< Lamentations 2 >

1 Comment, dans sa colère, l'Éternel a couvert d'un nuage la fille de Sion? Il a fait descendre du ciel à la terre la beauté d'Israël, et ne s'est pas souvenu de son marchepied au jour de sa colère.
Yadda Ubangiji ya rufe Diyar Sihiyona da gizagizan fushi! Ya jefar da darajar Isra’ila daga sama zuwa ƙasa; bai tuna da wurin ɗora ƙafafunsa ba a ranar fushinsa.
2 Le Seigneur a englouti toutes les habitations de Jacob. sans pitié. Il a renversé dans sa colère les forteresses de la fille de Juda. Il les a fait descendre jusqu'au sol. Il a profané le royaume et ses princes.
Ubangiji ya hallakar da wurin zaman Yaƙub ba tausayi; A cikin fushinsa kuma zai rurrushe kagaran Diyar Yahuda. Ya ƙasƙantar da mulki da masu mulki.
3 Il a coupé toute la corne d'Israël dans une colère ardente. Il a retiré sa main droite de devant l'ennemi. Il a brûlé Jacob comme un feu ardent, qui dévore tout autour.
A cikin zafin fushi ya fasa kowane ƙaho na Isra’ila. Ya janye hannun damansa sa’ad da maƙiyi ya zo. Ya yi ƙuna a cikin Yaƙub kamar wuta mai ƙone duk abin da yake kusa da ita.
4 Il a bandé son arc comme un ennemi. Il s'est tenu avec sa main droite comme un adversaire. Il a tué tout ce qui était agréable à l'œil. Dans la tente de la fille de Sion, il a déversé sa colère comme un feu.
Kamar abokin gāba, ya ɗana bakansa; hannun damansa na shirye. Kamar maƙiyi, ya kashe duk wanda idonsa ya ji daɗin gani; ya zuba fushinsa kamar wuta a kan tenti na Diyar Sihiyona.
5 Le Seigneur est devenu comme un ennemi. Il a englouti Israël. Il a englouti tous ses palais. Il a détruit ses forteresses. Il a multiplié les deuils et les lamentations dans la fille de Juda.
Ubangiji kamar maƙiyi ne; ya hallaka Isra’ila. Ya hallaka wurarenta duka ya kuma hallaka kagaranta. Ya ƙara yawan makoki da baƙin ciki wa Diyar Yahuda.
6 Il a violemment enlevé son tabernacle, comme si c'était un jardin. Il a détruit son lieu de rassemblement. Yahvé a fait en sorte que l'assemblée solennelle et le sabbat soient oubliés en Sion. Dans l'indignation de sa colère, il a méprisé le roi et le prêtre.
Ya rushe haikalinsa kamar lambu; ya hallaka wurin yi masa sujada. Ubangiji ya sa Sihiyona ta manta da bukukkuwanta da kuma ranakunta na Asabbaci; a cikin zafin fushinsa ya watsar da sarki da firist.
7 L'Éternel a rejeté son autel. Il a abhorré son sanctuaire. Il a livré les murs de ses palais aux mains de l'ennemi. Ils ont fait du bruit dans la maison de Yahvé, comme au jour d'une assemblée solennelle.
Ubangiji ya ƙi bagadensa ya kuma yi wofi da haikalinsa. Ya ba maƙiyinta fadodinta; suka yi sowa a cikin gidan Ubangiji kamar a ranar da ake yin biki.
8 Yahvé a décidé de détruire la muraille de la fille de Sion. Il a étiré la ligne. Il n'a pas retiré sa main de la destruction; Il a fait pleurer les remparts et les murs. Ils se languissent ensemble.
Ubangiji ya ƙuduri niyya yă rushe bangon da yake kewaye da Diyar Sihiyona. Ya auna da igiyar awo bai fasa hallaka ta ba. Ya sa katanga da katanga duk suka lalace.
9 Ses portes se sont enfoncées dans le sol. Il a détruit et brisé ses barreaux. Son roi et ses princes sont parmi les nations où la loi n'existe pas. Oui, ses prophètes ne trouvent aucune vision de Yahvé.
Ƙofofinta sun nutse a cikin ƙasa; ya kakkarya ƙarafanta. Sarakunanta da’ya’yan sarakunanta duk an kai su bauta cikin waɗansu ƙasashe, babu sauran doka, annabawa kuma ba su samun wahayi daga wurin Ubangiji.
10 Les anciens de la fille de Sion sont assis à terre. Ils gardent le silence. Ils ont jeté de la poussière sur leurs têtes. Ils se sont vêtus de sacs. Les vierges de Jérusalem baissent la tête vers le sol.
Dattawan Diyar Sihiyona sun zauna shiru a ƙasa; suka kuma sa rigar buhu.’Yan matan Urushalima suka sunkuyar da kawunansu ƙasa.
11 Mes yeux sont pleins de larmes. Mon cœur est troublé. Ma bile est versée sur la terre, à cause de la destruction de la fille de mon peuple, parce que les jeunes enfants et les nourrissons se pâment dans les rues de la ville.
Idanuna sun dushe don yawan kuka, raina na cike da baƙin ciki; zuciyata ta karaya domin mutanena sun hallaka, domin yara da jarirai suna suma a kan hanyoyi a cikin birni.
12 Ils demandent à leurs mères, « Où sont le blé et le vin? » quand ils s'évanouissent comme des blessés dans les rues de la ville, quand leur âme est versée dans le sein de leur mère.
Suna ce wa uwayensu, “Ina burodi da ruwan inabi?” Yayinda suke suma kamar mutanen da aka ji masu ciwo a cikin birni, sa’ad da suke mutuwa a hannuwan uwayensu.
13 Que vous dirai-je? Que te ressemblerai-je, fille de Jérusalem? Que dois-je comparer à vous, pour que je puisse te réconforter, vierge fille de Sion? Car ta brèche est aussi grande que la mer. Qui peut vous guérir?
Me zan ce miki? Da me zan kwatanta ki, ke Diyar Urushalima? Da me zan misalta ki, yadda zan iya yi miki ta’aziyya, Ke Budurwa Diyar Sihiyona? Ciwonki yana da zurfi kamar teku. Wane ne zai iya warkar da ke?
14 Vos prophètes ont eu pour vous des visions fausses et insensées. Ils n'ont pas découvert votre iniquité, pour inverser votre captivité, mais ont vu pour vous de fausses révélations et des causes de bannissement.
Wahayin annabawanki ƙarya ne kuma marasa amfani; ba su tona zunubanki ba yadda za su iya ceto ki daga bauta ba. Sun yi miki annabcin ƙarya marar amfani.
15 Tous les passants te frappent dans les mains. Ils sifflent et remuent la tête contre la fille de Jérusalem, en disant, « Est-ce la ville que les hommes appelaient 'La perfection de la beauté', la joie de toute la terre'? »
Duk masu wucewa suna yi miki tafi na reni; suna yi wa Diyar Urushalima tsaki suna kaɗa kai suna cewa, “Wannan ne birnin da aka ce kyakkyawa ne, mai farantawa dukan duniya rai?”
16 Tous tes ennemis ont ouvert la bouche contre toi. Ils sifflent et grincent des dents. Ils disent: « Nous l'avons engloutie ». C'est certainement le jour que nous attendions. Nous l'avons trouvé. Nous l'avons vu. »
Maƙiyanki duka suna ta surutu game da ke; suna tsaki suna cizon haƙora suna cewa, “Mun hallaka ta. Wannan ce ranar da muke jira; yau mun gan ta.”
17 L'Éternel a accompli ce qu'il avait prévu. Il a accompli sa parole qu'il a commandée dans les temps anciens. Il s'est jeté à terre, et n'a pas eu pitié. Il a fait en sorte que l'ennemi se réjouisse à votre sujet. Il a exalté la corne de tes adversaires.
Ubangiji ya yi abin da ya shirya; ya cika maganarsa, wadda ya umarta tun daɗewa. Ya jefar da ke ba tausayi, ya bari maƙiya sun yi nasara da ke, ya ɗaukaka ƙahon maƙiyanki.
18 Leur cœur a crié à l'Éternel. O mur de la fille de Sion, laisse les larmes couler comme une rivière jour et nuit. Ne vous donnez aucun répit. Ne laissez pas vos yeux se reposer.
Zuciyar mutane ta yi kuka ga Ubangiji. Ya bangon Diyar Urushalima, bar hawayenki su zuba kamar rafi dare da rana; kada ki huta, kada idanunki su huta.
19 Lève-toi, crie dans la nuit, au début des montres! Répands ton cœur comme de l'eau devant la face du Seigneur. Levez vos mains vers lui pour la vie de vos jeunes enfants, qui s'évanouissent de faim au bout de chaque rue.
Ki tashi, ki yi kuka cikin dare, dare na yi sai ki fara kuka; kina buɗewa Ubangiji zuciyarki. Ki ɗaga hannuwanki gare shi domin rayukan’ya’yanki, waɗanda suka suma don yunwa a kan kowane titi.
20 « Regarde, Yahvé, et vois à qui tu as fait cela! Les femmes devraient-elles manger leur progéniture, les enfants qu'ils tenaient et faisaient rebondir sur leurs genoux? Le prêtre et le prophète doivent-ils être tués dans le sanctuaire du Seigneur?
“Ka duba, ka gani ya Ubangiji. Wane ne ka taɓa yi wa haka? Ko ya kamata uwaye su ci’ya’yansu,’ya’yan da suka yi reno? Ko ya kamata a kashe firistoci da annabawa a cikin haikalin Ubangiji?
21 « Le jeune et le vieillard sont couchés par terre dans les rues. Mes vierges et mes jeunes hommes sont tombés par l'épée. Tu les as tués au jour de ta colère. Vous avez massacré, et pas plaint.
“Matasa da tsofaffi duk suna kwanciya a cikin ƙurar tituna; an karkashe matasa da’yan matana da takobi. Ka kashe su a ranar fushinka; ka kashe su ba tausayi.
22 « Tu as appelé, comme au jour d'une assemblée solennelle, mes terreurs de toutes parts. Il n'y eut personne qui échappa ou resta au jour de la colère de Yahvé. Mon ennemi a consumé ceux dont j'ai pris soin et que j'ai élevés.
“Kamar yadda kake yin gayyata a ranar biki, haka kake kawo mini tsoro a kowane gefe. A ranar fushin Ubangiji ba mai tserewa ba wanda zai tsira; maƙiyina ya kashe waɗanda na yi renonsu, na kuma lura da su.”

< Lamentations 2 >