< Psaumes 51 >

1 Psaume de David, au maître chantre. Touchant ce que Nathan le Prophète vint à lui, après qu'il fut entré vers Bathsebah. Ô Dieu! aie pitié de moi selon ta gratuité, selon la grandeur de tes compassions efface mes forfaits.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
2 Lave-moi parfaitement de mon iniquité, et me nettoie de mon péché.
Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
3 Car je connais mes transgressions, et mon péché est continuellement devant moi.
Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
4 J'ai péché contre toi, contre toi proprement, et j'ai fait ce qui déplaît à tes yeux: afin que tu sois connu juste quand tu parles, [et] trouvé pur, quand tu juges.
Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
5 Voilà, j'ai été formé dans l'iniquité, et ma mère m'a échauffé dans le péché.
Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
6 Voilà, tu aimes la vérité dans le cœur, et tu m'as enseigné la sagesse dans le secret [de mon cœur].
Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
7 Purifie-moi du péché avec de l'hysope, et je serai net; lave-moi, et je serai plus blanc que la neige.
Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
8 Fais-moi entendre la joie et l'allégresse, et fais que les os que tu as brisés se réjouissent.
Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
9 Détourne ta face de mes péchés, et efface toutes mes iniquités.
Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
10 Ô Dieu! crée-moi un cœur net, et renouvelle au dedans de moi un esprit bien remis.
Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
11 Ne me rejette point de devant ta face, et ne m'ôte point l'Esprit de ta Sainteté.
Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
12 Rends-moi la joie de ton salut, et que l'Esprit de l'affranchissement me soutienne.
Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
13 J'enseignerai tes voies aux transgresseurs, et les pécheurs se convertiront à toi.
Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
14 Ô Dieu! Dieu de mon salut, délivre-moi de tant de sang, [et] ma langue chantera hautement ta justice.
Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
15 Seigneur, ouvre mes lèvres, et ma bouche annoncera ta louange.
Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
16 Car tu ne prends point plaisir aux sacrifices, autrement j'en donnerais; l'holocauste ne t'est point agréable.
Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
17 Les sacrifices de Dieu sont l'esprit froissé: ô Dieu! tu ne méprises point le cœur froissé et brisé.
Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
18 Fais du bien selon ta bienveillance à Sion, [et] édifie les murs de Jérusalem.
Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
19 Alors tu prendras plaisir aux sacrifices de justice, à l'holocauste, et aux sacrifices qui se consument entièrement par le feu; alors on offrira des veaux sur ton autel.
Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.

< Psaumes 51 >