< Job 21 >

1 Et Job prit la parole, et dit:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Écoutez attentivement mes discours, et que cela me tienne lieu de vos consolations!
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Supportez-moi, et je parlerai; et, après que j'aurai parlé, tu te moqueras.
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 Mais est-ce à un homme que s'adresse ma plainte? Et comment ne perdrais-je pas toute patience?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Regardez-moi, et soyez étonnés, et mettez la main sur la bouche.
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 Quand j'y pense, je suis éperdu, et un frisson saisit ma chair.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 Pourquoi les méchants vivent-ils, vieillissent-ils, et croissent-ils en force?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Leur postérité s'établit devant eux, avec eux, et leurs rejetons sont sous leurs yeux.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Leurs maisons sont en paix, à l'abri de la crainte, et la verge de Dieu n'est pas sur eux.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 Leur taureau n'est jamais impuissant, leur génisse vêle et n'avorte pas.
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 Ils font courir devant eux leurs enfants comme un troupeau, et leur progéniture bondit.
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 Ils chantent avec le tambourin et la harpe, ils s'égaient au son du hautbois,
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 Ils passent leurs jours dans le bonheur, et ils descendent au Sépulcre en un moment. (Sheol h7585)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
14 Et cependant ils ont dit à Dieu: “Éloigne-toi de nous, nous ne voulons pas connaître tes voies.
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 Qu'est-ce que le Tout-Puissant, pour que nous le servions? Et que gagnerions-nous à le prier? “
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 Voici, leur bonheur n'est-il pas en leurs mains? (Que le conseil des méchants soit loin de moi! )
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 Combien de fois arrive-t-il que la lampe des méchants s'éteigne, que leur ruine vienne sur eux, que Dieu leur partage leurs lots dans sa colère,
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 Qu'ils soient comme la paille au souffle du vent, et comme la balle enlevée par le tourbillon?
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 Vous dites: “Dieu réserve la peine à ses enfants; “mais qu'Il le punisse lui-même, afin qu'il le sente!
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 Qu'il voie de ses propres yeux sa ruine, qu'il boive la colère du Tout-Puissant!
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 Car, que lui importe sa maison après lui, quand le nombre de ses mois est tranché?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Enseignerait-on la science à Dieu, lui qui juge ceux qui sont élevés?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 L'un meurt au sein du bien-être, tout à son aise et en repos.
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 Ses flancs sont chargés de graisse, et ses os comme abreuvés de mœlle;
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 Un autre meurt dans l'amertume de son âme, n'ayant jamais goûté le bonheur:
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 Ils sont couchés ensemble dans la poussière, et les vers les couvrent.
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Voici, je connais vos pensées et les desseins que vous formez contre moi.
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 Car vous dites: Où est la maison de l'homme opulent, et où est la tente, demeure des méchants?
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 N'avez-vous jamais interrogé les voyageurs, et n'avez-vous pas reconnu, par leurs témoignages,
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 Qu'au jour de la calamité, le méchant est épargné, et qu'au jour des colères, il est éloigné?
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 Qui lui représente en face sa conduite, et qui lui rend ce qu'il a fait?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 Il est porté au tombeau, et, sur le tertre, il veille encore.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 Les mottes de la vallée lui sont légères; après lui, suivent à la file tous les hommes, et devant lui, la foule est innombrable.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 Comment donc me donnez-vous des consolations vaines? De vos réponses, ce qui reste, c'est la perfidie.
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”

< Job 21 >