< Jérémie 3 >

1 « On dit: « Si un homme répudie sa femme, qu'elle s'éloigne de lui et devient la propriété d'un autre homme, doit-il revenir à elle? ». Cette terre ne serait-elle pas grandement polluée? Mais toi, tu t'es prostitué avec plusieurs amants, et tu reviendras vers moi, dit Yahvé.
“In mutum ya saki matarsa ta kuwa bar shi ta auri wani mutum, zai iya komo da ita kuma? Ƙasar ba za tă ƙazantu gaba ɗaya ba? Amma kun yi rayuwa kamar karuwa da masoya masu yawa yanzu za ki komo wurina?” In ji Ubangiji.
2 « Lève tes yeux vers les hauteurs dénudées, et regarde! Où n'as-tu pas été couché? Tu les as attendus au bord du chemin, comme un Arabe dans le désert. Tu as souillé le pays par ta prostitution et par ta méchanceté.
“Ta da idanu ki duba tsaunuka ki gani. Akwai wani wurin da ba a kwana da ke ba? A gefen hanya kin zauna kina jiran masoyanki, kin zauna kamar makiyayi a hamada. Kin ƙazantar da ƙasar da karuwancinki da muguntarki.
3 C'est pourquoi les pluies ont été retenues, et il n'y a pas eu d'arrière-saison; mais tu as eu le front d'une prostituée, et tu n'as pas voulu avoir honte.
Saboda haka an hana yayyafi, kuma babu ruwan bazara da ya sauka. Duk da haka kina da irin kallon da karuwa takan yi; kin ƙi ki ji kunya.
4 Ne me crieras-tu pas dès maintenant: « Mon Père, tu es le guide de ma jeunesse »?
Yanzu ba kin kira ni, ‘Mahaifina, abokina daga ƙuruciyata ba,
5 « Gardera-t-il toujours sa colère? La gardera-t-il jusqu'à la fin? Voici que vous avez parlé et fait des choses mauvaises, et que vous avez fait ce que vous vouliez. »
kullum za ka riƙa fushi? Hasalarka za tă ci gaba har abada ne?’ Haka kike magana, amma kina aikata dukan muguntar da kika iya yi.”
6 Et Yahvé m'a dit, au temps du roi Josias: « As-tu vu ce qu'a fait l'infidèle Israël? Elle est montée sur toute haute montagne et sous tout arbre vert, et elle s'y est prostituée.
A zamanin Sarki Yosiya, Ubangiji ya ce mini, “Ka ga abin da marar amincin nan, Isra’ila ta yi? Ta haura kan kowane tudu mai tsayi da kowane gindin itace mai duhuwa ta yi zina a can.
7 J'ai dit, après qu'elle eut fait toutes ces choses: « Elle reviendra vers moi »; mais elle n'est pas revenue, et sa perfide sœur Juda l'a vu.
Na yi zaton bayan ta yi wannan duka, za tă komo wurina amma ba tă yi haka ba,’yar’uwarta marar aminci nan Yahuda ta gani.
8 J'ai vu que lorsque, pour cette même raison, Israël rebelle avait commis un adultère, je l'ai répudiée et lui ai donné un certificat de divorce, la perfide Juda, sa sœur, n'a pas eu peur, mais elle est aussi allée se prostituer.
Na ba wa Isra’ila marar bangaskiya takardar saki na kuwa kore ta saboda duk zinanta. Duk da haka na ga cewa’yar’uwarta marar amincin nan Yahuda ba ta da tsoro; ita ma ta fita ta yi zina.
9 Parce qu'elle s'est prostituée à la légère, le pays a été souillé, et elle a commis l'adultère avec des pierres et avec du bois.
Domin fasikancin Isra’ila bai yi tasiri gare ta ba, sai ta ƙazantar da ƙasar ta kuma yi zina da dutse da kuma itace.
10 Et à cause de tout cela, Juda, sa sœur perfide, n'est pas revenue à moi de tout son cœur, mais seulement en faisant semblant, dit l'Éternel.
Duk da wannan duka, Yahuda’yar’uwarta rashin amincin ba tă komo gare ni da dukan zuciyarta ba, sai a munafunce,” in ji Ubangiji.
11 L'Éternel m'a dit: « L'infidèle Israël s'est montré plus juste que le perfide Juda.
Ubangiji ya ce mini, “Isra’ila marar bangaskiya ta fi Yahuda marar aminci.
12 Va, proclame ces paroles vers le nord, et dis: « Reviens, Israël rebelle, dit l'Éternel; je ne regarderai pas avec colère contre toi, car je suis miséricordieux, dit l'Éternel. Je ne garderai pas ma colère pour toujours.
Ka tafi, ka yi shelar saƙon nan wajen arewa cewa, “‘Ki komo, Isra’ila marar bangaskiya,’ in ji Ubangiji, ‘Ba zan ƙara yin fushi da ke ba, gama ni mai jinƙai ne,’ in ji Ubangiji, ‘Ba zan yi fushi da ke har abada ba.
13 Reconnais seulement ton iniquité, parce que tu as transgressé l'Éternel, ton Dieu, et que tu as dispersé tes voies parmi les étrangers, sous tout arbre vert, et que tu n'as pas écouté ma voix, dit l'Éternel.
Ki dai yarda da laifinki kin yi wa Ubangiji Allahnki tawaye, kin watsar da alheranki ga baƙin alloli a ƙarƙashin kowane itace mai duhuwa, ba ki kuwa yi mini biyayya ba,’” in ji Ubangiji.
14 « Revenez, enfants rebelles, dit Yahvé, car je suis votre mari. Je prendrai l'un de vous dans une ville, et deux dans une famille, et je vous amènerai à Sion.
“Ku komo, ku mutane marasa bangaskiya,” in ji Ubangiji, “gama ni ne mijinku. Zan ɗauke ku, ɗaya daga garuruwanku da kuma biyu daga zuriyarku in kawo ku a Sihiyona.
15 Je vous donnerai des bergers selon mon cœur, qui vous paîtront avec connaissance et intelligence.
Sa’an nan zan ba ku makiyaya da suke yin abin da zuciyata take so, waɗanda za su bishe ku da sani da kuma fahimi.
16 En ces jours-là, quand vous serez nombreux et que vous vous multiplierez dans le pays, dit l'Éternel, on ne dira plus: « L'arche de l'alliance de l'Éternel ». Ils ne s'en souviendront pas. Ils ne s'en souviendront pas. Elle ne leur manquera pas, et il n'y en aura pas d'autre.
A kwanakin, sa’ad da kuka ƙaru sosai a ƙasar,” in ji Ubangiji, “mutane ba za su ƙara yin magana a kan, ‘Akwatin alkawarin Ubangiji ba.’ Ba zai ƙara shiga zuciyarsu ko su tuna ba; ko su bukace shi, ko kuwa su yi wani irinsa ba.
17 En ce temps-là, on appellera Jérusalem « le trône de Yahvé », et toutes les nations seront rassemblées autour d'elle, autour du nom de Yahvé, autour de Jérusalem. Elles ne marcheront plus selon l'obstination de leur mauvais cœur.
A lokacin za su ce da Urushalima Kursiyin Ubangiji, kuma dukan al’ummai za su taru a Urushalima don su girmama sunan Ubangiji. Ba za su ƙara bin taurinkai zuciyarsu mai mugunta ba.
18 En ces jours-là, la maison de Juda marchera avec la maison d'Israël, et elles viendront ensemble du pays du nord au pays que j'ai donné en héritage à vos pères.
A kwanakin gidan Yahuda zai haɗu da gidan Isra’ila, tare kuma za su zo daga ƙasar da take wajen arewa zuwa ƙasar da na ba kakanninsu gādo.
19 « Mais moi, j'ai dit: « Comme je veux te mettre au milieu des enfants, et te donner un pays agréable, un bel héritage des armées des nations! » Et j'ai dit: « Tu m'appelleras « mon père », et tu ne te détourneras pas de moi ».
“Ni kaina na faɗa, “‘Da farin ciki zan ɗauke ki kamar’ya’yana maza in ba ki ƙasa mai daɗi, gādo mafi kyau da wata al’umma.’ Na zaci za ki kira ni ‘Mahaifi’ ba za ki ƙara rabuwa da bina ba.
20 « Comme une femme abandonne son mari par trahison, ainsi vous m'avez trahi, maison d'Israël », dit l'Éternel.
Amma kamar mace marar aminci ga mijinta, haka kika kasance marar aminci gare ni, ya gidan Isra’ila,” in ji Ubangiji.
21 Une voix se fait entendre sur les hauteurs dénudées, Les pleurs et les supplications des enfants d'Israël; Car ils ont perverti leur voie, Ils ont oublié Yahvé, leur Dieu.
An ji kuka a filayen tuddai, kuka da roƙon mutanen Isra’ila, domin sun lalace hanyoyinsu sun kuma manta da Ubangiji Allahnsu.
22 Revenez, enfants égarés, et je guérirai votre égarement. « Voici, nous sommes venus à toi, car tu es Yahvé notre Dieu.
“Ku komo, mutane marasa bangaskiya; zan warkar da ku daga ja da bayanku.” “I, za mu zo wurinka, gama kai ne Ubangiji Allahnmu.
23 En vérité, le secours des collines, le tumulte des montagnes, c'est en vain. C'est en Yahvé notre Dieu que réside le salut d'Israël.
Tabbatacce hayaniyar bin gumaka a kan tuddai da duwatsu banza ne; tabbatacce a wurin Ubangiji Allahnmu ne akwai ceton Isra’ila.
24 Mais l'ignominie a dévoré le travail de nos pères dès notre jeunesse, leurs troupeaux et leurs bêtes, leurs fils et leurs filles.
Daga ƙuruciyarmu allolin kunya sun cinye mu amfanin wahalar kakanninmu garkunan tumakinsu da na awakinsu, yaransu maza da mata.
25 Couchons-nous dans notre honte, et que notre confusion nous couvre; car nous avons péché contre Yahvé notre Dieu, nous et nos pères, depuis notre jeunesse jusqu'à ce jour. Nous n'avons pas obéi à la voix de Yahvé notre Dieu. »
Bari mu kwanta mu sha kunya, bari kuma kunyarmu ta rufe mu. Mun yi wa Ubangiji Allahnmu zunubi, da mu da kakanninmu; daga ƙuruciyarmu har yă zuwa yau ba mu yi wa Ubangiji Allahnmu biyayya ba.”

< Jérémie 3 >