< Ézéchiel 17 >

1 La parole de Yahweh me fut adressée en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 " Fils de l'homme, propose une énigme et raconte une parabole à la maison d'Israël,
“Ɗan mutum, ka shirya kacici-kacici ka faɗa wa gidan Isra’ila misali.
3 et dis: Ainsi parle le Seigneur Yahweh: Le grand aigle, aux grandes ailes, à la large envergure, et couvert d'un plumage aux couleurs variées, vint vers le Liban et enleva la cime du cèdre.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa babbar gaggafa mai manyan fikafikai, dogayen gasusuwa da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ta zo Lebanon. Ta cire kan al’ul,
4 Il arracha le plus élevé de ses rameaux, l'emporta dans un pays de Chanaan et le plaça dans une ville de marchands.
ta karya kan tohonsa da yake can bisansa ta kai ƙasar ciniki, inda ta shuka shi a birnin’yan kasuwa.
5 Puis il prit du plant du pays et le plaça dans un sol fertile; il le mit près d'une eau abondante et le planta comme un saule.
“‘Ta ɗebi waɗansu irin ƙasarku ta sa a ƙasa mai taƙi. Ta shuka shi kamar itacen wardi kusa da ruwa mai yawa,
6 Ce rejeton poussa et devint un cep de vigne étendu, peu élevé; ses rameaux étaient tournés vers l'aigle et ses racines étaient sous lui; il devint un cep, donna des jets et poussa des branches.
ya kuwa yi toho ya zama kuringa gajeruwa mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajen gaggafar, amma saiwoyinta suka zauna a ƙarƙashinta. Ta haka ta zama kuringa, ta yi rassa ta kuma fid da ganyaye.
7 Il y avait un autre grand aigle, aux grandes ailes, au plumage abondant; et voici que cette vigne étendit avidement ses racines vers lui, et que, du parterre où elle était plantée, elle poussa vers lui ses rameaux pour qu'il l'arrosât.
“‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Kuringan nan ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen wannan gaggafa daga inda aka shuka ta, ta kuma miƙe rassanta wajenta don gaggafar ta yi mata banruwa.
8 Elle était plantée dans une bonne terre, auprès d'eaux abondantes, de manière à pousser du feuillage et à porter du fruit, pour devenir une vigne magnifique.
An shuka ta a ƙasa mai kyau kusa da ruwa mai yawa don tă yi rassa masu yawa, ta ba da’ya’ya ta kuma zama kuringa mai daraja.’
9 Dis: Ainsi parle le Seigneur Yahweh: Prospérera-t-elle? N'arrachera-t-on pas ses racines et n'abattra-t-on pas son fruit pour qu'elle sèche? Toutes les jeunes feuilles qu'elle poussait se dessécheront. Il ne faudra ni un bras puissant ni beaucoup de gens pour l'enlever de ses racines.
“Ka gaya musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan za tă ci gaba? Ba za a tumɓuke ta a kuma kakkaɓe’ya’yanta don ta bushe ba? Dukan sababbin tohonta za su bushe. Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba.
10 Et voici qu'elle est plantée; mais prospérera-t-elle? Dès que le vent d'Orient l'aura touchée, ne séchera-t-elle pas? Dans le parterre où elle a poussé, elle séchera. "
Ko da an sāke shuka ta, za tă yi amfani ne? Ba za tă bushe gaba ɗaya sa’ad da iskar gabas ta hura ba, tă bushe a ƙasar da ta yi girma?’”
11 La parole de Yahweh me fut adressée en ces termes:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
12 " Dis donc à la maison rebelle: Ne savez-vous pas ce que cela signifie? Dis: Voici que le roi de Babylone est allé à Jérusalem, qu'il a pris son roi et ses chefs et les a fait venir auprès de lui à Babylone.
“Ka faɗa wa gidan’yan tawayen nan, ‘Ba ka san abin da waɗannan abubuwa suke nufi ba?’ Ka faɗa musu cewa, ‘Sarkin Babilon ya tafi Urushalima ya tafi da sarkinta da kuma manyan garinta, ya dawo da su Babilon.
13 Puis il a pris un homme de la race royale, il a conclu une alliance avec lui et lui a fait prêter serment. Il avait pris les hommes puissants du pays,
Sa’an nan ya ɗauki wani daga iyalin sarauta ya yi yarjejjeniya da shi, ya sa shi ya yi rantsuwa. Ya kuma tafi da shugabannin ƙasar,
14 pour que le royaume fût dans l'abaissement, sans pouvoir s'élever, observant son alliance pour subsister.
don a raunana masarautar, kada tă ƙara tashi, amma ta tsaya dai kan cika yarjejjeniyarsa.
15 Mais il s'est révolté contre lui, envoyant ses messagers en Egypte pour qu'on lui donnât des chevaux et beaucoup d'hommes. Réussira-t-il? Echappera-t-il, celui qui fait de telles choses? Il a rompu l'alliance, et il échapperait!
Amma sarkin nan ya yi tawaye a kan sarkin Babilon ta wurin aika jakadunsa zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. Zai ci nasara? Shi da ya yi wannan abu zai tsira? Zai iya taka yarjejjeniya har ya tsere?
16 Je suis vivant, — oracle du Seigneur Yahweh: C'est dans la ville du roi qui l'a fait régner, dont il a méprisé le serment et dont il a rompu l'alliance, c'est chez lui, dans Babylone, qu'il mourra.
“‘Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zai mutu a Babilon, a ƙasar sarkin nan da ya naɗa shi, domin bai cika rantsuwa da alkawarin da ya yi ba.
17 Et le pharaon n'agira pas pour lui, dans la guerre, avec une grande armée et un peuple nombreux, quand on élèvera des terrasses et qu'on construira des murs pour faire périr beaucoup d'hommes!
Fir’auna da yawan sojojinsa da kuma yawan jama’arsa ba zai zama da taimako gare shi a yaƙi ba, sa’ad da sarkin Babilon zai gina mahaurai ya kuma yi ƙawanya don yă hallaka rayuka masu yawa.
18 Il a méprisé le serment en rompant l'alliance, et voilà qu'il avait donné sa main! Il a fait tout cela, il n'échappera pas.
Bai cika rantsuwa ba ta wurin take alkawari. Domin sarkin Isra’ila ya ƙulla alkawari ya kuma aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai tsira ba.
19 C'est pourquoi ainsi parle le Seigneur Yahweh: Je suis vivant: c'est mon serment qu'il a méprisé, et mon alliance qu'il a rompue; je ferai retomber cela sur sa tête.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce muddin ina raye, zan nemi hakkin rantsuwata da ya ƙi cikawa da kuma alkawarin da ya take.
20 J'étendrai sur lui mon rets, et il sera pris dans mon filet; je le ferai venir à Babylone, et là je le mettrai en cause pour sa perfidie qu'il a montrée envers moi.
Zan kafa masa tarkona, zai kuma fāɗi a tarkona. Zan kawo shi a Babilon in kuma hukunta shi a can domin ya yi mini rashin aminci.
21 Tous ses fuyards de toutes ses troupes tomberont par l'épée, et ceux qui resteront seront dispersés à tout vent; et vous saurez que moi, Yahweh, j'ai parlé.
Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a kuma watsar da waɗanda suka ragu ko’ina. Ta haka za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa.
22 Ainsi parle le Seigneur Yahweh: Je prendrai, moi, un rameau de la cime du cèdre élevé et je le placerai; de l'extrémité de ses branches je couperai un tendre rameau, et je le planterai sur une montagne haute et élevée.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan cire toho a kan itacen al’ul da yake can bisa in shuka; zan kuma karya ƙanƙanin reshe daga can bisan tohon in shuka a dutse mai tsayi.
23 Je le planterai sur la haute montagne d'Israël; il poussera des branches et portera du fruit, et il deviendra un cèdre majestueux; tout passereau, tout oiseau habitera sous lui; ils habiteront à l'ombre de ses rameaux.
A ƙwanƙolin dutsen Isra’ila zan shuka shi; zai yi rassa yă ba da’ya’ya yă kuma zama al’ul mai daraja. Tsuntsaye iri-iri za su yi sheƙa a cikinsa; za su sami mafaka a inuwar rassansa.
24 Et tous les arbres des champs sauront que moi, Yahweh, j'ai abaissé l'arbre qui était élevé, et élevé l'arbre qui était abaissé, que j'ai fait sécher l'arbre vert et fait verdir l'arbre sec. Moi, Yahweh, j'ai parlé et j'agirai. "
Dukan itatuwan jeji za su san cewa Ni Ubangiji ne mai sa manyan itatuwa su zama ƙanana in kuma sa ƙananan itatuwa su zama manya. Nakan sa ɗanyen itace ya bushe, busasshen itace kuma ya zama ɗanye. “‘Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.’”

< Ézéchiel 17 >