< Job 28 >
1 L'argent a des lieux d'extraction, et l'or a des endroits où on l'affine.
Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
2 Le fer se tire de la poussière, et la pierre fondue donne l'airain.
Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
3 L'homme dissipe les ténèbres; il explore, jusqu'aux extrêmes limites, la pierre qui est dans l'obscurité et l'ombre de la mort.
Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
4 Il creuse un puits, loin des passants; ne se souvenant plus de ses pieds, il est suspendu et balancé loin des humains.
Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
5 C'est de la terre que sort le pain, et elle est bouleversée, dans ses profondeurs, comme par le feu.
Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
6 Ses rochers sont la demeure du saphir, et l'on y trouve la poudre d'or.
akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
7 L'oiseau de proie n'en connaît pas le chemin, et l'œil du milan ne le découvre pas.
Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
8 Les bêtes féroces n'y ont point marché, le lion n'a point passé par là.
Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
9 L'homme met la main sur le granit; il bouleverse les montagnes jusqu'en leurs fondements.
Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
10 Il taille des galeries dans les rochers, et son œil découvre tout ce qu'il y a de précieux.
Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
11 Il arrête la filtration des eaux, et il met au jour ce qui était caché.
Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
12 Mais la sagesse, où la trouvera-t-on? Où donc est le lieu de l'intelligence?
Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
13 L'homme ne connaît pas son prix, et elle ne se trouve pas dans la terre des vivants.
Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
14 L'abîme dit: Elle n'est pas en moi; et la mer dit: Elle n'est pas avec moi.
Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
15 Elle ne se donne pas pour de l'or fin, elle ne s'achète pas au poids de l'argent.
Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
16 On ne la met pas en balance avec l'or d'Ophir; ni avec le précieux onyx, ni avec le saphir.
Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
17 On ne la compare point avec l'or et avec le verre, et on ne l'échange pas pour des vases d'or fin.
Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
18 On ne parle ni du corail ni du cristal, et la possession de la sagesse vaut plus que des perles.
Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
19 On ne la compare pas avec la topaze d'Éthiopie; on ne la met pas en balance avec l'or le plus fin.
Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
20 Mais la sagesse, d'où viendra-t-elle? Et où donc est la demeure de l'intelligence?
“To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
21 Elle est cachée aux yeux de tous les vivants; elle se dérobe aux oiseaux des cieux.
An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
22 Le gouffre et la mort disent: Nous avons de nos oreilles entendu parler d'elle.
Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
23 C'est Dieu qui sait son chemin; c'est lui qui connaît sa demeure.
Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
24 Car il regarde, lui, jusqu'aux extrémités du monde; il voit sous tous les cieux.
Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
25 Quand il donnait au vent son poids, quand il pesait et mesurait les eaux,
Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
26 Quand il prescrivait une loi à la pluie, et un chemin à l'éclair des tonnerres,
Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
27 Il la vit alors et la proclama; il l'établit, et même il la sonda;
sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
28 Puis il dit à l'homme: Voici, la crainte du Seigneur, c'est la sagesse, et se détourner du mal, c'est l'intelligence.
Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”