< Luc 23 >

1 Puis toute l'assemblée, s'étant levée, le mena devant Pilate.
Sai dukan majalisa suka tashi, suka kai shi gaban Bilatus.
2 Alors ils se mirent à l'accuser, en disant: Nous avons trouvé cet homme soulevant notre nation, défendant de payer le tribut à César, et se disant le Christ, le Roi.
Suka fara zarginsa suna cewa, “Mun sami wannan mutum yana rikitar da al’ummarmu. Yana hana a biya haraji ga Kaisar. Yana kuma cewa, shi Kiristi ne, sarki kuma.”
3 Pilate lui demanda: C'est toi qui es le roi des Juifs? Jésus lui répondit: Tu le dis!
Sai Bilatus ya tambayi Yesu ya ce, “Kai ne sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
4 Alors Pilate dit aux principaux sacrificateurs et au peuple: Je ne trouve rien de criminel en cet homme.
Sai Bilatus ya sanar wa manyan firistoci da taron ya ce, “Ni fa, ban sami wani ainihin abin zargi game wannan mutum nan ba.”
5 Mais ils insistaient plus fortement en disant: Il soulève le peuple, en enseignant dans toute la Judée; après avoir commencé par la Galilée, il est venu jusqu'ici.
Amma suka nace, suna cewa, “Yana tā da hankulan mutane, ko’ina a Yahudiya da koyarwarsa. Ya fara daga Galili, ga shi har ya kai nan.”
6 Lorsque Pilate entendit cela, il demanda si cet homme était Galiléen.
Da Bilatus ya ji haka, sai ya yi tambaya, “Ko shi mutumin Galili ne?”
7 Apprenant que Jésus était de la juridiction d'Hérode, il le renvoya à Hérode, qui se trouvait aussi à Jérusalem en ces jours-là.
Da ya ji cewa, Yesu yana ƙarƙashin mulkin Hiridus ne, sai ya aika da shi zuwa wurin Hiridus, don a lokacin Hiridus yana Urushalima.
8 Quand Hérode vit Jésus, il eut une grande joie; car depuis longtemps il désirait le voir, à cause de ce qu'il avait entendu dire de lui, et il espérait qu'il lui verrait faire quelque miracle.
Da Hiridus ya ga Yesu, sai ya yi murna ƙwarai, don tun dā ma yana marmari ya gan shi a kan abin da ya ji game da shi. Ya yi fata ya ga Yesu, yă kuma yi waɗansu ayyukan banmamaki.
9 Il lui adressa donc plusieurs questions; mais Jésus ne lui répondit rien.
Ya yi masa tambayoyi masu yawa, amma Yesu bai ba shi ko amsa ba.
10 Et les principaux sacrificateurs et les scribes étaient là, qui l'accusaient avec véhémence.
Manyan firistoci da malaman dokoki suna tsaye a wurin, suna kawo zargi masu ƙarfi a kansa.
11 Alors Hérode, ainsi que les gens de sa garde, le traita avec mépris et se moqua de lui; puis, après l'avoir revêtu d'un manteau éclatant, il le renvoya à Pilate.
Sai Hiridus da sojojinsa suka wulaƙanta shi, suka yi masa ba’a. Sa’an nan, suka sa masa babban riga, suka mai da shi wurin Bilatus.
12 Ce jour-là même, Pilate et Hérode devinrent amis, d'ennemis qu'ils étaient auparavant.
A ranar, Hiridus da Bilatus suka zama abokan juna, don tun dā ma, su abokan gāba ne.
13 Pilate, ayant réuni les principaux sacrificateurs, les magistrats et le peuple, leur dit:
Bilatus ya tara manyan firistoci, da masu mulki, da mutane,
14 Vous m'avez amené cet homme, l'accusant de soulever le peuple; et cependant, après l'avoir interrogé en votre présence, je ne l'ai trouvé coupable d'aucun des crimes dont vous l'accusez,
ya ce musu, “Kun kawo mini wannan mutum, a matsayin wanda yana zuga mutane su yi tawaye. Na bincike shi a gabanku, ban ga a kan me kuka kawo kararsa ba.
15 ni Hérode non plus, puisqu'il nous l'a renvoyé: il n'a donc rien fait qui mérite la mort.
Haka ma Hiridus, shi ya sa ya dawo da shi nan wurinmu. Kamar yadda ku ma kun gani, ba abin da mutumin nan ya yi, da ya isa mutuwa.
16 Ainsi, après l'avoir fait châtier, je le relâcherai.
Saboda haka, zan yi masa bulala, in sāke shi.”
17 [Or, à chaque fête, Pilate était obligé de leur relâcher un prisonnier].
18 Alors ils se mirent à crier tous ensemble: Fais mourir celui-ci, et relâche-nous Barabbas!
Suka yi ihu gaba ɗaya suka ce, “A yi gaba da wannan mutum! A sake mana Barabbas!”
19 Or, cet homme avait été mis en prison pour une sédition qui avait eu lieu dans la ville, et pour un meurtre.
(Barabbas yana kurkuku saboda laifin tā da hankali a birnin, da kuma don kisankai.)
20 Pilate leur parla de nouveau, dans le dessein de délivrer Jésus.
Sai Bilatus ya sāke yin musu magana don yana so ya saki Yesu.
21 Mais ils crièrent; Crucifie-le! crucifie-le!
Amma sai suka ci gaba da ihu, suna cewa, “A gicciye shi! A gicciye shi!”
22 Il leur dit pour la troisième fois: Quel mal a-t-il donc fait? Je n'ai rien trouvé en lui qui mérite la mort. Ainsi, après l'avoir fait châtier, je le relâcherai.
Ya sāke ce musu, sau na uku, “Don me? Wane laifi wannan mutum ya yi? Ni dai ban same shi da wani dalilin da ya isa a kashe shi ba. Saboda haka, zan sa a hore shi, sa’an nan in sāke shi.”
23 Mais ils insistaient, demandant à grands cris qu'il fût crucifié, et leurs clameurs l'emportèrent.
Amma suna ihu, suna nacewa, suna cewa, dole a gicciye shi, har ihunsu ya rinjaye shi.
24 Pilate prononça la sentence qui répondait à leur désir.
Sai Bilatus ya biya bukatarsu da ya ji roƙonsu.
25 Il relâcha donc celui qui avait été mis en prison pour sédition et pour meurtre, et qu'ils réclamaient; et il abandonna Jésus à leur volonté.
Ya saki mutumin da aka jefa a kurkuku saboda tā da hankali, da kisankai, shi wanda suka roƙa. Sa’an nan ya ba da Yesu ga nufinsu.
26 Comme ils l'emmenaient, ils prirent un homme de Cyrène, nommé Simon, qui revenait des champs; et ils le chargèrent de la croix, pour qu'il la portât derrière Jésus.
Sa’ad da suna tafiya da Yesu, sai wani da ake kira Siman, mutumin Sairin, yana zuwa daga ƙauye. Suka kama shi, suka aza masa gicciyen, suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen, ya bi Yesu a baya.
27 Le peuple, en grande multitude, suivait Jésus, ainsi que des femmes qui se frappaient la poitrine et qui pleuraient sur lui.
Mutane da yawa sosai suka bi shi, a cikinsu ma da mata waɗanda suka yi makoki da kuka dominsa.
28 Mais Jésus, se tournant vers elles, leur dit: Filles de Jérusalem, ne pleurez pas sur moi, mais pleurez sur vous-mêmes et sur vos enfants!
Yesu ya juya, ya ce musu, “’Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka saboda ni, amma ku yi kuka saboda kanku, da kuma saboda’ya’yanku.
29 Car voici que les jours viennent où l'on dira: Heureuses les stériles, heureuses les entrailles qui n'ont pas enfanté, et les mamelles qui n'ont point allaité!
Gama lokaci yana zuwa da za ku ce, ‘Masu albarka ne bakararru, wato, mata marasa haihuwa, da mahaihuwar da ba su taɓa haihuwa ba, da kuma mama da ba su taɓa shayar da nono ba!’
30 Alors les hommes se mettront à dire aux montagnes: Tombez sur nous!!- et aux coteaux: Couvrez-nous!
Sa’an nan “‘za su ce wa duwatsu, “Ku fāɗi a kanmu!” Za su ce wa tuddai kuma, “Ku rufe mu!”’
31 Car si l'on fait ces choses au bois vert, qu'arrivera-t-il au bois sec?
Gama in mutane suna yin waɗannan abubuwa a lokacin da itace na ɗanye, me zai faru in ya bushe?”
32 On conduisait aussi deux autres hommes, des malfaiteurs, pour les faire mourir avec lui.
Tare da shi akwai mutum biyu masu laifi, da aka tafi da su don a gicciye.
33 Quand ils furent arrivés au lieu appelé le lieu du Crâne, ils le crucifièrent là, ainsi que les malfaiteurs, l'un à sa droite, et l'autre à sa gauche.
Da suka isa wurin da ake kira “Ƙoƙon Kai,” nan suka gicciye shi, tare da masu laifin nan, ɗaya a hannun damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
34 Mais Jésus disait: Père, pardonne-leur; car ils ne savent ce qu'ils font. Puis, ils se partagèrent ses vêtements, en les tirant au sort.
Yesu ya ce, “Ya Uba ka yi musu gafara, don ba su san abin da suke yi ba.” Suka rarraba tufafinsa ta wurin jefa ƙuri’a.
35 Le peuple se tenait là et regardait. Et les chefs se moquaient, en disant: Il en a sauvé d'autres; qu'il se sauve lui-même, s'il est le Christ, l'élu de Dieu!
Mutanen suka tsaya suna kallo. Har masu mulki ma suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, to, ya ceci kansa in shi ne Kiristi na Allah, Zaɓaɓɓe.”
36 Les soldats aussi le tournaient en dérision. Ils s'approchaient et lui présentaient du vinaigre
Sojoji su ma, suka zo suka yi masa ba’a. Suka miƙa masa ruwan tsami.
37 en disant: Si tu es le roi des Juifs, sauve-toi toi-même!
Suka ce, “In kai ne sarkin Yahudawa, ka ceci kanka mana.”
38 Au-dessus de sa tête, il y avait cette inscription: Celui-ci est le roi des Juifs.
Bisa da shi kuma akwai rubutun da ya ce, Wannan shi ne Sarkin Yahudawa.
39 Or, l'un des malfaiteurs qui avaient été crucifiés, l'injuriait, en disant: N'es-tu pas le Christ? Sauve-toi toi-même, et nous avec toi!
Ɗaya daga cikin masu laifin da aka gicciye a wurin ya zazzage shi ya ce, “Shin, ba kai ne Kiristi ba? To, ka ceci kanka, ka kuma cece mu mana!”
40 Mais l'autre, le reprenant, lui dit: Ne crains-tu pas Dieu, toi qui subis la même condamnation?
Amma ɗayan mai laifi ya kwaɓe shi ya ce, “Ba ka da tsoron Allah ne, wai saboda kana ƙarƙashin hukunci ɗaya tare da shi?
41 Pour nous, ce n'est que justice, car nous recevons ce que nos actions ont mérité; mais celui-ci n'a fait aucun mal.
Horonmu, daidai aka yi mana, sakamakon abin da muka yi ne. Amma wannan mutum, bai yi wani laifi ba.”
42 Puis il disait; Jésus, souviens-toi de moi, quand tu viendras dans ton règne!
Sai ya ce, “Yesu, ka tuna da ni sa’ad da ka shiga mulkinka.”
43 Jésus lui répondit: En vérité, je te le déclare, aujourd'hui tu seras avec moi dans le paradis.
Yesu ya amsa, ya ce masa, “Gaskiya nake faɗa maka, yau ɗin nan, za ka kasance tare da ni, a mulkina a sama.”
44 Il était déjà environ la sixième heure, et il y eut des ténèbres sur tout le pays jusqu'à la neuvième heure.
Yanzu kuwa wajen sa’a ta shida ne, kuma duhu ya rufe ko’ina a ƙasar, har zuwa sa’a ta tara,
45 Le soleil s'obscurcit, et le voile du temple se déchira par le milieu.
domin rana ta daina haskakawa. Labulen da yake cikin haikali kuma ya yage kashi biyu.
46 Alors Jésus jeta un grand cri et dit: Père, je remets mon esprit entre tes mains! Et après avoir dit cela, il expira.
Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Ya Uba, na danƙa ruhuna a hannunka.” Da ya faɗi haka, sai ya ja numfashi na ƙarshe.
47 Le centenier, voyant ce qui était arrivé, donna gloire à Dieu et dit: Certainement cet homme était juste.
Da jarumin ya ga abin da ya faru, sai ya yabi Allah ya ce, “Gaskiya, wannan mutum mai adalci ne.”
48 Et tout le peuple qui était accouru à ce spectacle, voyant ce qui s'était passé, s'en retournait en se frappant la poitrine.
Da dukan mutanen da suka taru, domin shaidar waɗannan abubuwa, suka ga abin da ya faru, sai suka buga ƙirjinsu suka tafi.
49 Mais ceux qui connaissaient Jésus, ainsi que les femmes qui l'avaient suivi de la Galilée, se tenaient tous à distance et regardaient.
Amma dukan mutanen da suka san Yesu, tare da mata da suka bi shi daga Galili, suka tsaya daga nesa suna kallon abubuwan nan.
50 Il y avait un homme, appelé Joseph, qui était membre du Sanhédrin, homme droit et juste,
Akwai wani mutum mai suna Yusuf, ɗan Majalisa, wanda shi nagari ne, mai adalci,
51 qui n'avait pas consenti au dessein des autres, ni à ce qu'ils avaient fait. Il était d'Arimathée, ville de Judée, et il attendait le royaume de Dieu.
shi dā ma bai yarda da shawararsu, da kuma abin da suka yi ba. Shi daga Arimateya ne wani garin Yahudiya. Yana kuma jiran zuwa mulkin Allah.
52 Il vint donc trouver Pilate et lui demanda le corps de Jésus.
Sai ya je wurin Bilatus ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
53 Après l'avoir descendu de la croix, il l'enveloppa d'un linceul et le déposa dans un tombeau, taillé dans le roc, où personne n'avait encore été mis.
Sai ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi a cikin zanen lilin, ya sa shi a wani kabari da aka fafe a cikin dutse, wadda ba a taɓa sa kowa ba.
54 C'était le jour de la préparation, et le sabbat allait commencer.
An yi haka ne a Ranar Shirye-shirye, ranar Asabbaci kuma yana dab da farawa.
55 Les femmes qui étaient venues de la Galilée avec Jésus, ayant accompagné Joseph, virent le tombeau, et comment le corps de Jésus y avait été placé.
Matan da suka zo tare da Yesu, daga Galili suka bi Yusuf suka ga kabarin, da kuma yadda aka ajiye jikin.
56 Puis s'en étant retournées, elles préparèrent des aromates et des parfums. Le jour du sabbat, elles se reposèrent, conformément à la loi.
Sa’an nan, suka koma gida, suka shirya kayan ƙanshi da turare. Amma suka huta a ranar Asabbaci don kiyaye doka.

< Luc 23 >