< Ézéchiel 1 >

1 Or, la trentième année, le quatrième mois, le cinquième jour du mois, comme j'étais au milieu des captifs près du fleuve Kebar, les cieux s'ouvrirent, et je vis des visions de Dieu.
A shekara ta talatin, a wata na huɗu a rana biyar, yayinda nake cikin’yan zaman bauta kusa da Kogin Kebar, sai sammai suka buɗe na kuwa ga wahayoyin Allah.
2 Le 5 du mois, qui était la cinquième année de la captivité du roi Jojakin,
A rana biyar ga wata, a shekara ta biyar ne ta zaman bautan Sarki Yehohiyacin,
3 la parole de Yahvé fut adressée à Ézéchiel, le prêtre, fils de Buzi, au pays des Chaldéens, près du fleuve Kebar; et la main de Yahvé était là sur lui.
maganar Ubangiji ta zo wa Ezekiyel firist, ɗan Buzi, kusa da Kogin Kebar a ƙasar Babiloniyawa. A can hannun Ubangiji yana a kansa.
4 Je regardai, et voici, un vent impétueux venait du septentrion: c'était une grande nuée, avec des éclairs étincelants, et un éclat autour d'elle, et au milieu d'elle comme un métal incandescent, au milieu du feu.
Na duba, sai na ga guguwa ta taso daga arewa babban hadari cike da walƙiya kewaye da haske mai haske sosai. Tsakiyar wutar ta yi kamar ƙarfe mai cin wuta balbal,
5 De son centre sortait l'image de quatre êtres vivants. Telle était leur apparence: Ils avaient la ressemblance d'un homme.
a cikin wutar kuwa akwai abin da ya yi kamar halittu guda huɗu. A bayyane kamanninsu ya yi kamar siffar mutum,
6 Tous avaient quatre visages, et chacun d'eux avait quatre ailes.
amma kowannensu yana da fuskoki huɗu da fikafikai guda huɗu.
7 Leurs pieds étaient des pieds droits. La plante de leurs pieds était comme la plante du pied d'un veau, et ils étincelaient comme de l'airain poli.
Ƙafafunsu miƙaƙƙu ne; kuma ƙafafunsu sun yi kamar na maraƙi suna kuma walƙiya kamar tagullar da aka goge.
8 Ils avaient les mains d'un homme sous leurs ailes, sur leurs quatre côtés. Tous les quatre avaient leur visage et leurs ailes ainsi:
A ƙarƙashin fikafikansu huɗu suna da hannuwan mutum a kowane gefe. Dukansu huɗu suna da fuskoki da fikafikai,
9 Leurs ailes étaient jointes l'une à l'autre. Ils ne se tournaient pas quand ils allaient. Chacun allait droit devant lui.
kuma fikafikansu suna taɓan juna. Kowanne ya miƙe gaba; ba sa juyawa sa’ad da suke tafiya.
10 Quant à la ressemblance de leurs visages, ils avaient un visage d'homme. Les quatre autres avaient à droite la face d'un lion. Les quatre autres avaient, à gauche, une face de bœuf. Les quatre autres avaient une face d'aigle.
Fuskokinsu sun yi kamar haka. Kowanne a cikin huɗun yana da fuskar mutum, kuma a gefen dama kowanne yana da fuskar zaki, a hagu kuma fuskar maraƙi; kowanne yana kuma da fuskar gaggafa.
11 Tels étaient leurs visages. Leurs ailes étaient étendues en haut. Deux de leurs ailes se touchaient, et deux recouvraient leur corps.
Haka fuskokinsu suka kasance. Fikafikansu sun buɗu sama; kowanne yana da fikafikai biyu, ɗaya yana taɓa fikafikan ɗayan halittar a ɗayan gefe, fikafikai biyu kuma suna rufe jikinsa.
12 Chacun allait droit devant lui. Là où l'esprit devait aller, ils allaient. Ils ne se retournaient pas en allant.
Kowanne ya miƙe gaba sosai. Duk inda ruhu zai tafi, can za su, ba tare da juyawa ba yayinda suke tafiya.
13 Quant à la ressemblance des êtres vivants, leur aspect était comme des charbons ardents, comme l'aspect de torches. Le feu montait et descendait parmi les êtres vivants. Le feu était brillant, et des éclairs sortaient du feu.
Kamannin halittun ya yi kamar garwashi mai cin wuta ko kuwa kamar fitilu. Wuta tana kai da kawowa a cikin halittun; ta yi haske ƙwarai, walƙiya kuma tana wulgawa daga cikinta.
14 Les êtres vivants couraient et revenaient comme l'aspect d'un éclair.
Halittun suna gaggauta kai da kawowa kamar walƙiya.
15 Comme je voyais les êtres vivants, voici, il y avait sur la terre, à côté des êtres vivants, une roue pour chacune de ses quatre faces.
Yayinda nake kallon rayayyun halittun nan, sai na ga da’ira a ƙasa kusa da kowace halitta da fuskokinsa huɗu.
16 L'aspect des roues et de leur travail était semblable à un béryl. Les quatre roues avaient la même apparence. Leur aspect et leur travail étaient comme une roue dans une roue.
Ga kamanni da fasalin da’irorin. Suna ƙyalƙyali kamar kirisolit, kuma dukan huɗun sun yi kama da juna. Kowacce ta yi kamar da’ira a cikin da’ira.
17 Quand elles allaient, elles allaient dans leurs quatre directions. Ils ne tournaient pas en marchant.
Yayinda suke tafiya, sukan nufi duk wani gefe guda cikin gefe huɗun da halittun suka nufa; da’irorin ba za su juya ba sa’ad da halittun suke tafiya.
18 Leurs bords étaient hauts et redoutables, et les quatre avaient leurs bords remplis d'yeux tout autour.
Ƙarafansu da suka yi kamar zobe sun yi tsayi suna kuma da bantsoro, dukan ƙarafan nan huɗu kuwa da suka yi kamar zobe suna cike da idanu a kewaye.
19 Quand les êtres vivants allaient, les roues allaient à côté d'eux. Quand les êtres vivants étaient soulevés de la terre, les roues étaient soulevées.
Sa’ad da rayayyun halittun suke tafiya, da’irorin da suke kusa da su kan motsa; kuma sa’ad da rayayyun halittun sun tashi sama, da’irorin su ma sukan tashi sama.
20 Là où l'esprit devait aller, elles allaient. L'esprit devait aller là. Les roues s'élevaient à côté d'eux, car l'esprit de l'être vivant était dans les roues.
Duk inda ruhu za shi, su ma can za su, kuma da’irorin za su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun nan yana a cikin da’irorin.
21 Quand ils allaient, ceux-ci allaient. Quand ils se tenaient debout, ils se tenaient debout. Quand ils étaient enlevés de la terre, les roues étaient élevées à côté d'eux, car l'esprit de l'être vivant était dans les roues.
Sa’ad da halittun sun motsa, sai su ma su motsa; sa’ad da halittun sun tsaya cik, su ma sai su tsaya cik, sa’ad da kuma halittun sukan tashi sama, da’irorin suka tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun nan yana a cikin da’irorin.
22 Au-dessus de la tête de l'être vivant, il y avait une sorte d'étendue, comme un cristal impressionnant à regarder, qui s'étendait au-dessus de leurs têtes.
A bisa kawunan rayayyun halittun nan akwai abin da ya yi kamar ƙanƙara, mai bantsoro.
23 Sous l'étendue, leurs ailes étaient droites, l'une vers l'autre. Chacun en avait deux qui le couvraient de ce côté, et chacun en avait deux qui couvraient son corps de ce côté.
A ƙarƙashin al’arshin fikafikansu sun miƙe kyam ɗaura da juna, kuma kowanne yana da fikafikai biyu da suka rufe jikinsa.
24 Quand ils partaient, j'entendais le bruit de leurs ailes comme le bruit de grandes eaux, comme la voix du Tout-Puissant, un bruit de tumulte comme le bruit d'une armée. Quand ils se sont arrêtés, ils ont laissé tomber leurs ailes.
Sa’ad da halittun suke tafiya, sai na ji ƙarar fikafikansu, kamar rurin ruwaye masu gudu, kamar muryar Maɗaukaki, kamar hayaniyar rundunar mayaƙa. In sun tsaya cik, sukan sauko da fikafikansu.
25 Il y eut une voix au-dessus de l'étendue qui était au-dessus de leurs têtes. Quand ils se tinrent debout, ils abaissèrent leurs ailes.
Sai aka ji murya daga al’arshi a kan kawunansu yayinda suke tsaye da fikafikansu a sauke.
26 Au-dessus de l'étendue qui était au-dessus de leurs têtes, il y avait la ressemblance d'un trône, comme l'apparence d'une pierre de saphir. Sur la ressemblance du trône était une ressemblance comme l'apparence d'un homme au-dessus.
A bisa al’arshin a kan kawunansu akwai abin da ya yi kamar saffaya, kuma a can bisa a kan kursiyin akwai siffa kamar na mutum.
27 Je vis comme un métal incandescent, comme l'apparence du feu en lui tout autour, depuis l'apparence de sa taille et en haut; et depuis l'apparence de sa taille et en bas, je vis comme l'apparence du feu, et il y avait de l'éclat autour de lui.
Na ga daga abin da ya yi kamar kwankwasonsa zuwa bisa ya yi kamar ƙarfe mai walƙiya, sai ka ce wuta, kuma daga kwankwasonsa zuwa ƙasa ya yi kamar wuta; haske kuma mai walƙiya sosai kewaye da shi.
28 Comme l'apparence de l'arc-en-ciel qui est dans la nuée au jour de la pluie, ainsi était l'apparence de la clarté tout autour. C'était l'apparition de la ressemblance de la gloire de Yahvé. Quand je la vis, je tombai sur ma face, et j'entendis la voix de quelqu'un qui parlait.
Kamar kamannin bakan gizo a cikin gizagizai a ranar da aka yi ruwan sama, haka hasken da ya kewaye shi. Wannan shi ne kwatancin kamannin ɗaukakar Ubangiji. Sa’ad da na gani, sai na fāɗi rubda ciki, na kuma ji muryar wani tana magana.

< Ézéchiel 1 >