< Ézéchiel 29 >

1 La dixième année, au dixième mois, le douze du mois, la parole de Yahweh me fut adressée en ces termes:
A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 " Fils de l'homme, tourne ta face contre Pharaon, roi d'Egypte, et prophétise sur lui et sur l'Egypte tout entière;
“Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
3 parle et dis: Ainsi parle le Seigneur Yahweh: Voici que je viens à toi, Pharaon, roi d'Egypte, toi le grand crocodile, couché au milieu de tes fleuves, qui as dit: " Mon fleuve est à moi, et c'est moi qui me le suis fait. "
Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
4 Je mettrai des crochets dans tes mâchoires, et je ferai s'attacher à tes écailles les poissons de tes fleuves; et je te ferai monter du milieu de tes fleuves, toi et tous les poissons de tes fleuves, attachés à tes écailles;
Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
5 et je te jetterai au désert, toi et tous les poissons de tes fleuves; tu tomberas sur la face des champs, tu ne seras ni relevé, ni ramassé; je te donne en pâture aux bêtes de la terre et aux oiseaux du ciel;
Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
6 et tous les habitants de l'Egypte sauront que je suis Yahweh — parce qu'ils ont été un appui de roseau pour la maison d'Israël!
Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
7 Quand ils te prennent avec la main, tu casses, et tu leur déchires toute l'épaule; et quand ils s'appuient sur toi, tu te brises, tu les fais se tenir sur leurs reins à tous.
Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
8 C'est pourquoi ainsi parle le Seigneur Yahweh: Voici que je ferai venir sur toi l'épée et j'exterminerai du milieu de toi hommes et bêtes;
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
9 et la terre d'Egypte deviendra une désolation et un désert, et l'on saura que je suis Yahweh. Parce que Pharaon a dit: " Le fleuve est à moi, et c'est moi qui l'ai fait, "
Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
10 à cause de cela, voici que je viens à toi et à tes fleuves; et je ferai du pays d'Egypte des ruines désertes et désolées, de Migdol a Syène, et jusqu'à la frontière de l'Ethiopie.
saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
11 Il n'y passera nul pied d'homme, et nul pied de bête n'y passera, et il sera inhabité pendant quarante ans.
Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
12 Je ferai du pays d'Egypte une désolation, au milieu des pays désolés, et ses villes, au milieu des villes ruinées, seront une désolation, durant quarante ans; je disperserai les Egyptiens parmi les nations; et je les disséminerai en divers pays.
Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
13 Car ainsi parle le Seigneur Yahweh: Au bout de quarante ans, je rassemblerai les Egyptiens, d'entre les peuples chez lesquels ils auront été dispersés;
“‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
14 je ferai revenir les captifs d'Egypte, et je les ramènerai dans le pays de Pathros, dans le pays de leur origine, et ils y seront un humble royaume.
Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
15 L'Egypte sera humble entre les royaumes, et elle ne s'élèvera plus au-dessus des nations; je réduirai leur nombre, afin qu'ils ne dominent pas sur les nations.
Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
16 Ils ne seront plus pour la maison d'Israël un objet de confiance; ils lui rappelleront l'iniquité qu'elle commettait en se tournant vers eux; et l'on saura que je suis le Seigneur Yahweh. "
Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
17 La vingt-septième année, au premier mois, le premier du mois, la parole de Yahweh me fut adressée en ces termes:
A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 " Fils de l'homme, Nabuchodonosor, roi de Babylone, a fait faire à son armée un rude service contre Tyr; toute tête est devenue chauve, toute épaule meurtrie; et il n'a retiré de Tyr aucun salaire, ni pour lui, ni pour son armée, pour le service qu'il a fait contre elle.
“Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
19 C'est pourquoi ainsi parle le Seigneur Yahweh: Voici que je donne à Nabuchodonosor, roi de Babylone, le pays d'Egypte; il en emportera les richesses; il dépouillera ce qu'il y a à dépouiller, il pillera son butin et prendra ses dépouilles: et ce sera un salaire pour son armée.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
20 Pour prix du travail qu'il a fait contre Tyr, je lui donne le pays d'Egypte, parce qu'ils ont travaillé pour moi — oracle du Seigneur Yahweh.
Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 En ce jour-là, je ferai pousser une corne à la maison d'Israël, et je te donnerai d'ouvrir la bouche au milieu d'eux; et ils sauront que je suis Yahweh. "
“A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ézéchiel 29 >