< Psaumes 116 >
1 J'aime l'Eternel, car il a exaucé ma voix, [et] mes supplications.
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
2 Car il a incliné son oreille vers moi, c'est pourquoi je l'invoquerai durant mes jours.
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
3 Les cordeaux de la mort m'avaient environné, et les détresses du sépulcre m'avaient rencontré; j'avais rencontré la détresse et l'ennui. (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol )
4 Mais j'invoquai le Nom de l’Eternel, [en disant]: je te prie, ô Eternel! délivre mon âme.
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
5 L'Eternel est pitoyable et juste, et notre Dieu fait miséricorde.
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
6 L'Eternel garde les simples; j'étais devenu misérable, et il m'a sauvé.
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
7 Mon âme, retourne en ton repos; car l'Eternel t'a fait du bien.
Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
8 Parce que tu as mis à couvert mon âme de la mort, mes yeux de pleurs, [et] mes pieds de chute.
Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
9 Je marcherai en la présence de l'Eternel dans la terre des vivants.
don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
10 J'ai cru, c'est pourquoi j'ai parlé; j'ai été fort affligé.
Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
11 Je disais en ma précipitation: tout homme est menteur.
Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
12 Que rendrai-je à l'Eternel? tous ses bienfaits sont sur moi.
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
13 Je prendrai la coupe des délivrances, et j'invoquerai le Nom de l’Eternel.
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
14 Je rendrai maintenant mes vœux à l'Eternel, devant tout son peuple.
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
15 [Toute sorte] de mort des bien-aimés de l'Eternel est précieuse devant ses yeux.
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
16 Ouï, ô Eternel! car je suis ton serviteur, je suis ton serviteur, fils de ta servante, tu as délié mes liens.
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
17 Je te sacrifierai des sacrifices d'actions de grâces, et j'invoquerai le Nom de l’Eternel.
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
18 Je rendrai maintenant mes vœux à l'Eternel, devant tout son peuple;
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
19 Dans les parvis de la maison de l'Eternel, au milieu de toi, Jérusalem. Louez l'Eternel.
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.