< Psaumes 77 >
1 Ma voix s'adresse à Dieu, et je crie, ma voix s'adresse à Dieu, et il m'écoutera.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
2 Au jour de ma détresse, j'ai cherché le Seigneur; la nuit, ma main était étendue vers lui et ne se lassait point; mon âme refusait d'être consolée.
Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
3 Je me souvenais de Dieu, et je gémissais; je méditais, et mon esprit était abattu. (Sélah, pause)
Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
4 Tu avais retenu mes yeux dans les veilles; j'étais troublé, je ne pouvais parler.
ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
5 Je pensais aux jours d'autrefois, aux années des temps passés.
Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
6 Je me rappelais mes mélodies de la nuit; je méditais en mon cœur, et mon esprit examinait.
na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
7 Le Seigneur rejettera-t-il pour toujours, ne sera-t-il plus désormais propice?
“Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
8 Sa bonté a-t-elle cessé pour toujours? Sa parole a-t-elle pris fin pour tous les âges?
Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
9 Dieu a-t-il oublié d'avoir pitié? A-t-il dans sa colère fermé ses compassions?
Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
10 Et j'ai dit: Voilà ce qui fait ma souffrance: C'est que la droite du Très-Haut a changé.
Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
11 Je me rappellerai les exploits de l'Éternel, me souvenant de tes merveilles d'autrefois;
Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
12 Je méditerai sur toutes tes œuvres, et je considérerai tes hauts faits.
Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
13 O Dieu, tes voies sont saintes! Quel autre Dieu est grand comme Dieu?
Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
14 Tu es le Dieu qui fait des merveilles; tu as fait connaître ta force parmi les peuples.
Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
15 Par ton bras, tu rachetas ton peuple, les enfants de Jacob et de Joseph. (Sélah)
Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
16 Les eaux te virent, ô Dieu! Les eaux te virent; elles tremblèrent; même les abîmes s'émurent.
Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
17 Les nues se répandirent en eaux; les nuages tonnèrent; tes traits aussi volèrent çà et là.
Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
18 Ton tonnerre gronda dans le tourbillon; les éclairs brillèrent sur le monde; la terre s'émut et trembla.
Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
19 Tu as fait ton chemin dans la mer, tes sentiers dans les grandes eaux; et tes traces n'ont point été connues.
Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
20 Tu as conduit ton peuple comme un troupeau, par la main de Moïse et d'Aaron.
Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.