< Josué 3 >

1 Josué se leva de bon matin; ils partirent de Shittim et arrivèrent au Jourdain, lui et tous les enfants d'Israël. Ils campèrent là avant de traverser.
Kashegari Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Shittim suka nufi Urdun inda suka sauka kafin su haye.
2 Au bout de trois jours, les officiers passèrent au milieu du camp;
Bayan kwana uku sai shugabannin suka zazzaga sansani, suna
3 et ils donnèrent cet ordre au peuple: « Lorsque vous verrez l'arche de l'alliance de Yahvé, votre Dieu, et les prêtres lévitiques qui la portent, quittez votre place et suivez-la.
ba da umarni ga mutane, suna cewa, “Lokacin da kuka ga akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku, da firistoci waɗanda su ne Lawiyawa, suna ɗauke da shi, sai ku tashi daga inda kuke, ku bi shi.
4 Mais il y aura entre vous et elle un espace d'environ deux mille coudées - ne vous en approchez pas - afin que vous sachiez par quel chemin vous devez passer, car vous n'avez jamais passé par là auparavant. »
A ta haka za ku san inda za ku bi, gama ba ku taɓa bin hanyar ba. Sai dai ku ɗan ba da rata wajen yadi ɗari tara tsakaninku da akwatin alkawari, kada ku kusace shi.”
5 Josué dit au peuple: « Sanctifiez-vous, car demain Yahvé fera des prodiges au milieu de vous. »
Yoshuwa ya ce wa mutane, “Ku tsarkake kanku, gama gobe Ubangiji zai yi abubuwan al’ajabi a cikinku.”
6 Josué parla aux prêtres, et dit: « Portez l'arche de l'alliance, et passez devant le peuple. » Ils prirent l'arche de l'alliance, et passèrent devant le peuple.
Yoshuwa ya ce wa firistoci, “Ku ɗauki akwatin alkawari ku sha gaba.” Sai suka ɗauki akwatin alkawari suka wuce gaban sauran jama’a.
7 Yahvé dit à Josué: « Aujourd'hui, je vais commencer à te magnifier aux yeux de tout Israël, afin qu'ils sachent que, comme j'ai été avec Moïse, je serai avec toi.
Ubangiji kuwa ya ce wa Yoshuwa, “Yau, zan fara ɗaukaka ka a gaban Isra’ilawa duka don su sani cewa ina tare da kai kamar yadda na kasance tare da Musa.
8 Tu donneras cet ordre aux prêtres qui portent l'arche de l'alliance: « Quand vous arriverez au bord des eaux du Jourdain, vous vous arrêterez dans le Jourdain ».
Ka ce wa firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawari, ‘Sa’ad da kuka kai bakin Urdun, ku shiga cikin ruwan ku tsaya.’”
9 Josué dit aux enfants d'Israël: « Venez ici, et écoutez les paroles de l'Éternel, votre Dieu. »
Yoshuwa ya ce wa Isra’ilawa, “Ku zo nan ku ji maganar Ubangiji Allahnku.
10 Josué dit: « Vous saurez ainsi que le Dieu vivant est au milieu de vous et qu'il chassera devant vous, sans faute, le Cananéen, le Héthien, le Hévien, le Phérézien, le Guirgasien, l'Amoréen et le Jébusien.
Ta haka ne za ku san cewa Allah mai rai yana tare da ku, kuma ba shakka a gabanku za ku gani zai kore Kan’aniyawa, Hittiyawa, Hiwiyawa, Ferizziyawa, Girgashiyawa, Amoriyawa da Yebusiyawa.
11 Voici, l'arche de l'alliance de l'Éternel de toute la terre passe devant vous dans le Jourdain.
Ku duba, akwatin alkawarin Ubangiji na dukan duniya zai yi gaba cikin Urdun kafin ku.
12 Maintenant, prenez douze hommes parmi les tribus d'Israël, un homme pour chaque tribu.
Yanzu sai ku zaɓi mutum goma sha biyu daga kabilan Isra’ila, ɗaya daga kowace kabila.
13 Lorsque la plante des pieds des prêtres qui portent l'arche de l'Éternel, le Seigneur de toute la terre, reposera dans les eaux du Jourdain, les eaux du Jourdain seront coupées. Les eaux qui descendent d'en haut se tiendront en un seul amas. »
Kuma da firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji, Ubangiji dukan duniya, sun sa ƙafa cikin ruwan kogin Urdun, ruwan da yake gudu a rafin zai tsaya cik yă taru a wuri ɗaya.”
14 Lorsque le peuple quitta ses tentes pour passer le Jourdain, les sacrificateurs qui portaient l'arche de l'alliance étant devant le peuple,
Saboda haka sa’ad da mutanen suka tashi don su ƙetare Urdun, firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawarin suka sha gaba.
15 et lorsque ceux qui portaient l'arche furent arrivés au Jourdain, et que les pieds des sacrificateurs qui portaient l'arche eurent trempé dans le bord de l'eau (car le Jourdain déborde sur toutes ses rives pendant toute la moisson),
Da kaka Urdun yakan cika makil da ruwa. Duk da haka da zarar firistoci masu ɗauke da akwatin alkawari suka tsoma ƙafafunsu a gefen ruwa,
16 les eaux qui descendaient d'en haut s'arrêtèrent et s'élevèrent en un seul monceau à une grande distance, à Adam, ville voisine de Zarethan; et celles qui descendaient vers la mer de la plaine, la mer Salée, furent entièrement coupées. Et le peuple passa près de Jéricho.
sai ruwan da yake gangarowa ya tsaya, ya tattaru a wuri ɗaya ya yi tudu daga nan har zuwa wani garin da ake kira Adam kusa da Zaretan, ruwan da yake gangarowa zuwa Tekun Araba (Tekun Gishiri) kuma ya yanke gaba ɗaya. Sai mutane suka ƙetare kusa da Yeriko.
17 Les prêtres qui portaient l'arche de l'alliance de Yahvé s'arrêtèrent à sec au milieu du Jourdain, et tout Israël traversa à sec, jusqu'à ce que toute la nation ait entièrement passé le Jourdain.
Firistocin kuwa da suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji suka tsaya daram a kan busasshiyar ƙasa a tsakiyar Urdun a lokacin da Isra’ilawa suka ƙetarewa, har sai da dukan mutane suka gama ƙetarewa.

< Josué 3 >