< Proverbes 8 >

1 La sagesse ne crie-t-elle pas, et l'intelligence ne fait-elle pas entendre sa voix?
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 Elle se place au sommet des hauteurs, sur le chemin, aux carrefours.
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 Près des portes, devant la ville, à l'entrée des rues, elle s'écrie:
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 O hommes! je vous appelle, et ma voix s'adresse aux enfants des hommes.
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 Vous, stupides, apprenez le discernement; vous, insensés, devenez intelligents de cœur.
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Écoutez, car je dirai des choses importantes, et j'ouvrirai mes lèvres pour enseigner ce qui est droit.
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 Car ma bouche dit la vérité, et mes lèvres ont en horreur le mensonge.
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 Toutes les paroles de ma bouche sont selon la justice; il n'y a rien en elles de faux ni de trompeur.
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 Toutes sont claires pour l'homme intelligent, et droites pour ceux qui ont trouvé la science.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Recherchez mon instruction, plus que de l'argent; et la science, plus que de l'or choisi.
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 Car la sagesse est meilleure que les perles, et tout ce qu'on pourrait souhaiter ne la vaut pas.
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 Moi, la sagesse, j'habite avec le discernement, et je possède la science des sages pensées.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 La crainte de l'Éternel, c'est la haine du mal; je hais l'orgueil et l'arrogance, la voie du mal et la bouche perverse.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 C'est à moi qu'appartient le conseil et l'habileté; je suis la prudence; la force est à moi.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 Par moi les rois règnent, et les princes ordonnent ce qui est juste.
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 Par moi dominent les puissants et les grands, et tous les juges de la terre.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 J'aime ceux qui m'aiment; et ceux qui me cherchent me trouvent.
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 Avec moi sont les richesses et la gloire, les biens durables et la justice.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 Mon fruit est meilleur que l'or fin, même que l'or raffiné, et ce que je rapporte est meilleur que l'argent le plus pur.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 Je fais marcher par le chemin de la justice, et par le milieu des sentiers de la droiture,
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 Pour donner en héritage des biens à ceux qui m'aiment, et pour remplir leurs trésors.
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 L'Éternel m'a possédée dès le commencement de ses voies, avant qu'il fît aucune de ses œuvres.
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 J'ai été établie depuis l'éternité, dès le commencement, dès l'origine de la terre.
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 J'ai été engendrée lorsqu'il n'y avait point encore d'abîmes, ni de fontaines riches en eaux.
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 J'ai été engendrée avant que les montagnes fussent assises, et avant les coteaux;
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 Avant qu'il eût fait la terre, et les campagnes, et le commencement de la poussière du monde.
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 Quand il agençait les cieux, j'y étais; quand il traçait le cercle au-dessus de l'abîme,
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 Quand il fixait les nuages en haut, quand il faisait jaillir les fontaines de l'abîme.
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 Quand il imposait à la mer sa loi, afin que ses eaux n'en franchissent pas les limites, quand il posait les fondements de la terre,
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 Alors j'étais auprès de lui son ouvrière, j'étais ses délices de tous les jours, et je me réjouissais sans cesse en sa présence.
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 Je trouvais ma joie dans le monde et sur la terre, et mon bonheur parmi les enfants des hommes.
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 Maintenant donc, mes enfants, écoutez-moi. Heureux ceux qui garderont mes voies!
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 Écoutez l'instruction, pour devenir sages, et ne la rejetez point.
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Heureux l'homme qui m'écoute, qui veille à mes portes chaque jour, et qui garde les poteaux de l'entrée de ma maison!
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 Car celui qui me trouve, trouve la vie, et obtient la faveur de l'Éternel;
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 Mais celui qui m'offense fait tort à son âme. Tous ceux qui me haïssent, aiment la mort.
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”

< Proverbes 8 >