< Amos 1 >

1 Paroles d'Amos, qui était parmi les bergers de Tekoa, et qu'il vit concernant Israël, au temps d'Ozias, roi de Juda, et au temps de Jéroboam, fils de Joas, roi d'Israël, deux ans avant le tremblement de terre.
Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
2 Il dit: « Yahvé rugira de Sion, et faire entendre sa voix de Jérusalem; et les pâturages des bergers seront en deuil, et le sommet du Carmel se flétrira. »
Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
3 Yahvé dit: « Pour trois transgressions de Damas, oui, pour quatre, Je ne détournerai pas son châtiment, car ils ont battu Galaad avec des instruments de fer;
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
4 mais je vais envoyer un feu dans la maison de Hazaël, et il dévorera les palais de Ben Hadad.
zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
5 Je briserai la barre de Damas, et a exterminé l'habitant de la vallée de l'Aven, et celui qui tient le sceptre de la maison d'Eden; et le peuple de Syrie ira en captivité à Kir, » dit Yahvé.
Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
6 Yahvé dit: « Pour trois transgressions de Gaza, oui, pour quatre, Je ne détournerai pas son châtiment, car ils ont emmené en captivité toute la communauté, pour les livrer à Edom;
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
7 mais j'enverrai un feu sur le mur de Gaza, et il dévorera ses palais.
Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
8 J'exterminerai l'habitant d'Asdod, et celui qui tient le sceptre d'Ashkelon; et je tournerai ma main contre Ekron; et le reste des Philistins périra, » dit le Seigneur Yahvé.
Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Yahvé dit: « Pour trois transgressions de Tyr, oui, pour quatre, Je ne détournerai pas son châtiment; car ils ont livré toute la communauté à Edom, et ne s'est pas souvenu de l'alliance fraternelle;
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
10 mais j'enverrai un feu sur la muraille de Tyr, et il dévorera ses palais. »
zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
11 Yahvé dit: « Pour trois transgressions d'Edom, oui, pour quatre, Je ne détournerai pas son châtiment, parce qu'il a poursuivi son frère avec l'épée et de rejeter toute pitié, et sa colère se déchaînait sans cesse, et il a gardé sa colère pour toujours;
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
12 mais j'enverrai un feu sur Théman, et elle dévorera les palais de Bozrah. »
Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
13 Yahvé dit: « Pour trois transgressions des enfants d'Ammon, oui, pour quatre, Je ne détournerai pas son châtiment, car ils ont éventré les femmes enceintes de Gilead, afin qu'ils puissent élargir leur frontière.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
14 Mais je vais allumer un feu dans la muraille de Rabba, et il dévorera ses palais, avec des cris au jour de la bataille, avec une tempête au jour du tourbillon;
Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
15 et leur roi ira en captivité, lui et ses princes ensemble, » dit Yahvé.
Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.

< Amos 1 >