsa ku ku bi ƙa’idodina ku kuma kiyaye dokokina.
28 Et vous habiterez dans la terre que j’ai donnée à vos pères: vous serez mon peuple, et moi je serai votre Dieu.
Za ku zauna a ƙasar da na ba wa kakanninku; za ku zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
29 Et je vous délivrerai de toutes vos souillures; et j’appellerai le froment, et je le multiplierai, et je ne ferai plus peser sur vous la famine.
Zan cece ku daga dukan rashin tsabtarku. Zan sa hatsi ya yi yalwa ba zan kawo yunwa a kanku ba.
30 Je multiplierai le fruit des arbres et les productions des champs, afin que vous ne portiez plus l’opprobre de la famine devant les nations.
Zan ƙara’ya’yan itatuwa da amfanin gona, saboda kada ku ƙara shan kunya a cikin al’ummai saboda yunwa.
31 Et vous vous souviendrez de vos voies très mauvaises et de vos affections déréglées; et vos crimes et vos iniquités vous déplairont.
Sa’an nan za ku tuna mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda zunubanku da kuma ayyukanku na banƙyama.
32 Ce n’est pas à cause de vous que j’agirai, dit le Seigneur Dieu, sachez-le; soyez confus et rougissez de vos voies, maison d’Israël.
Ina so ku san cewa ba na yi wannan saboda ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku ji kunya ku kuma giggita saboda halinku, ya gidan Isra’ila!
33 Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Le jour auquel je vous aurai purifiés de toutes vos iniquités, et que j’aurai fait habiter vos villes, et que j’aurai rétabli les lieux ruinés;
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na tsarkake ku daga dukan zunubanku, zan sāke zaunar da ku a garuruwanku, a kuma sāke gina kufai.
34 Et qu’aura été bien cultivée la terre qui était autrefois déserte et désolée aux yeux du voyageur,
Ƙasar da take kango a dā za ku nome ta a maimakon zama kango a idon dukan masu ratsawa a cikinta.
35 On dira: Cette terre inculte est devenue comme un jardin de délices; et les cités désertes, et abandonnées, et démolies, sont fortifiées.
Za su ce, “Wannan ƙasar da take kango a dā ta zama kamar lambu Eden; biranen da dā suke kufai, kango da kuma aka lalata, yanzu suna da katanga ana kuma zama a ciki.”
36 Et toutes les nations qui seront restées au tour de vous, sauront que c’est moi le Seigneur qui ai rétabli les lieux ruinés, planté les champs incultes, que c’est moi le Seigneur qui ai parlé et exécuté.
Sa’an nan al’ummai kewaye da ku da suka rage za su san cewa Ni Ubangiji na sāke gina abin da aka lalace na kuma sāke shuka abin da yake kango. Ni Ubangiji na faɗa, kuma zan aikata.’
37 Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Encore en ceci, les enfants de la maison d’Israël me trouveront disposé à agir pour eux; je les multiplierai comme un troupeau d’hommes;
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa har yanzu zan ji roƙon gidan Isra’ila in kuma yi musu wannan. Zan sa mutanensu su yi yawa kamar tumaki,
38 Comme un troupeau saint, comme le troupeau de Jérusalem dans ses solennités; c’est ainsi que les cités désertes seront remplies de troupeaux d’hommes; et ils sauront que je suis le Seigneur.
yawansu ya yi kamar garken tumaki don hadaya a Urushalima a ƙayyadaddun lokuta bukukkuwarta. Haka biranen da suke kufai za su cika da ɗumbun mutane. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”