< Psaumes 68 >

1 Pour le chef musicien. Un psaume de David. Une chanson. Que Dieu se lève! Que ses ennemis soient dispersés! Que ceux qui le haïssent fuient aussi devant lui.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
2 Comme la fumée est chassée, donc les chasser. Comme la cire fond devant le feu, Ainsi, que les méchants périssent devant la présence de Dieu.
Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
3 Mais que les justes se réjouissent. Qu'ils se réjouissent devant Dieu. Oui, qu'ils se réjouissent avec allégresse.
Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
4 Chantez à Dieu! Chantez les louanges de son nom! Exaltez celui qui monte sur les nuages: à Yah, son nom! Réjouissez-vous devant lui!
Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
5 Un père pour les orphelins, un défenseur des veuves, est Dieu dans sa demeure sainte.
Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
6 Dieu place les solitaires dans les familles. Il fait sortir les prisonniers en chantant, mais les rebelles habitent une terre brûlée par le soleil.
Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
7 Dieu, quand tu es sorti devant ton peuple, quand tu marchais dans le désert... (Selah)
Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
8 La terre a tremblé. Le ciel a également déversé de la pluie en présence du Dieu du Sinaï... en présence de Dieu, le Dieu d'Israël.
duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
9 Toi, Dieu, tu as envoyé une pluie abondante. Tu as confirmé ton héritage quand il était fatigué.
Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
10 Ta congrégation y a vécu. Toi, Dieu, tu as préparé ta bonté pour les pauvres.
Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
11 Le Seigneur annonça la parole. Ceux qui le proclament sont une grande entreprise.
Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
12 « Les rois des armées fuient! Ils fuient! » Celle qui attend à la maison partage le butin,
“Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
13 pendant que vous dormez parmi les feux de camp, les ailes d'une colombe gainées d'argent, ses plumes avec de l'or brillant.
Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
14 Quand le Tout-Puissant dispersa en elle les rois, il a neigé sur Zalmon.
Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
15 Les montagnes de Bashan sont des montagnes majestueuses. Les montagnes de Bashan sont accidentées.
Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
16 Pourquoi regardez-vous avec envie, montagnes escarpées? à la montagne où Dieu choisit de régner? Oui, Yahvé y habitera pour toujours.
Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
17 Les chars de Dieu sont des dizaines de milliers et des milliers de milliers. Le Seigneur est au milieu d'eux, depuis le Sinaï, dans le sanctuaire.
Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
18 Tu es monté sur les hauteurs. Vous avez emmené des captifs. Vous avez reçu des dons parmi les gens, oui, parmi les rebelles aussi, afin que Yah Dieu y habite.
Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
19 Béni soit le Seigneur, qui porte chaque jour nos fardeaux, le Dieu qui est notre salut. (Selah)
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
20 Dieu est pour nous un Dieu de délivrance. C'est à Yahvé, le Seigneur, qu'il appartient d'échapper à la mort.
Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
21 Mais Dieu frappera la tête de ses ennemis, le cuir chevelu poilu de celui qui persiste dans sa culpabilité.
Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
22 L'Éternel dit: « Je te ferai revenir de Basan, Je te ramènerai des profondeurs de la mer,
Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
23 pour les écraser, en trempant ton pied dans le sang, pour que les langues de tes chiens aient leur part de tes ennemis. »
don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
24 Ils ont vu tes processions, Dieu, même les processions de mon Dieu, mon Roi, dans le sanctuaire.
Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
25 Les chanteurs marchaient devant, les ménestrels suivaient, parmi les dames jouant avec des tambourins,
A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
26 « Bénissez Dieu dans les congrégations, le Seigneur dans l'assemblée d'Israël! »
Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
27 Il y a le petit Benjamin, leur chef, les princes de Juda, leur conseil, les princes de Zabulon, et les princes de Nephtali.
Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
28 Ton Dieu a ordonné ta force. Fortifie, Dieu, ce que tu as fait pour nous.
Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
29 A cause de ton temple à Jérusalem, les rois vous apporteront des présents.
Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
30 Réprimandez l'animal sauvage des roseaux, la multitude des taureaux avec les veaux des peuples. Piétinez les barres d'argent. Dispersez les nations qui prennent plaisir à la guerre.
Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
31 Des princes sortiront d'Égypte. L'Éthiopie s'empressera de tendre ses mains vers Dieu.
Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
32 Chantez à Dieu, royaumes de la terre! Chantez les louanges du Seigneur- (Selah)
Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
33 à celui qui monte sur le ciel des cieux, qui sont vieux; voici qu'il fait entendre sa voix, une voix puissante.
gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
34 Attribuez la force à Dieu! Son excellence est sur Israël, sa force est dans les cieux.
Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
35 Tu es grandiose, Dieu, dans tes sanctuaires. Le Dieu d'Israël donne force et puissance à son peuple. Loué soit Dieu!
Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!

< Psaumes 68 >