< Josué 5 >

1 Lorsque tous les rois des Amoréens, qui étaient de l'autre côté du Jourdain, à l'ouest, et tous les rois des Cananéens, qui étaient près de la mer, apprirent comment Yahvé avait mis à sec les eaux du Jourdain, depuis devant les enfants d'Israël jusqu'à ce que nous ayons traversé, leur cœur se fondit, et il n'y eut plus d'esprit en eux, à cause des enfants d'Israël.
To, da dukan sarakunan Amoriyawa na yammancin Urdun, da dukan sarakunan Kan’aniyawan da suke bakin teku suka ji yadda Ubangiji ya busar da kogin Urdun a gaban Isra’ilawa, har sai da dukansu suka ƙetare, zuciyarsu ta narke, suka karaya sosai har ma suka rasa samun ƙarfin hali su fuskanci Isra’ilawa.
2 En ce temps-là, Yahvé dit à Josué: « Fais des couteaux de silex, et circoncis de nouveau les fils d'Israël pour la seconde fois. »
A lokacin nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka yi wuƙaƙe na duwatsu ka yi wa Isra’ilawa kaciya.”
3 Josué se fit des couteaux de silex, et il circoncit les fils d'Israël à la colline des prépuces.
Sai Yoshuwa ya yi wuƙaƙe na duwatsu, ya yi wa Isra’ilawa kaciya a Gibeyat-Ha’aralot.
4 Voici pourquoi Josué les circoncit: tout le peuple sorti d'Égypte, les mâles, tous les hommes de guerre, moururent dans le désert, en chemin, après leur sortie d'Égypte.
Dalilin da ya sa ya yi haka shi ne, dukan waɗanda suka fito daga Masar, dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja, sun mutu a cikin jeji a hanya bayan sun bar Masar.
5 Car tous ceux qui étaient sortis d'Égypte étaient circoncis, mais tous ceux qui étaient nés dans le désert, sur le chemin de la sortie d'Égypte, n'avaient pas été circoncis.
Dukan mutanen da suka fito daga Masar an yi musu kaciya, amma duk waɗanda aka haifa a jeji a tafiya daga Masar, ba a yi musu ba.
6 Les enfants d'Israël marchèrent quarante ans dans le désert, jusqu'à ce que toute la nation, même les hommes de guerre qui étaient sortis d'Égypte, aient été consumés, parce qu'ils n'avaient pas écouté la voix de Yahvé. Yahvé leur jura de ne pas leur laisser voir le pays que Yahvé avait juré à leurs pères de nous donner, un pays où coulent le lait et le miel.
Isra’ilawa sun yi tafiya a jeji shekaru arba’in, har sai da dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja da suka bar Masar suka mutu, domin ba su yi wa Ubangiji biyayya ba. Gama Ubangiji ya rantse cewa ba zai bar su su ga ƙasar da ya yi wa iyayensu alkawari da rantsuwa cewa zai ba su ba, ƙasar da zuma da madara suke kwarara, ƙasar da take cike da albarka.
7 Leurs enfants, qu'il suscita à leur place, furent circoncis par Josué, car ils étaient incirconcis, faute d'avoir été circoncis en chemin.
Sai ya sa yaransu ne suka taso a maimakonsu, su ne waɗanda Yoshuwa ya yi wa kaciya. Sun kasance ba kaciya gama ba a yi musu ba a hanya.
8 Lorsqu'ils eurent fini de circoncire toute la nation, ils restèrent à leur place dans le camp jusqu'à ce qu'ils soient guéris.
Kuma bayan da aka yi wa al’ummar kaciya dukansu, sai suka dakata a nan, sai da suka warke.
9 Yahvé dit à Josué: « Aujourd'hui, je roule loin de toi l'opprobre de l'Égypte. » C'est pourquoi le nom de ce lieu a été appelé Gilgal jusqu'à ce jour.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Yau na kawar muku da zargin Masar.” Saboda haka ake kiran sunan wurin Gilgal har wa yau.
10 Les enfants d'Israël campèrent à Guilgal. Ils célébrèrent la Pâque le quatorzième jour du mois, le soir, dans les plaines de Jéricho.
Da yamman rana ta goma sha huɗu ga wata, lokacin da suke a Gilgal a filin Yeriko, Isra’ilawa suka yi Bikin Ƙetarewa.
11 Ils mangèrent des gâteaux sans levain et des grains desséchés provenant des produits du pays le lendemain de la Pâque, le même jour.
A kashegarin Bikin, a wannan rana, sai suka ci daga cikin amfanin ƙasar, burodi marar yisti da hatsin da aka gasa.
12 La manne cessa le jour suivant, après qu'ils eurent mangé des produits du pays. Les enfants d'Israël n'eurent plus de manne, mais ils mangèrent des fruits du pays de Canaan cette année-là.
Kashegari bayan da suka ci amfanin ƙasar kuwa, Manna ta yanke, mutanen Isra’ila kuma ba su ƙara samunta ba. A wannan shekara suka fara cin amfanin ƙasar Kan’ana.
13 Lorsque Josué fut près de Jéricho, il leva les yeux et regarda, et voici qu'un homme se tenait devant lui, son épée tirée à la main. Josué alla vers lui et lui dit: « Es-tu pour nous, ou pour nos ennemis? ».
To, da Yoshuwa ya yi kusa da Yeriko, ya tā da idanunsa ya duba, sai ya ga wani mutum tsaye a gabansa riƙe da takobi, sai Yoshuwa ya je wurinsa ya ce masa, “Kai namu ne ko na abokan gābanmu?”
14 Il répondit: « Non, mais je suis venu maintenant comme commandant de l'armée de l'Éternel. » Josué tomba la face contre terre, se prosterna et lui demanda: « Que dit mon seigneur à son serviteur? »
Mutumin ya ce, “Babu ko ɗaya, na dai zo ne a matsayin shugaban rundunar sojojin Ubangiji.” Sai Yoshuwa ya kwanta da fuskarsa har ƙasa, ya girmama shi, ya ce masa, “Ranka yă daɗe, wane saƙo kake da shi domin bawanka?”
15 Le prince de l'armée de Yahvé dit à Josué: « Enlève tes sandales, car le lieu sur lequel tu te tiens est saint. « Josué fit ainsi.
Shugaban rundunar sojojin Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka cire takalmanka, gama wurin da kake tsaye, mai tsarki ne.” Sai Yoshuwa ya cire takalmansa.

< Josué 5 >