< Psaumes 47 >

1 Peuples, battez tous des mains; poussez des cris de joie à Dieu avec une voix de triomphe!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
2 Car l'Éternel est le Très-Haut, le terrible, le grand Roi, régnant sur toute la terre.
Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
3 Il range les peuples sous nous, et les nations sous nos pieds.
Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
4 Il nous choisit notre héritage, la gloire de Jacob qu'il aime. (Sélah)
Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
5 Dieu est monté au milieu des cris de joie; l'Éternel est monté au son de la trompette.
Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
6 Chantez à Dieu, chantez; chantez à notre Roi, chantez!
Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
7 Car Dieu est roi de toute la terre; chantez le cantique!
Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
8 Dieu règne sur les nations; Dieu siège sur son trône saint.
Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
9 Les princes des peuples se rassemblent avec le peuple du Dieu d'Abraham; car à Dieu sont les boucliers de la terre; il est souverainement élevé.
Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.

< Psaumes 47 >