< 1 Samuel 1 >
1 Il y eut un homme de Ramathaïmsophim, de la montagne d’Ephraïm, et son nom était Elcana, fils de Jéroam, fils d’Eliu, fils de Thohu, fils de Suph: il était Ephrathéen;
Akwai wani mutum daga Ramatayim, mutumin Zuf daga ƙasar tuddan Efraim, sunansa Elkana, ɗan Yeroham, shi jikan Elihu ɗan Tohu, tattaɓa kunnen Zuf, mutumin Efraim.
2 Et il avait deux femmes; le nom d’une était Anne, et le nom de la seconde Phénenna. Or Phénenna eut des fils, mais Anne n’avait pas d’enfants.
Yana da mata biyu, ɗaya sunanta Hannatu, ɗayan kuwa ana kiranta Feninna. Ita Feninna tana da’ya’ya, amma Hannatu ba ta da’ya’ya.
3 Et cet homme montait de sa ville aux jours prescrits, pour adorer et sacrifier au Seigneur des armées à Silo. Or il y avait là les deux fils d’Héli, Ophni et Phinéès, prêtres du Seigneur.
Shekara-shekara wannan mutum yakan haura daga garinsa zuwa Shilo domin yin sujada da miƙa hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki. A can kuwa’ya’yan Eli maza biyu, Hofni da Finehas su ne firistoci na Ubangiji.
4 Vint donc le jour, et Elcana offrit un sacrifice, et il donna des portions à Phénenna, sa femme, et à tous ses fils et à ses filles;
Duk sa’ad da rana ta kewayo don Elkana yă miƙa hadaya, yakan ba da kashin nama ga matarsa Feninna da dukan’ya’yanta maza da mata.
5 Mais à Anne il donna une seule portion avec tristesse, parce qu’il chérissait Anne. Or, le Seigneur l’avait frappée de stérilité.
Amma Hannatu kuwa sai yă ba ta babban rabo gama yana ƙaunarta ko da yake Ubangiji ya kulle mahaifarta.
6 Sa rivale l’affligeait aussi et la tourmentait violemment, au point de lui reprocher que le Seigneur l’avait frappée de stérilité.
Saboda Ubangiji ya kulle mahaifarta, sai kishiyarta ta dinga tsokanarta don tă ba ta haushi.
7 C’est ainsi qu’elle faisait chaque année, lorsque, le temps revenant, ils montaient au temple du Seigneur, et c’est ainsi qu’elle la provoquait. Or, Anne pleurait et ne prenait pas de nourriture.
Wannan ya ci gaba shekara da shekaru. Duk lokacin da Hannatu ta haura zuwa haikalin Ubangiji, sai kishiyarta tă tsokane ta har tă yi ta kuka tă kuma ƙi cin abinci.
8 Elcana, son mari, lui dit donc: Anne, pourquoi pleures-tu? d’où vient que tu ne manges pas? et pour quel motif ton cœur est-il affligé? Est-ce que moi je ne vaux pas mieux pour toi que dix fils?
Elkana mijinta kuwa yakan ce mata, “Hannatu don me kike kuka? Me ya sa ba za ki ci abinci ba? Don me kika karaya? Ashe, ban fi’ya’ya goma a gare ki ba?”
9 Mais Anne se leva après qu’elle eut mangé et bu à Silo. Et, Héli, le prêtre, étant assis sur son mari, lui dit donc: Anne, pourquoi pleures-tu? d où vient que tu ne manges pas? et pour quel motif ton cœur est-il affligé? Est-ce que moi je ne vaux pas mieux pour toi que dix fils?
Wata rana sa’ad da suka gama ci da sha a Shilo, Hannatu ta miƙe tsaye. Eli firist kuwa yana zaune a kujera a bakin ƙofar haikalin Ubangiji.
10 Mais Anne se leva après qu’elle eut mangé et bu à Silo. Et, Héli, le prêtre, étant assis sur son siège devant la porte du temple du Seigneur,
A cikin baƙin ciki, Hannatu ta yi kuka mai zafi ta yi addu’a ga Ubangiji.
11 Anne, qui avait le cœur dans l’amertume, adressa des prières au Seigneur, pleurant abondamment,
Ta yi ta cewa, “Ya Ubangiji Maɗaukaki. In har ka dubi baƙin cikin baiwarka, ka tuna da ni, ba ka kuma manta da baiwarka ba, amma ka ba ta ɗa, ni ma zan miƙa shi ga Ubangiji dukan rayuwarsa, aska kuwa ba za tă taɓa kansa ba.”
12 Et elle voua un vœu, disant: Seigneur des armées, si abaissant votre regard, vous voyez l’affliction de votre servante, si vous vous souvenez de moi; si vous n’avez pas oublié votre servante, et que vous donniez à votre esclave un enfant mâle, je le donnerai au Seigneur pour tous les jours de sa vie, et le rasoir ne montera jamais sur sa tête.
Yayinda take addu’a ga Ubangiji, Eli ya lura da bakinta.
13 Or, il arriva, que, comme elle multipliait ses prières devant le Seigneur, Héli observait sa bouche.
Hannatu tana addu’a a zuci, ba a jin muryarta, sai leɓunanta ne kawai suna motsi. Eli kuwa ya yi tsammani ta bugu ne.
14 Mais Anne parlait en son cœur, ses lèvres seules étaient en mouvement, et sa voix n’était pas du tout entendue. Héli donc la jugea ivre,
Sai ya ce mata, “Har yaushe za ki ci gaba da maye? Ki daina shan ruwan inabi.”
15 Et il lui dit: Jusqu’à quand seras-tu ivre? Laisse reposer quelque temps le vin qui t’enivre.
Hannatu ta ce, “Ba haka ba ne, ranka yă daɗe, ni mace ce da take cikin matsala ƙwarai da gaske. Ban sha ruwan inabi ba, ko wani abu mai sa maye, ina dai faɗa wa Ubangiji abin da yake damuna ne.
16 Anne répondant: Nullement, dit-elle, mon seigneur; car je suis une femme très malheureuse; le vin et tout ce qui peut enivrer, je n’en ai pas bu; mais j’ai répandu mon âme en la présence du Seigneur.
Kada ka yi zato baiwarka’yar iska ce. Ina addu’a a nan saboda yawan azaba da baƙin cikin da nake ciki.”
17 Ne prenez pas votre servante pour une des filles de Bélial; parce que c’est dans l’excès de ma douleur et de mon affliction que j’ai parlé jusqu’à présent.
Eli ya ce, “In haka ne, to, ki sauka lafiya, Allah na Isra’ila kuma yă ba ki abin da kika roƙa daga gare shi.”
18 Alors Héli lui répliqua: Va en paix, et que le Dieu d’Israël t’accorde la demande que tu lui as faite.
Ta ce, bari baiwarka tă sami tagomashi a idonka. Sai ta yi tafiyarta ta je ta ci wani abu, fuskarta kuwa ba tă ƙara kasance da baƙin ciki ba.
19 Et Anne répondit: Plût à Dieu que votre servante trouvât grâce à vos yeux! Et la femme s’en alla en son chemin; elle mangea, et ses traits n’éprouvèrent plus aucun changement.
Kashegari da sassafe suka tashi suka yi sujada a gaban Ubangiji, sai suka koma garinsu a Rama. Elkana kuwa ya kwana da matarsa Hannatu, Ubangiji kuma ya tuna da ita.
20 Après cela, ils se levèrent le matin, et ils adorèrent devant le Seigneur; puis ils s’en retournèrent et vinrent dans leur maison à Ramatha. Or, Elcana connut Anne sa femme, et le Seigneur se souvint d’elle.
Ana nan sai Hannatu ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa. Ta ba shi suna Sama’ila; tana cewa, “Domin na roƙe shi daga wurin Ubangiji.”
21 Et, il arriva qu’après une révolution de jours, Anne conçut, puis enfanta un fils, et elle lui donna le nom de Samuel, parce qu’elle l’avait demandé au Seigneur.
Da shekara ta kewayo, sai Elkana da iyalinsa suka sāke tafi Shilo domin su yi hadaya ga Ubangiji, yă kuma cika alkawarin da ya yi.
22 Or, Elcana, son mari, monta au temple, ainsi que toute sa maison, pour immoler au Seigneur l’hostie solennelle, et s’acquitter de son vœu;
Hannatu kuwa ba tă bi su ba. Ta gaya wa mijinta cewa, “Sai bayan na yaye yaron, zan kai shi in miƙa shi a gaban Ubangiji, yă kuma kasance a wurin koyaushe.”
23 Mais Anne n’y monta point; car elle dit à son mari: Je n’irai pas, jusqu’à ce que l’enfant soit sevré, et que je le conduise, afin qu’il paraisse en la présence du Seigneur, et qu’il y demeure perpétuellement.
Elkana mijinta ya ce mata, “Ki yi abin da kika ga ya fi miki kyau. Ki jira har sai bayan kin yaye shi. Ubangiji dai ya cika maganarsa.” Saboda haka matar ta tsaya a gida, ta yi ta renon ɗanta har ta yaye shi.
24 Et Elcana, son mari, lui répondit: Fais ce qui le semble bon, et demeure jusqu’à ce que tu le sèvres; et je prie pour que le Seigneur accomplisse sa parole. Sa femme demeura donc, et elle allaita son fils, jusqu’à ce qu’elle le sevrât.
Bayan ta yaye shi, sai ta ɗauki yaron tare da bijimi bana uku, da mudun gari, da salkan ruwan inabi, ta kawo su a gidan Ubangiji a Shilo.
25 Et elle l’amena avec elle, après qu’elle l’eut sevré, en prenant trois veaux, trois boisseaux de farine et une cruche de vin; ainsi elle l’amena dans la maison du Seigneur à Silo. Or, l’enfant était encore un tout petit enfant.
Bayan an yanka bijimin, sai suka kawo yaron wurin Eli.
26 Et ils immolèrent le veau, et présentèrent l’enfant à Héli.
Sai ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ba ka gane ni ba? Ai, ni ce matar da ta taɓa tsayawa a gabanka, tana addu’a ga Ubangiji.
27 Et Anne dit: Je vous conjure, mon seigneur, votre âme vit, seigneur! c’est moi qui suis cette femme qui me suis tenue devant vous ici, priant le Seigneur.
Wannan yaron ne na roƙa daga wurin Ubangiji, ya kuwa ba ni abin da na roƙa daga gare shi.
28 C’est pour cet enfant que j’ai prié, et le Seigneur m’a accordé ma demande que je lui ai faite. C’est pour cela aussi que moi je l’ai donné au Seigneur, pour tous les jours pour lesquels il aura été donné au Seigneur. Ainsi ils adorèrent là le Seigneur, et Anne pria et dit:
Saboda haka, na ba da shi ga Ubangiji muddin ransa, zai zama na Ubangiji.” A can kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.