< Abdias 1 >

1 La vision d'Abdias. Voici ce que dit le Seigneur Yahvé au sujet d'Édom. Nous avons entendu des nouvelles de Yahvé, et un ambassadeur est envoyé parmi les nations, disant: « Levez-vous, et levons-nous contre elle dans la bataille.
Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
2 Voici, je t'ai rendu petit parmi les nations. Tu es grandement méprisée.
“Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
3 L'orgueil de ton cœur t'a trompé, toi qui habites dans les fentes du rocher, dont la demeure est élevée, et qui dis en son cœur: Qui me fera descendre à terre?
Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
4 Tu as beau monter comme l'aigle, et ton nid est placé parmi les étoiles, je t'en ferai descendre, dit Yahvé.
Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
5 « Si des voleurs venaient chez toi, si des brigands de nuit - oh, quel désastre t'attend - ne voleraient-ils pas seulement jusqu'à ce qu'ils en aient assez? Si des vendangeurs venaient chez toi, ne laisseraient-ils pas des raisins à glaner?
“In ɓarayi suka zo miki, in kuma’yan fashi suka shigo gidan da dare, kash, bala’i zai jira ki ba abin da suke so ne kawai za su sata ba? In kuma masu tsinka’ya’yan inabi suka zo miki, ba sukan bar’ya’yan inabi kaɗan ba?
6 Comme Esaü sera mis à sac! Comme on cherche ses trésors cachés!
Amma za a washe Isuwa ƙaƙaf, a kuma yaye ɓoyayyiyar dukiyarsa!
7 Tous les hommes de ton alliance t'ont conduit sur ton chemin, jusqu'à la frontière. Les hommes qui étaient en paix avec toi t'ont trompé, et ont prévalu contre toi. Les amis qui mangent ton pain te tendent un piège. Il n'y a pas d'intelligence en lui. »
Dukan waɗanda kike tarayya da su, za su kore ki zuwa iyaka; abokanki kuma za su yaudare ki, su kuma sha ƙarfinki; waɗanda suke cin abincinki, za su sa miki tarko, amma ba za ki gane ba.
8 « Ne détruirai-je pas en ce jour-là, dit Yahvé, les sages d'Édom et l'intelligence de la montagne d'Ésaü?
“A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.
9 Tes vaillants hommes, Teman, seront consternés, au point que tous seront retranchés de la montagne d'Ésaü par le massacre.
Jarumawanki, ya Teman, za su razana, za a kashe kowane mutum a duwatsun Isuwa.
10 A cause de la violence faite à ton frère Jacob, la honte te couvrira, et tu seras retranché pour toujours.
Saboda halin kama-karyar da kika yi wa ɗan’uwanka Yaƙub, za ki sha kunya; za a hallaka ki har abada.
11 Le jour où tu t'es tenu à l'écart, le jour où des étrangers ont emporté ses biens, où des étrangers sont entrés dans ses portes et ont tiré au sort Jérusalem, toi aussi tu as été comme l'un d'eux.
A ranan nan kin tsaya kawai kina zuba ido yayinda baƙi suke washe dukiyar ɗan’uwanki, baƙi kuma suka shiga ta ƙofofinsa suka jefa ƙuri’a don a rarraba Urushalima, kin tsaya kina kallo kamar ɗaya daga cikin abokan gābansa.
12 Mais ne méprise pas ton frère au jour de son malheur, et ne te réjouis pas des fils de Juda au jour de leur ruine. Ne t'enorgueillis pas au jour de la détresse.
Bai kamata ki rena ɗan’uwanki a ranar masifarsa ba, ko ki yi farin ciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu, ko ki yi fariya sosai a ranar wahalarsu.
13 N'entre pas dans la porte de mon peuple au jour de son malheur. Ne méprise pas leur détresse au jour de leur calamité, et ne t'empare pas de leurs biens au jour de leur calamité.
Bai kamata ki bi ta ƙofofin mutanena a ranar bala’insu ba, ko ki rena su a cikin masifarsu a ranar bala’insu, ko ki ƙwace dukiyarsu a ranar bala’insu ba.
14 Ne te tiens pas aux carrefours pour couper la route à ceux qui s'échappent. Ne livre pas ceux d'entre eux qui restent au jour de la détresse.
Bai kamata ki tsaya a mararraba don ki kashe waɗanda suke ƙoƙarin tserewa ba, ko ki ba da waɗanda suka tsere ga hannun maƙiyansu a ranar wahalarsu ba.
15 Car le jour de Yahvé est proche de toutes les nations! Ce que vous avez fait, il vous sera fait. Tes actes retomberont sur ta propre tête.
“Ranar Ubangiji ta yi kusa don dukan al’ummai. Kamar yadda kuka yi, haka za a yi muku; ayyukanku za su koma a kanku.
16 Car, comme vous avez bu sur ma montagne sainte, toutes les nations boiront sans cesse. Oui, elles boiront, elles avaleront, et elles seront comme si elles n'avaient pas été.
Kamar yadda kuka sha a kan tuduna mai tsarki, haka dukan al’ummai za su yi ta sha, za su sha, su kuma sha su zama sai ka ce ba su taɓa kasancewa ba.
17 Mais sur la montagne de Sion, il y aura ceux qui échapperont, et elle sera sainte. La maison de Jacob possédera ses biens.
Amma a kan Dutsen Sihiyona za a sami ceto; Dutsen zai zama mai tsarki, gidan Yaƙub kuma zai mallaki gādonsa.
18 La maison de Jacob sera un feu, la maison de Joseph une flamme, et la maison d'Ésaü un chaume. Ils brûleront au milieu d'eux et les dévoreront. Il ne restera rien à la maison d'Ésaü. » En effet, Yahvé a parlé.
Gidan Yaƙub zai zama kamar wuta, gidan Yusuf kuma kamar harshen wuta; gidan Isuwa zai zama kamar tattaka, za a kuma sa masa wuta yă ƙone. Babu wanda zai tsira daga gidan Isuwa.” Ni Ubangiji na faɗa.
19 Ceux du Sud posséderont la montagne d'Ésaü, et ceux de la plaine, les Philistins. Ils posséderont le champ d'Ephraïm et le champ de Samarie. Benjamin possédera Galaad.
Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.
20 Les captifs de cette armée des enfants d'Israël, qui sont chez les Cananéens, posséderont jusqu'à Zarephath; et les captifs de Jérusalem, qui sont à Sépharad, posséderont les villes du Néguev.
Wannan ƙungiyar Isra’ilawan da aka kwashe zuwa bauta da suke a Kan’ana za su mallaki ƙasar har zuwa Zarefat; waɗannan da aka kwashe zuwa bauta daga Urushalima da suke a Sefarad za su mallaki garuruwan Negeb.
21 Des sauveurs monteront sur la montagne de Sion pour juger les montagnes d'Ésaü, et le royaume sera à Yahvé.
Masu kawo ceto za su haura zuwa Dutsen Sihiyona don su yi mulkin duwatsun Isuwa. Ubangiji ne zai yi mulki.

< Abdias 1 >