< Luc 22 >

1 La fête des pains sans levain, appelée la Pâque, approchait.
Yanzu fa, Bikin Burodi Marar Yistin da ake kira Bikin Ƙetarewa ya yi kusa,
2 Et les principaux sacrificateurs et les scribes cherchaient comment ils pourraient faire mourir Jésus; car ils craignaient le peuple.
manyan firistoci da malaman dokoki kuma suna neman yadda za su kashe Yesu a ɓoye, don suna tsoron mutane.
3 Or, Satan entra dans Judas, nommé Iscariote, qui était du nombre des Douze.
Shaiɗan kuwa ya shiga Yahuda, wanda ake kira Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun.
4 Judas alla trouver les principaux sacrificateurs et les chefs des gardes, pour s'entendre avec eux sur les moyens de le leur livrer.
Sai Yahuda ya je ya tattauna da manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, a kan yadda zai ba da Yesu a gare su.
5 Ceux-ci, remplis de joie, lui promirent de lui donner de l'argent.
Suka kuwa yi murna, suka yarda su ba shi kuɗi.
6 Il se mit d'accord avec eux, et il cherchait une occasion favorable pour livrer Jésus à l'insu de la foule.
Ya ko yarda, ya fara neman zarafin da zai ba da Yesu a gare su, sa’ad da taro ba sa nan tare da shi.
7 Le jour des pains sans levain, où l'on devait immoler la Pâque, étant arrivé,
Sai ranar Bikin Burodi Marar Yisti ta kewayo, wato, ranar hadayar ɗan ragon kafara na Bikin Ƙetarewa.
8 Jésus envoya Pierre et Jean, et il leur dit: Allez nous préparer la Pâque, afin que nous la mangions.
Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yohanna, ya ce musu, “Ku je ku yi shirye-shiryen Bikin Ƙetarewar da za mu ci.”
9 Ils lui dirent: Où veux-tu que nous la préparions?
Suka tambaye shi suka ce, “Ina kake so mu je mu yi shirin?”
10 Il leur répondit: Lorsque vous entrerez dans la ville, vous rencontrerez un homme portant une cruche d'eau; suivez-le dans la maison où il entrera,
Ya amsa ya ce, “Sa’ad da kuka shiga cikin gari, za ku sadu da wani mutum yana ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi zuwa gidan da zai shiga.
11 et dites au maître de la maison: Le Maître te fait dire: Où se trouve la salle dans laquelle je dois manger la Pâque avec mes disciples?
Ku ce wa maigidan, Malam ya aike mu mu ce maka, ‘Ina ɗakin baƙi, inda ni da almajiraina za mu ci abincin Bikin Ƙetarewa?’
12 Et il vous montrera une grande chambre haute, toute meublée; préparez-y ce qu'il faut.
Zai nuna muku wani babban ɗakin sama a shirye. Nan za ku yi shirin.”
13 Ils s'en allèrent et trouvèrent les choses comme Jésus le leur avait dit; et ils préparèrent la Pâque.
Sai suka tafi, suka kuma iske kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
14 Quand l'heure fut venue, il se mit à table, et les apôtres avec lui.
Da lokaci ya yi, sai Yesu ya zauna tare da manzanninsa don cin abinci.
15 Puis il leur dit: J'ai fort désiré de manger cette Pâque avec vous, avant que je souffre.
Sai ya ce musu, “Na yi marmari ƙwarai don in ci wannan Bikin Ƙetarewa tare da ku, kafin in sha wahala.
16 Car, je vous le déclare, je ne la mangerai plus, jusqu'à ce qu'elle soit accomplie dans le royaume de Dieu.
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara cinsa ba, sai ya sami cika a mulkin Allah.”
17 Et, ayant pris une coupe et rendu grâces, il dit: Prenez ceci, et partagez-le entre vous.
Bayan ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, sai ya ce, “Ku karɓa, ku rarraba wa junanku.
18 Car, je vous le déclare, désormais je ne boirai plus du fruit de la vigne, jusqu'à ce que le royaume de Dieu soit venu.
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai mulkin Allah ya zo.”
19 Puis il prit du pain, et, après avoir rendu grâces, il le rompit et le leur donna, en disant: Ceci est mon corps, qui est donné pour vous; faites ceci en mémoire de moi.
Sai ya ɗauki burodi ya yi godiya, ya kakkarya ya ba su, da cewa, “Wannan jikina ne, da aka bayar dominku. Ku riƙa yin haka don tunawa da ni.”
20 De même, après avoir soupé, il leur donna la coupe, en disant: Cette coupe est la nouvelle alliance en mon sang, qui est répandu pour vous.
Haka kuma, bayan abincin, ya ɗauki kwaf ruwan inabi ya ce, “Wannan kwaf ruwan inabi shi ne, na sabon alkawari cikin jinina, da aka zubar dominku.
21 Au reste, la main de celui qui me trahit est près de moi: il est assis à cette table!
Amma hannun wanda zai ci amanata, yana cin abincin tare da ni.
22 En ce qui concerne le Fils de l'homme, il s'en va, conformément à ce qui a été arrêté; mais malheur à cet homme, par qui il est trahi!
Ɗan Mutum zai mutu kamar yadda aka ƙaddara, amma kaiton mutumin da zai bashe shi.”
23 Alors ils se mirent à se demander les uns aux autres, quel était donc celui d'entre eux qui ferait cela.
Sai suka fara tambayar junansu, ko wane ne a cikinsu zai yi wannan.
24 Il s'éleva aussi parmi eux une contestation, pour savoir lequel d'entre eux devait être regardé comme le plus grand.
Gardama ta tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma.
25 Mais Jésus leur dit: Les rois des nations leur commandent en maîtres, et ceux qui exercent l'autorité sur elles sont appelés bienfaiteurs.
Yesu ya ce musu, “Sarakunan Al’ummai suna nuna iko a kan mutanensu, kuma waɗanda suke nuna iko a kansu, suna kiran kansu Masu Taimakon mutane.
26 Pour vous, ne faites pas ainsi; mais, que le plus grand parmi vous soit comme le plus petit, et celui qui gouverne, comme celui qui sert.
Amma ku, kada ku zama haka. A maimakon haka, sai dai wanda ya fi girma a cikinku, ya zama kamar wanda ya fi ƙanƙanta, wanda kuma ke mulki, ya zama kamar mai hidima.
27 Car lequel est le plus grand, celui qui est à table, ou celui qui sert? N'est-ce pas celui qui est à table? Moi pourtant, je suis au milieu de vous comme celui qui sert.
Wane ne ya fi girma? Wanda yake zaune a tebur ne, ko kuma shi da yake yin hidima? Ashe, ba wanda yake zaune a tebur ba ne? Amma ga ni, ni mai yin hidima ne a cikinku.
28 Quant à vous, vous avez persévéré avec moi dans mes épreuves,
Ku ne kuka tsaya tare da ni a gwaje-gwajen da na sha.
29 et je dispose du royaume en votre faveur, comme mon Père en a disposé pour moi,
Daidai kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka ni ma nake ba ku.
30 afin que vous mangiez et que vous buviez à ma table dans mon royaume, et que vous soyez assis sur des trônes, jugeant les douze tribus d'Israël.
Saboda ku ci, ku sha a teburina a cikin mulkina. Kuma ku zauna a kan gadon sarauta, ku yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
31 Simon, Simon, voici que Satan a demandé à vous passer au crible comme le blé.
“Siman, Siman, Shaiɗan ya nemi izini ya sheƙe kakamar alkama.
32 Mais j'ai prié pour toi, afin que ta foi ne défaille point. Toi donc, quand tu seras converti, affermis tes frères.
Amma na yi maka addu’a, Siman, domin kada bangaskiyarka ta kāsa. Bayan ka juyo, ka ƙarfafa’yan’uwanka.”
33 Pierre lui dit: Seigneur, je suis prêt à aller avec toi, et en prison et à la mort!
Amma ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina a shirye in tafi tare da kai har kurkuku, ko mutuwa ma.”
34 Jésus répondit: Pierre, je te le déclare, le coq ne chantera pas aujourd'hui, que tu n'aies par trois fois nié de me connaître.
Yesu ya ce, “Ina gaya maka Bitrus, kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
35 Puis il ajouta: Lorsque je vous ai envoyés sans bourse, sans sac et sans chaussures, avez-vous manqué de quelque chose? Ils répondirent: De rien.
Sai Yesu ya tambaye, su ya ce, “Lokacin da na aike ku ba tare da jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma ba, kun rasa wani abu?” Suka amsa, “Babu.”
36 Mais maintenant, leur dit-il, que celui qui a une bourse, la prenne, et de même, celui qui a un sac; et que celui qui n'a point d'épée, vende son manteau et en achète une.
Ya ce musu, “Amma yanzu, in kuna da jakar kuɗi, ko jaka, ku ɗauka. In kuma ba ku da takobi, ku sayar da rigarku, ku saya.
37 Car, je vous le déclare, il faut que s'accomplisse en ma personne ce qui est écrit: «Il a été mis au rang des malfaiteurs.» En effet, ce qui me concerne touche à sa fin.
A rubuce yake cewa, ‘An lissafta shi tare da masu zunubi.’ Ina kuwa gaya muku, dole wannan ya cika a kaina. I, abin da aka rubuta a kaina yana kusan cikawa.”
38 Ils dirent: Seigneur, voici deux épées. Il leur répondit: Cela suffit.
Almajiran suka ce, “Duba Ubangiji, ga takuba biyu.” Yesu ya ce, “Ya isa.”
39 Puis, Jésus sortit et alla, selon sa coutume, à la montagne des Oliviers; et les disciples le suivirent.
Yesu ya fita zuwa Dutsen Zaitun kamar yadda ya saba, almajiransa kuma suka bi shi.
40 Quand il fut arrivé en ce lieu, il leur dit: Priez, afin que vous ne tombiez pas dans la tentation.
Da ya kai wurin, sai ya ce musu, “Ku yi addu’a don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
41 Alors il s'éloigna d'eux d'un jet de pierre environ, et, s'étant mis à genoux, il priait,
Sai ya janye daga wurinsu, misalin nisan jifa, ya durƙusa a ƙasa ya yi addu’a,
42 disant: Père, si tu voulais éloigner de moi cette coupe! Toutefois, que ta volonté soit faite et non la mienne!
“Uba, in ka yarda, ka ɗauke mini wannan kwaf, amma ba nufina ba, sai dai naka.”
43 Et un ange lui apparut du ciel, qui le fortifiait.
Wani mala’ika daga sama ya bayyana gare shi, ya ƙarfafa shi.
44 Étant en agonie, il priait plus instamment, et sa sueur devint comme de grosses gouttes de sang qui tombaient à terre.
Domin tsananin azaba, sai ya ƙara himma cikin addu’a, zuffansa kuma na ɗigowa ƙasa kamar jini.
45 Après avoir prié, il se leva et revint vers les disciples, qu'il trouva endormis de tristesse.
Da ya tashi daga addu’a, ya koma inda almajiransa suke, sai ya iske su suna barci, daga gajiyar baƙin ciki.
46 Et il leur dit: Pourquoi dormez-vous? Levez-vous, et priez, afin que vous ne tombiez pas dans la tentation.
Ya tambaye su, “Don me kuke barci? Ku tashi ku yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
47 Comme il parlait encore, une troupe parut. Celui qu'on nommait Judas, l'un des Douze, marchait devant elle, et il s'approcha de Jésus pour lui donner un baiser.
Yana cikin magana sai ga taro sun zo. Mutumin nan da ake kira Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun, shi ya bi da su. Sai ya matso kusa da Yesu don yă yi masa sumba.
48 Jésus lui dit: Judas, tu trahis le Fils de l'homme par un baiser!
Amma Yesu ya tambaye shi ya ce, “Yahuda, ashe, da sumba za ka bashe Ɗan Mutum?”
49 Alors ceux qui étaient avec lui, voyant ce qui allait arriver, lui dirent: Seigneur, frapperons-nous de l'épée?
Da masu bin Yesu suka ga abin da zai faru, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takubanmu ne?”
50 Et l'un d'eux frappa le serviteur du souverain sacrificateur, et il lui emporta l'oreille droite.
Sai ɗayansu ya kai sara ga bawan babban firist, ya sare kunnen damansa.
51 Mais Jésus, prenant la parole, dit: Arrêtez un moment! Et, ayant touché l'oreille de cet homme, il le guérit.
Amma Yesu ya amsa ya ce, “Kada a ƙara yin wannan!” Sai ya taɓa kunnen mutumin da aka sara, ya warkar da shi.
52 Puis Jésus dit aux principaux sacrificateurs, aux chefs des gardes du temple et aux anciens, qui étaient venus vers lui: Vous êtes sortis avec des épées et des bâtons, comme après un brigand.
Sai Yesu ya ce wa manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, da dattawa, waɗanda suka zo don su kama shi, “Ina jagoran wani tawaye ne, da za ku zo da takuba da sanduna?
53 J'étais tous les jours dans le temple avec vous, et vous n'avez pas mis la main sur moi. Mais c'est ici votre heure et la puissance des ténèbres.
Kullum ina tare da ku a filin haikali, amma ba ku kama ni ba. Amma wannan ne sa’a naku, lokacin da duhu yake mulki.”
54 Alors, ils le saisirent et l'emmenèrent; et ils le firent entrer dans la maison du souverain sacrificateur, Pierre suivait de loin.
Sai suka kama shi suka kai shi gidan babban firist. Bitrus ya bi su daga nesa.
55 Ils allumèrent du feu au milieu de la cour et s'assirent ensemble; et Pierre s'assit parmi eux.
Amma da suka hura wuta a tsakiyar harabar gidan, kowa ya zauna, sai Bitrus ya zo ya zauna tare da su.
56 Une servante, le voyant assis près du feu et le regardant attentivement, dit: Cet homme était aussi avec lui.
Wata baiwa ta gan shi zaune kusa da wutar. Ta dube shi sosai sa’an nan, ta ce, “Ai, wannan mutum ma yana tare da shi.”
57 Mais il renia Jésus, en disant: Femme, je ne le connais point!
Amma ya yi mūsu ya ce, “Mace, ban san shi ba!”
58 Un peu après, un autre, l'ayant vu, lui dit: Toi aussi, tu es de ces gens-là! Pierre répondit à cet homme: Je n'en suis pas!
Bayan ɗan lokaci kaɗan, wani dabam ya gan shi ya ce, “Kai ma ɗayansu ne.” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ba na cikinsu!”
59 Environ une heure plus tard, un autre assurait la même chose et disait: Certainement, cet homme était aussi avec lui; car il est Galiléen.
Bayan kamar sa’a ɗaya, sai wani mutum ya ce, “Ba shakka, mutumin nan ma yana tare da shi, don shi mutumin Galili ne.”
60 Mais Pierre reprit: homme, je ne sais ce que tu veux dire! Au même instant, comme il parlait encore, le coq chanta;
Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ban ma san abin da kake magana a kai ba!” Yana cikin magana, sai zakara ya yi cara.
61 et le Seigneur, s'étant retourné, regarda Pierre. Pierre se ressouvint de la parole que le Seigneur lui avait dite: Avant que le coq chante aujourd'hui, tu me renieras trois fois.
Ubangiji kuma ya juya ya kafa wa Bitrus ido. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Ubangiji ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
62 Et étant sorti, il pleura amèrement.
Sai ya fita waje, ya yi kuka mai zafi.
63 Or, ceux qui gardaient Jésus se moquaient de lui et le frappaient;
Mutanen da suke gadin Yesu suka fara masa ba’a da dūka.
64 et, lui ayant couvert le visage, ils lui disaient: Prophétise, devine qui t'a frappé!
Suka rufe masa idanu suna tambaya cewa, “Ka yi annabci! Wa ya mare ka?”
65 Et ils proféraient beaucoup d'autres injures contre lui.
Suka kuma yi masa waɗansu baƙaƙen maganganu masu yawa.
66 Quand le jour fut venu, les anciens du peuple, les principaux sacrificateurs et les scribes se réunirent, et ils le firent venir dans leur Sanhédrin.
Da gari ya waye, sai majalisar dattawa na mutane, da manyan firistoci, da malaman dokoki, suka taru wuri ɗaya. Sai aka kawo Yesu a gabansu.
67 Ils lui dirent: Si tu es le Christ, déclare-le-nous. Il leur répondit: Si je le disais, vous ne le croiriez pas;
Suka ce, “Ka faɗa mana, ko kai ne Kiristi?” Yesu ya amsa ya ce, “Ko na gaya muku, ba za ku gaskata ni ba,
68 et si je vous interrogeais, vous ne me répondriez pas.
in kuma na yi muku tambaya ba za ku iya ba ni amsa ba.
69 Mais désormais le Fils de l'homme sera assis à la droite du Dieu tout-puissant.
Amma daga yanzu, Ɗan Mutum zai zauna a hannun dama na Allah Mai Iko.”
70 Ils dirent tous: Tu es donc le Fils de Dieu? Il leur répondit: Vous dites vous-mêmes que je le suis.
Sai dukansu suka yi tambaya suka ce, “Wato, kai Ɗan Allah ke nan?” Ya amsa ya ce, “Kun faɗa daidai, ni ne.”
71 Alors ils s'écrièrent: Qu'avons-nous encore besoin de témoignage? Nous venons nous-mêmes de l'entendre de sa propre bouche!
Sai suka ce, “Wace shaida kuma muke nema? Ai, mun ji abin da ya ce da bakinsa.”

< Luc 22 >