< 2 Samuel 1 >
1 Or, il arriva, après que Saül fut mort, que David revint de la défaite d’Amalec, et qu’il demeura à Siceleg pendant deux jours.
Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
2 Mais au troisième jour, il parut un homme, venant du camp de Saül, le vêtement déchiré et la tête couverte de poussière; et dès qu’il arriva auprès de David, il tomba sur sa face, et se prosterna.
A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
3 Et David lui demanda: D’où viens-tu? Celui-ci lui répondit: Je me suis échappé du camp d’Israël.
Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
4 David lui demanda encore: Qu’est-ce qui a été fait? Apprends-le moi. Il répondit: Le peuple s’est enfui de la bataille, et beaucoup d’entre le peuple, ayant succombé, sont morts; et Saül même et Jonathas son fils ont péri.
Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
5 Et David dit au jeune homme qui lui apportait la nouvelle: D’où sais-tu que Saül est mort, et Jonathas son fils?
Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
6 Et le jeune homme qui lui apportait la nouvelle lui répondit: Je suis venu par hasard sur la montagne de Gelboé, et Saül était appuyé sur sa lance; or, les chariots et les cavaliers s’avançaient vers lui,
Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
7 Et s’étant retourné, et me voyant, il m’a appelé. Et quand je lui eus répondu: Me voici,
Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
8 Il me demanda: Qui es-tu? Et je lui répondis: Je suis Amalécite.
“Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
9 Alors il me dit: Jette-toi sur moi, et tue-moi, parce que je suis en proie aux angoisses, et que toute mon âme est encore en moi.
“Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
10 Me jetant donc sur lui, je le tuai; car je savais qu’il ne pouvait pas vivre après son désastre; alors je pris le diadème qui était sur sa tête, et le bracelet de son bras, et je les apportai ici à vous, mon seigneur.
“Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
11 Mais David prenant ses vêtements, les déchira; ce que firent aussi tous les hommes qui étaient avec lui.
Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
12 Et ils furent dans le deuil, et ils pleurèrent et ils jeûnèrent jusqu’au soir, au sujet de Saül, de Jonathas, son fils, du peuple du Seigneur et de la maison d’Israël, parce qu’ils avaient succombé au glaive.
Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
13 Et David dit au jeune homme qui lui avait apporté la nouvelle: D’où es-tu? Il répondit: Je suis fils d’un étranger, d’un Amalécite.
Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
14 Et David lui dit: Pourquoi n’as-tu pas craint de lever ta main, pour tuer le christ du Seigneur?
Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
15 Et David appelant un de ses serviteurs, dit: Approche-toi, jette-toi sur lui. Le serviteur le frappa, et il mourut,
Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
16 Et David ajouta: Ton sang sur ta tête! car ta bouche a parlé contre toi, disant: C’est moi qui ai tué le christ du Seigneur.
Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
17 Alors David fit entendre cette complainte sur Saül et sur Jonathas, son fils
Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
18 (Et il ordonna qu’on enseignât l’arc aux enfants de Juda, comme il est écrit dans le Livre des Justes), et il dit: Considère, ô Israël, ceux qui sont morts sur tes hauts lieux, couverts de blessures.
Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
19 Les illustres, ô Israël, ont été tués sur tes montagnes: comment des forts sont-ils tombés?
“Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
20 Ne l’annoncez pas dans Geth, ne l’annoncez pas dans les carrefours d’Ascalon, de peur que les filles des Philistins ne se livrent à la joie, et que les filles des incirconcis ne bondissent d’allégresse.
“Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
21 Montagnes de Gelboé, que ni pluie, ni rosée ne viennent sur vous: qu’il n’y ait point de champs de prémices, parce que là a été jeté un bouclier de forts, le bouclier de Saül, comme s’il n’avait pas été oint avec l’huile.
“Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
22 La flèche de Jonathas n’est jamais retournée en arrière, sans avoir du sang de ceux qui ont été tués, et de la graisse des forts, et le glaive de Saül n’est pas revenu en vain.
“Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
23 Saül et Jonathas, aimables et beaux dans leur vie, même à leur mort, n’ont pas été séparés; plus rapides que des aigles, plus forts que des lions.
Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
24 Filles d’Israël, pleurez sur Saül, qui vous revêtait d’écarlate au milieu des délices, et vous fournissait de l’or pour votre parure.
“Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
25 Comment des forts sont-ils tombés dans la bataille? Jonathas a été tué sur tes hauteurs.
“Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
26 Je pleure sur toi, mon frère, Jonathas, de la plus grande beauté, aimable au-dessus de l’amour des femmes. Comme une mère aime son fils unique, ainsi moi je te chérissais.
Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
27 Comment des forts sont-ils tombés, et des armes guerrières ont-elles péri?
“Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”